Aminiya:
2025-11-02@20:54:38 GMT

Lakurawa sun kashe mutane 15 a Sakkwato

Published: 3rd, July 2025 GMT

Wasu ‘yan bindigar da ake zargi Lakurawa ne sun kashe mutane sama da 15 a wani sabon hari a Karamar Hukumar Tangaza ta Jihar Sakkwato.

Wani mazauni kauyen Kwalajiya ya ce ‘yan bindigar Lakurawa sun zo  kauyen a daren Lahadi har zuwa Asuba ta ranar Litinin inda suka kashe wasu mutane, a yayin da suka yi ta harbi kan mai uwa da wabi.

“Bayan sun kashe mana mutane sun tafi da dabbobi masu yawa, duk da mutanenmu sun yi kokari amma yawan maharan da makaman da suke dauke da su ya sa suka fi karfinmu.

“Har zuwa yanzu ba mu san adadin wadanda aka kai asibiti ba domin suna da yawa, sai dai wadanda suka rasu 15 muka yi wa Sallah.

“Muna kira ga jami’an tsaro su mayar da hankali wurin korar mana wadannan ‘yan bindigar don mu samu zaman lafiya a jiha baki daya.”

Babban Jami’in Kungiyar Agaji Red Cross a Sakkwato, Alhaji Abubakar Ainu ya ce harin ya matukar tayar da hankalin mutanen yankin saboda an dauki dogon rabon da a samu irin hakan.

Ainu ya ce, “jami’anmu sun ziyarci kauyen Kwalajiya da ke Mazabar Magoho a garin Tangaza domin jajantawa da kuma halartar Sallar Jana’izar mutanen da ‘yan bindigar suka kashe sama da 15.

“Waxanda suka jikkata an kai su Asibitin Kashi na Wamakko da Asibitin Koyarwa ta Jam’ar Usmanu Danfodiyo da na Kwararru a birnin Sakkwo domin karbar magani.”

Ya ce yankin na cikin wuraren da ke fama da matsalar barayin shanu da masu tayar da kayar baya.

“Wannan lamari ba ya da dadi ko kadan, dubi yadda aka mayar da wasu mata zawarawa aka mayar da wasu yara marayu domin biyan wata bukata wadda addini bai yarda da ita ba. Ina kira ga hukuma ta sake salon yakar ‘yan bindiga da take yi,” in ji Ainu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Lakurawa yan bindigar

এছাড়াও পড়ুন:

Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure

Babbar Kotun Kano mai lamba 7 da ke zama a cikin birni ta bayar da umarnin tsare Aminu Ismail, mazaunin Unguwar Bai a Karamar Hukumar Ajingi ta jihar, bisa zarginsa da kashe mahaifinsa, Malam Dahiru Ahmad, ta hanyar caka masa wuƙa har lahira.

Lamarin ya faru ne bayan samun sabani tsakaninsu kan aniyar Aminu ta ƙara aure, wadda mahaifinsa ya ƙi goyon baya saboda abin da ya kira halin tattalin arzikin da ake fama da shi a kasa.

Babu wani uzuri da za a yi wa sabbin hafsoshi kan matsalar tsaron Nijeriya — Tinubu Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum

A cewar lauyan masu ƙara, Barrista Lamido Abba Sorondinki, wanda ake tuhuma ya shaida wa mahaifinsa niyyarsa ta kara mata ta biyu, amma mahaifinsa ya ba shi shawarar kada ya yi hakan, yana mai danganta matsalar da halin tattalin arzikin ƙasa ke ciki.

Wannan sabani ya rikide zuwa faɗa, inda ake zargin Aminu da caccaka wa mahaifin nasa wuƙa a ƙirji, lamarin da ya jawo masa rauni mai tsanani har ya rasa ransa.

An gurfanar da Aminu da laifin kisan kai, wanda ya saba da Sashe na 221 na kundin penal code.

Ana ci gaba da shari’ar, kuma kotu ta bayar da umarnin tsare shi har zuwa lokacin da za a ci gaba da sauraron ƙarar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure