Gwamnatin kasar Amurka ta ce bata bukatar samuwar jkadan kasar Afrika ta kudu Ebrahim Rasool a kasar.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto sakataren harkokin wajen kasar Amurka Marco Rubio yana fadar haka a shafinsa na X a jiya Jumma’a, ya kuma kara da cewa Rasool mutum ne wanda yake nuna wariya, yake kuma kin Amurkawa.

Don haka bama da abinda zamu tattauna da shi, kawai bama son ganinsa a cikin kasar babba.

Rubio bai bayyana dalilan daukar wannan matakin a kan jakadan ba, amma hakan ya faru ne bayan da Jakadan Rasool ya wata cibiyar bincike na Afrika ta kudu inda a jawabin da ya gabatar ya zargi shugaban kasar Amurka Donal Trump da, da samar da shirin “sake maida Amurka kasa babba” da wani shirin fifita fararem Amurka  a kan sauran mutane a duniya.

Labarin ya kara da cewa tun lokacinda Trump ya sake dawowa fadar white house aka hana jakadan Afirka ta kudu a kasar ganawa da jami’an fadar white House kamar yadda ya dace. Fakon haka Amurka ta yi barazanar dakatar da tallafin da take bawa kasar Afrika ta kudu saboda karar da ta shigar kan HKI wacce ta aiwatar da kissan kiyashi kan Falasdinawa a Gaza daga ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 har zuwa yanzun. Banda haka kasar ta sami goyon baya daga kasashen duniya da dama. Kuma gwamnatin Amurka ta bukata Afirka ta kudu ta janye karar amma taki amincewa.

Ya zuwa yanzu dai kotun ta ICC ta fidda sammacin kama Firai ministan HKI Benyamin Natanyahu da kuma tsohon ministansa na Tsaro Yauf Galant. Kafin haka dai Ebrahim Rasool ya taba zaman jakadan Afrika ta kudu a kasarAmurka daga shekara ta 2010-2015 a lokacin shugabancin Barak Obama

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Ce; An Rusa Hanyar Tattaunawa da Iran Kan Shirin Na Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya

Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa; Amurkawa sun jefa bama-bamai a kan teburin tattaunawa tare da lalata harkar diflomasiyya

Shugaban Iran Masoud Pezeshkian ya ce Iran na gudanar da shawarwari ba na kai tsaye ba da Amurka, amma sai suka jefa bama-bamai a kan teburin tattaunawa tare da lalata hanyar diflomasiyya.

A wata hira da Tucker Carlson mai watsa labarai na Amurka, shugaba Pezeshkian yayi magana da Carlson cewa: Mr. Carlson! Mun kasance a kan teburin shawara kuma ana cikin tattaunawa saboda shugaban Amurka ya kira zuwa ga zaman lafiya kuma a wannan taron sun gaya mana cewa gwamnatin Isra’ila ba za ta kai wani hari ba.

Pezeshkian ya kara da cewa: Amma a jajibirin taro na shida, muna cikin tattaunawa, sai suka jefa bama-bamai a kan teburin tattaunawa tare da lalata harkokin diflomasiyya.

Dangane da bincike da tantancewa, shugaban na Iran ya ce: “Ba shakka a shirye muke mu koma tattaunawa da tantancewa, ba mu taba kaucewa tantancewa ba, kuma a shirye muke mu sake gudanar da wani bincike.” Abin takaici, bayan harin da Amurka ta kai kan cibiyoyin nukiliya, yawancin kayan aiki da wuraren sun lalace kuma ba su da sauƙin samuwa. Dole ne mu jira mu ga ko za a iya sake samun damar nazarin shiga wani sabon tattaunawa nan gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce; An Rusa Hanyar Tattaunawa da Iran Kan Shirin Na Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya
  • Kasar China Ta Yi Watsi da Barazanar Trump Na Kakabawa Kasashen BRICS Karin Takunkuman Tattalin Arziki
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Yace Mutanen Kasarsa Suna Cikin Shiri Don Kare Kansu Da Karfi
  • HKI Tana Tana Son Ci Gaba Da Yaki Kuma Trump Yana Tare Da Shi
  • Gwamnatin Kasar Iran Ta Yi Allawadai Da Hare-Haren HKI Kan Kasar Yemen
  • Gwamnatin Kasar Iran Ta Yaba Da Kungiyar BRICS Saboda Yin Tir Da HKI A Yakin Kwanaki 12
  • China Ta Maida Martani da Haka Kayakin Kiwon Lafiya Na Tarayyar Turai Shigowa Kasar
  • Elon Musk zai kafa sabuwar jam’iyyar siyasa a Amurka
  • Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson
  • Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin