Aminiya:
2025-09-17@21:50:59 GMT

Lakurawa sun kashe mutane 15 a Sakkwato

Published: 3rd, July 2025 GMT

Wasu ‘yan bindigar da ake zargi Lakurawa ne sun kashe mutane sama da 15 a wani sabon hari a Karamar Hukumar Tangaza ta Jihar Sakkwato.

Wani mazauni kauyen Kwalajiya ya ce ‘yan bindigar Lakurawa sun zo  kauyen a daren Lahadi har zuwa Asuba ta ranar Litinin inda suka kashe wasu mutane, a yayin da suka yi ta harbi kan mai uwa da wabi.

“Bayan sun kashe mana mutane sun tafi da dabbobi masu yawa, duk da mutanenmu sun yi kokari amma yawan maharan da makaman da suke dauke da su ya sa suka fi karfinmu.

“Har zuwa yanzu ba mu san adadin wadanda aka kai asibiti ba domin suna da yawa, sai dai wadanda suka rasu 15 muka yi wa Sallah.

“Muna kira ga jami’an tsaro su mayar da hankali wurin korar mana wadannan ‘yan bindigar don mu samu zaman lafiya a jiha baki daya.”

Babban Jami’in Kungiyar Agaji Red Cross a Sakkwato, Alhaji Abubakar Ainu ya ce harin ya matukar tayar da hankalin mutanen yankin saboda an dauki dogon rabon da a samu irin hakan.

Ainu ya ce, “jami’anmu sun ziyarci kauyen Kwalajiya da ke Mazabar Magoho a garin Tangaza domin jajantawa da kuma halartar Sallar Jana’izar mutanen da ‘yan bindigar suka kashe sama da 15.

“Waxanda suka jikkata an kai su Asibitin Kashi na Wamakko da Asibitin Koyarwa ta Jam’ar Usmanu Danfodiyo da na Kwararru a birnin Sakkwo domin karbar magani.”

Ya ce yankin na cikin wuraren da ke fama da matsalar barayin shanu da masu tayar da kayar baya.

“Wannan lamari ba ya da dadi ko kadan, dubi yadda aka mayar da wasu mata zawarawa aka mayar da wasu yara marayu domin biyan wata bukata wadda addini bai yarda da ita ba. Ina kira ga hukuma ta sake salon yakar ‘yan bindiga da take yi,” in ji Ainu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Lakurawa yan bindigar

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

 

A yayin samamen, kakakin ‘yansandan Neja ya ce an kama mutane shida a wurin da ake hakar ma’adinan yayin da wasu kuma suka tsere.

 

Abiodun ya bayyana sunayen wadanda ake cafken da Aliyu Rabiu, Samaila Ibrahim, Sadiku Auwal, Ibrahim Babangida, Musa Adamu da Sani Hassan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano