Aminiya:
2025-07-03@22:00:07 GMT

Lakurawa sun kashe mutane 15 a Sakkwato

Published: 3rd, July 2025 GMT

Wasu ‘yan bindigar da ake zargi Lakurawa ne sun kashe mutane sama da 15 a wani sabon hari a Karamar Hukumar Tangaza ta Jihar Sakkwato.

Wani mazauni kauyen Kwalajiya ya ce ‘yan bindigar Lakurawa sun zo  kauyen a daren Lahadi har zuwa Asuba ta ranar Litinin inda suka kashe wasu mutane, a yayin da suka yi ta harbi kan mai uwa da wabi.

“Bayan sun kashe mana mutane sun tafi da dabbobi masu yawa, duk da mutanenmu sun yi kokari amma yawan maharan da makaman da suke dauke da su ya sa suka fi karfinmu.

“Har zuwa yanzu ba mu san adadin wadanda aka kai asibiti ba domin suna da yawa, sai dai wadanda suka rasu 15 muka yi wa Sallah.

“Muna kira ga jami’an tsaro su mayar da hankali wurin korar mana wadannan ‘yan bindigar don mu samu zaman lafiya a jiha baki daya.”

Babban Jami’in Kungiyar Agaji Red Cross a Sakkwato, Alhaji Abubakar Ainu ya ce harin ya matukar tayar da hankalin mutanen yankin saboda an dauki dogon rabon da a samu irin hakan.

Ainu ya ce, “jami’anmu sun ziyarci kauyen Kwalajiya da ke Mazabar Magoho a garin Tangaza domin jajantawa da kuma halartar Sallar Jana’izar mutanen da ‘yan bindigar suka kashe sama da 15.

“Waxanda suka jikkata an kai su Asibitin Kashi na Wamakko da Asibitin Koyarwa ta Jam’ar Usmanu Danfodiyo da na Kwararru a birnin Sakkwo domin karbar magani.”

Ya ce yankin na cikin wuraren da ke fama da matsalar barayin shanu da masu tayar da kayar baya.

“Wannan lamari ba ya da dadi ko kadan, dubi yadda aka mayar da wasu mata zawarawa aka mayar da wasu yara marayu domin biyan wata bukata wadda addini bai yarda da ita ba. Ina kira ga hukuma ta sake salon yakar ‘yan bindiga da take yi,” in ji Ainu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Lakurawa yan bindigar

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila na bincike kan harin dakarunta da ya kashe fararen hula a Gaza

Rundunar sojin Isra’ila ta sanar da ƙaddamar bincike a game da harin da dakarunta suka kai kan wata cibiyar intanet da ke yankin Gaza, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar ɗimbin fararen hula a jiya Litinin.

Hukumar kare lafiyar fararen hula ta Falasɗinu, ta ce wasu daga cikin makaman da Isra’ila ta harba a jiya Litinin sun faɗa kan kasuwar kwamfuta ta ‘Al-baqa’ da ke gaɓar teku da ke birnin Gaza, kuma a wannan cibiyar kaɗai mutane 24 ne suka rasa raukansu.

Ɗaya daga cikin masu magana da yawun rundunar sojin Isra’ila ya shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa cewa, tabbatas sun kai hare-hare kan wurare da dama da dakarun Hamas ke fakewa don gudanar da ayyukansu a Gaza, to amma sun ɗauki dukkanin matakan da suka wajaba domin taƙaita illolin farmakin ga fararen hula.

Ahmed al-Nayrab, mai shekaru 26 a duniya kuma ɗaya daga cikin waɗanda suka tsira da rayukansu a wannan farmaki, ya ce lokacin da aka kai harin, akwai ɗimbin mutane da suka haɗa da masu shan shayi da kuma waɗanda suka zo don samun sadarwar intanet.

Ahmed ya ci gaba da cewa, “abin da ya faru a wannan wuri ba ya da bambanci da kisan kiyashi”, yana mai cewa “a duk inda ka duba sassan gaɓoɓi ne da kuma gangar jikunan mutane ne, yayin da wasu daga cikin gawarwakin ke ci da wuta kana wasu ke kwance jina-jina’’.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lukurawa Sun Kashe Mutane 15 a Sakkwato
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara
  • ’Yansanda Sun Ceto Ɗan Ghana, Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 3
  • Lakurawa sun kashe mutum 15 a harin ramuwar gayya a Sakkwato
  • Kasar Iran Ta Nuna Ire-Iren Makamai Masu Linzami Da Ta Mayar Da Martani Da Su Kan ‘Yan Mamaya
  • An Kashe Kusan Mutane 1500 Kan Sabanin Mazhaba A Kasar Siriya A Wata Guda
  • Isra’ila na bincike kan harin dakarunta da ya kashe fararen hula a Gaza
  • Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram 10 a Borno
  • Togo: An Kashe Mutane 7 A Zanga-zangar Kin Jinin Gwamnati