Leadership News Hausa:
2025-11-13@07:28:21 GMT

Sin Ba Za Ta Taba Amincewa Da Ayyukan ’Yan Aware Ba 

Published: 15th, March 2025 GMT

Sin Ba Za Ta Taba Amincewa Da Ayyukan ’Yan Aware Ba 

Babban dan majalisar zartaswar kasar Sin, kuma shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama’ar kasar Zhao Leji, ya jaddada matsayar kasar Sin ta dakile duk wani yunkuri na samun ’yancin yankin Taiwan, da yunkurin ’yan aware, da duk wasu matakan tsoma hannu cikin harkokin gidan kasar Sin daga sassan waje.

Zhao, wanda ya bayyana hakan yau Juma’a a nan birnin Beijing, yayin wani taron karawa juna sani, albarkacin bikin cika shekaru 20 da fara aiwatar da dokar haramta ware wani yankin kasa, ya jaddada muhimmancin ci gaba da bunkasa manufar dinke sassan kasar Sin wuri guda. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Yi Kira Da A Inganta Mika Mulki Cikin Kwanciyar Hankali A Sudan Ta Kudu

Mataimakin wakilin dindindin na Sin a MDD Sun Lei, ya gabatar da jawabi yayin taron kwamitin sulhu game da batun Sudan ta Kudu da aka gudanar jiya Talata, inda ya yi kira da a inganta mika mulki cikin kwanciyar hankali a Sudan ta Kudu.

Sun Lei ya ce, Sin ta bukaci dukkan bangarorin kasa da kasa da su mayar da hankali kan yanayin zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar, kana su dakatar da ayyukan da ka iya haifar da tashe-tashen hankula, musamman ma a hana amfani da karfin tuwo da kuma guje wa karuwar rikice-rikice.

Sun Lei ya kara da cewa, kasar Sin ta yi imanin cewa, mabudin warware matsalolin kasashen Afirka yana hannun Afirka. Duk wata mafita ya kamata ta kare ikon mulki kan Sudan ta Kudu da shugabancinta, tare da mutunta batutuwan da kasar ta damu da su.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, Sun Lei ya bayyana cewa Sin ta yi kira ga kasashen duniya da su kara ba da tallafi don daidaita tattalin arziki da rayuwar jama’ar kasar, da kyautata walwalar jama’arta, da kuma tallafawa Sudan ta Kudu wajen daukar hanyar samun ci gaba mai ’yanci da dorewa. (Safiyah Ma)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam November 11, 2025 Daga Birnin Sin Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa November 11, 2025 Daga Birnin Sin CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya November 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dattawa Ta Amince da Karbo Rancen Naira Tiriliyan 1.15 Domin Cike Gibin Kasafin Kudi
  • Sin Ta Yi Kira Da A Inganta Mika Mulki Cikin Kwanciyar Hankali A Sudan Ta Kudu
  • Ɗan Majalisar Wakilai daga Kano Sagir Ƙoƙi ya fice daga NNPP
  • Masar Da Sudan Sun Jaddada Wajabcin Tabbatar Da Zaman Lafiya A Yankin
  • Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro
  • An ceto mutane 86 daga hannun ’yan ta’adda a Borno
  • An ceto mutane 86 daga hannun ’yan ta’adda 29 a Borno
  •  Babu Wani Zabi Da Ya Rage Face Amincewa Da Iran A Matsayin Cibiyar Kimiyyar Masana’antar Nukiliya
  • Yadda Sojoji Suka Tarwatsa Haramtattun Matatun Mai 14 A Yankin Neja Delta 
  • ’Yan bindiga sun sace mata 5 a Kano