’Yan bindiga sun kashe mutum 3, sun sace 26 a ƙauyukan Zamfara
Published: 19th, May 2025 GMT
Aƙalla mutum uku aka kashe, yayin da aka sace 26 a wani sabon harin da ’yan bindiga suka kai yankin Ƙaramar Hukumar Kaura Namoda, a Jihar Zamfara.
Harin ya faru ne daga ranar Alhamis zuwa Asabar a ƙauyukan da suka haɗa da Sabon Gari da Kungurki.
Mataimakiyar shugaban majalisar dokokin Edo ta yi murabus Hajji: Gwamnan Gombe ya yi bankwana da maniyyata 966, ya bai wa kowa kyautar Riyal 200Wani mazaunin yankin ya ce: “Mutane sun fara barin gidajensu da daddare, suna dawowa ne da safe.
Ana zargin yaran wani ƙasurgumin ɗan bindiga mai suna Bello Kaura wanda aka fi sani da Dan Sade ne da kai wannan harin.
Wata majiya ta ce yana da sansani kusa da Sabon Gari.
Wani mazaunin ya ƙara da cewa: “Muna roƙon gwamnati ta kafa sansanin soja a Kungurki.
“Waɗannan ’yan bindiga na kai mana hari duk lokacin da suka ga dama, rayuwarmu tana cikin firgici.”
A wani harin da suka kai, mutum huɗu suka kashe, tare da sace wani mutum ɗaya.
Daga baya, ’yan bindigar sun nemi a biya su Naira miliyan uku a matsayin kuɗin fansa amma suka ƙi barin kowa ya ji muryar wanda suka sace.
Gwamna Dauda Lawal ya tabbatar da ƙarin goyon bayansa ga hukumomin tsaro tare da ƙaddamar da dakarun sa-kai na Community Protection Guard domin taimakawa wajen kare al’umma.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga hari Sacewa Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe
Aƙalla Mutane biyar sun kwanta dama wasu huɗu kuma sun jiggata sakamakon tsinkewar igiyar lantarki bayan dawo da wutar lantarkin mai ƙarfi a unguwar Tudun Wadan Pantami, ta jihar Gombe.
Kamar yadda wani mazaunin yankin Adamu Abubakar Kulani, ya shaidawa manema labarai, mummunan lamarin ya faru ne a daren ranar Juma’a yayin da aka kawo wutar lantarkin bayan sun kwashe kwanaki babu ita.
Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Lura Da Yanayin Bala’u Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga MataYa ƙara da cewa sanadiyar wutar ta zo da ƙarfi ne ta haifar da tartsatsi, kana ta tsinka igiyar babban layin lantarkin wanda ta faɗa kan mutanen.
Tuni jama’ar yankin aka garzaya da waɗanda suka jiggata Baban Asibitin Ƙwararru na Jihar Gombe, domin duba lafiyarsu da basu kulawa kana sauran kuma da suka riga mu gidan gaskiya aka yi jana’izarsu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp