Sin Ba Za Ta Taba Amincewa Da Ayyukan ’Yan Aware Ba
Published: 15th, March 2025 GMT
Babban dan majalisar zartaswar kasar Sin, kuma shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama’ar kasar Zhao Leji, ya jaddada matsayar kasar Sin ta dakile duk wani yunkuri na samun ’yancin yankin Taiwan, da yunkurin ’yan aware, da duk wasu matakan tsoma hannu cikin harkokin gidan kasar Sin daga sassan waje.
Zhao, wanda ya bayyana hakan yau Juma’a a nan birnin Beijing, yayin wani taron karawa juna sani, albarkacin bikin cika shekaru 20 da fara aiwatar da dokar haramta ware wani yankin kasa, ya jaddada muhimmancin ci gaba da bunkasa manufar dinke sassan kasar Sin wuri guda. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana
Wani rahoto da hukumar kula da kididdiga ta kasar Sin (NBS) ta fitar a yau Litinin ya nuna cewa, ribar da manyan masana’antun kasar Sin suka samu cikin watanni tara na farkon shekarar 2025 da muke ciki, ta karu da kashi 3.2 cikin dari.
A cewar hukumar ta NBS, masana’antun da ke samun kudaden shiga da suka kai akalla yuan miliyan 20 (kimanin dala miliyan 2.8) a shekara-shekara, sun samu jimillar ribar da ta kai yuan tiriliyan 5.37 a cikin watanni taran.
A watan Satumba, ribar da manyan masana’antun ke samu ta farfado sosai, inda ta karu da kashi 21.6 cikin dari a kan na makamancin lokacin a bara, kamar yadda hukumar ta NBS ta bayyana. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA