Leadership News Hausa:
2025-12-07@19:57:04 GMT

Sin Ba Za Ta Taba Amincewa Da Ayyukan ’Yan Aware Ba 

Published: 15th, March 2025 GMT

Sin Ba Za Ta Taba Amincewa Da Ayyukan ’Yan Aware Ba 

Babban dan majalisar zartaswar kasar Sin, kuma shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama’ar kasar Zhao Leji, ya jaddada matsayar kasar Sin ta dakile duk wani yunkuri na samun ’yancin yankin Taiwan, da yunkurin ’yan aware, da duk wasu matakan tsoma hannu cikin harkokin gidan kasar Sin daga sassan waje.

Zhao, wanda ya bayyana hakan yau Juma’a a nan birnin Beijing, yayin wani taron karawa juna sani, albarkacin bikin cika shekaru 20 da fara aiwatar da dokar haramta ware wani yankin kasa, ya jaddada muhimmancin ci gaba da bunkasa manufar dinke sassan kasar Sin wuri guda. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun harbe ɗan sanda har lahira a Edo

An harbe wani jami’in ɗan sanda har lahira, yayin da yake tsaka da binciken ababen hawa a Benin a Jihar Edo.

Kakakin rundunar, CSP Moses Yamu, ya ce lamarin ya faru da misalin ƙarfe 12 na ranar Juma’a, lokacin da jami’an rundunar suka tsayar da wata baƙar mota ƙirar Lexus, amma ta ƙi tsayawa.

’Yan sanda sun ceto yara 2 da aka yi garkuwa da su a Borno Ƙasashen waje na taimaka wa ’yan ta’adda a Najeriya —Sheikh Gumi

Ɗaya daga cikin mutanen da ke cikin motar ya buɗe wa jami’an da ke shingen wuta, sannan suka tsere.

A dalilin haka ne suka harbe wani ɗan sanda wanda ba a bayyana sunansa ba har lahira.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, Monday Agbonika, ya umarci a farauto waɗanda suka aikata laifin.

Ya roƙi jama’a su bayar da sahihan bayanai, musamman idan suka ga irin wannan motar da aka zayyana.

Rundunar ta tabbatar wa jama’a cewa an ƙara tsaurara tsaro a faɗin jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An gano gawar malamin Islamiyya da ya ɓace a Neja
  • Tawagar Majalisar Amurka ta iso Nijeriya Don Bincika Zargin Tauye Haƙƙin Addini
  • Amurka: Mun Yi Kokarin Kifar Da Gwamnatin JMI Har Sau Biyu Ba Tare Da Samun Nasara Ba
  • Iran Ta Gargadi Kasashen Larabawa Dangane Da Tsibiran Kasar Guda Uku A cikin Tekun Farisa
  • ’Yan bindiga sun harbe ɗan sanda har lahira a Edo
  • Kasashen Musulmi 8 Sun Ki Amincewa Da Korar Falasdinawa Daga Gaza
  • Jigajigan Majalisar Ribas 17 Sun Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
  • Na’im Kassim Ya Yi Suka Akan Shigar Kasar Cikin Kwamitin Tattaunawa Da “Isra’ila” Kai Tsaye
  • Gwamnatin Iraki Ta Kore Saninta Da Shigar Da Sunayen Hizbullah Da “Ansarullah” A Cikin Na ‘Yan Ta’adda
  • Iran Ta Mayar Da Martani Kan Sanarwar Bayan Taron  Majalisar Kasashen Yankin Tekun Fasha