Leadership News Hausa:
2025-06-16@18:43:19 GMT

Gwamnan Kano Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Tsaro

Published: 19th, May 2025 GMT

Gwamnan Kano Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Tsaro

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya rantsar da tsohon Sojan sama (Air Vice Marshal) Ibrahim Umaru a matsayin sabon Kwamishinan tsaro na cikin gida a yayin taron majalisar zartarwa na 28 a fadar gwamnati.

Tsohon hafsan Sojan saman, wanda ya yi ritaya, ya kasance Daraktan-Janar na sashin aiyuka na musamman a fadar gwamnatin jihar Kano kafin naɗin nasa.

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

Gwamnan Yusuf ya buƙaci sabon kwamishinan ya yi aiki da gaskiya, mutunci da himma wajen kare rayuka da dukiya a jihar, yana mai jaddada mahimmancin haɗin gwuiwa tsakanin hukumomin tsaro.

AVM Ibrahim Umaru mai ritaya ya na da gogewar shekaru da yawa a Sojan sama na Nijeriya (NAF) zuwa sabon muƙaminsa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Sabon harin Iran ya hallaka mana mutum 8 – Isra’ila

Isra’ila ta ce mutum takwas sun mutu a daren ranar Litinin sakamakon sabon harin da Iran ta kai a biranen Tel Aviv da Haifa da wasu sassa na ƙasar.

Wannan na zuwa ne a matsayin ci gaba daga jerin hare-hare da Iran ke kai wa tun bayan da Isra’ila ta fara kai mata hari makonnin da suka wuce.

NAJERIYA A YAU: Dalilan Durƙushewar Sababbin Sana’o’i Tun Ba A Je Ko’ina Ba Iran ta kai sabbin hare-hare birnin Tel Aviv da Haifa

Yanzu haka, adadin mutanen da hare-haren Iran suka kashe a Isra’ila ya kai 24, yayin da mutane sa.a da 300 ke kwance a asibitoci saboda raunuka.

Isra’ila ta ce a martaninta, jiragen yaƙin ƙasar sun kai hari a birnin Tehran, babban birnin Iran, inda suka lalata wata hedikwatar dakarun juyin juya hali.

Haka kuma sun kai farmaki a wasu cibiyoyi da Iran ke adana makamai a tsakiyar ƙasar.

An fara wannan rikici ne bayan da Isra’ila ta kai hari da asubahin ranar Juma’a a Iran.

Iran ta ce a wannan harin, mutane sama da 200 ne suka mutu.

Wannan hari ya fusata gwamnatin Iran, inda ta fara mayar da martani da hare-hare a Isra’ila.

A baya ma, ana zargin Isra’ila da kai hare-hare da dama a Iran, musamman kan dakarun da ta ke zargi da taimaka wa ƙungiyoyin da ke barazana gare ta, kamar Hezbollah da Hamas.

Rikicin ya ci gaba da tsananta, yayin da kowane ɓangare ke kai farmaki ga ɗaya, al’ummar ƙasashen biyu na ci gaba da jikkata da mutuwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sabon harin Iran ya hallaka mana mutum 8 – Isra’ila
  • IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 
  • Mataimakin Gwamnan Sakkwato bai karɓi shanun tallafin layya ba — Hukumar Zakka
  • Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC
  • Ƴansanda Sun Fara Tsananta Ɗaukar Mataki Kan Ƴan Daba A Kano
  • Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga
  • Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Bayyana Sabon Salon Mayar Da Martani Kan Isra’ila
  • Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila
  • Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai