Wasu manyan malaman yahudawa 350 sun rattaba hannu akan wata wasika da a ciki su ka bayyana rashin amincewarsu da shirin shugaban kasar Amurka Donald Trump na fitar da Falasdinawa daga yankin Gaza.

Wasikar ta kunshi cewa, Yahudawa ba su amince da  kiyan kiyashi ba akan Falasdinawa ba.

Jaridar Guardian da ake bugawa a Birtaniya wacce ta dauki labarin tare da ambato wasu fitattun malaman na yahudawa da su ka rattaba hannu akan takardar, daga cikinsu har da Sharon Bruss, Roly Matalon, da Alisa Waiser, sai kuma wasu fitattun yahudawa a Amurkan.

Cody Edgerly wanda daya ne daga cikin wadanda su ka rattaba hannu akan takardar, kuma shugaban kiran, ya nuna abinda shugaban na kasar Amurka yake son yi da cewa tsallake iyaka ne wacce a baya ake tsammancin cewa ba za a taba ketare ta ba, amma ga shi tana faruwa a karkashin kawancen Trump da Netanyahu.

Haka nan kuma wasikar ta fadawa Falasdinawa cewa: Sakonmu a gare ku shi ne cewa, ba ku kadai ba ne,muna a tare da ku, kuma  kowane daya daga cikinsu a shirye yake ya yi yaki har kar karshen rayuwasa.

Rabbi Toba Spitzer ya bayyana abinda Trump din yake son aikatawa da cewa; “Babban zunubi ne.” Ya kuma yi tuni da abinda aka yi wa Falasdinawa a 1948 da  kungiyoyin Sahayoniya masu dauke da makamai su ka kori dubun dubatar Falasdinawa daga gidajensu.

Shi kuwa Rabbi Yusuf  Berman, cewa ya yi: Da alama Trump yana daukar kansa a matsayin mamallakin wannan duniya da yake da hakkin shimfida ikonsa a ko’ina a duniya.”

Haka nan kuma ya ce; koyarwar Attaura a fili take cewa; Trump mutum ne, ba shi ne mamallaki duniya ba, don haka ba shi da hakkin da zai raba Flasdinawa da kasarsu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka

Shugaban Amurka Donald Trump ya umarci jami’an hukumar kula da shige-da-ficen-kasar da su dakatar da aikin samamen kama baƙin-haure ’yan ci-rani, a gonaki da otal-otal da ma gidajen sayar da abinci na fadin kasar.

Jaridar New York Times ta Amurka ta rawaito ma’aikatar tsaron cikin gida na tabbatar da samun umarnin, wanda aka mika shi ga hukumar kula da shige-da-fice da kuma ta yaki da fasa-kwauri, to sai dai kamfanin dillancin labarai na Reuters bai kai ga tabbatar da sahihancin umarnin ba.

’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe

Tun a lokacin yakin neman zaben shugabancin Amurka zango na biyu ,Mista Trump ya alkawarta korar bakin-hauren da suka shiga kasar ba bisa ka’ida ba.

To sai dai wannan mataki ya fuskanci kakkausan suka sakamakon yadda ake kame mutanen da ba su taba aikata laifin komai ba, musamman wadanda ke aiki a gonaki da sauran wurare, lamarin da ya janyo barkewar zanga-zanga a wasu sassan kasar.

Rahotanni sun tabbatar da cewa kawo yanzu an shafe kwanaki ana tarzoma a birnin Los Angeles na Jihar California ta Amurka, inda masu zanga-zanga ke dauki-ba-dadi da dakarun tsaron kasa da Shugaba Trump ya tura tun farko domin kwantar da zanga-zangar da ta barke sakamakon kamen bakin haure.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka
  • An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 
  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Miliyoyin Mutane Sun Gudanar  Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi
  • Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi
  • Isra’ila ta hana ayarin motocin agaji na arewacin Afrika shiga Gaza
  • Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane