Sin Ba Za Ta Taba Amincewa Da Ayyukan ’Yan Aware Ba
Published: 15th, March 2025 GMT
Babban dan majalisar zartaswar kasar Sin, kuma shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama’ar kasar Zhao Leji, ya jaddada matsayar kasar Sin ta dakile duk wani yunkuri na samun ’yancin yankin Taiwan, da yunkurin ’yan aware, da duk wasu matakan tsoma hannu cikin harkokin gidan kasar Sin daga sassan waje.
Zhao, wanda ya bayyana hakan yau Juma’a a nan birnin Beijing, yayin wani taron karawa juna sani, albarkacin bikin cika shekaru 20 da fara aiwatar da dokar haramta ware wani yankin kasa, ya jaddada muhimmancin ci gaba da bunkasa manufar dinke sassan kasar Sin wuri guda. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila Ta Hana Motocin Agaji 6000 Shiga Gaza Duk Da Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta
Hukumar bada agaji da samar da ayyukan ga falasdinawa na majalisar dinkin duniya UNRWA ta fadi cewa isra’ila ta hana motoci makare da kayan agaji guda 6000 shiga yankin Gaza da suke dauke da abinci magunguna da za su iya wadatar da yankin na tsawon watanni 3.
Kakakin kungiyar ta UNRWA Adnan Abu Hasna ya fadi cewa duk da yake cewa adadin kayan da ake shiga da shi yankin gaza ya karu tun bayan cimma yarjejeniyar dakatar da bude wuta a watan oktoba, sai dai duk da haka isra’ila ta hana shigar da kayayyakin da ake bukata da zasu iya taimakwa wajen warware matsalar da yankin ke fuskata.
A watan oktoba isra’ila ta shaidawa majalisar dinkin duniya cewa za ta bari motoci dauke da kayan agaji guda 3000 su shiga yankin gaza inda suka raba adadin zuwa gida biyu, jiragen Ruwan da Isra’ila ta kama suna dauke da dubban tanti da barguna da aka kiyasta za su kai guda 1.3 domin rabawa wadanda aka rusa gidajensu a fadin yankin.
Kungiyoyin bada agaji sun yi barazanar cewa Rashin sakin dubban kayayyakin daga isra’ila ya kara jefa yankin cikin mummunan bala’I da zai kara dagula alamura a yankin, inda Asibitoci bada aiki saboda babu kayan aiki, mutane da ake rusa gidajensu basu da wajen zama, kuma cututtuka na yaduwa kamar farin dango a yankin gaza
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Amurka ta soke bada mafaka ga ‘yan kasashen Afirka 10 December 3, 2025 Masar Ta Sanar Da Tattaunawa Da Amurka Don Shirya Sake Gina Gaza December 3, 2025 Kasar Qatar Ta Gargadi Isra’ila Game Da ci Gaba Da Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza December 3, 2025 Sharhi: HKI tana fama da karancin sojoji a dukkan rassan sojojin kasar December 2, 2025 Shugaba Pizishkiyan: Goyon Bayan Al’ummar Iran Ga Tsarin Musulunci Ne Ya Hana Abokan Gaba Cimma Manufa December 2, 2025 Shugaban Kasar Najeriya Ya Nada Janar Chiristopher Musa ( Ritaya) A Matsayin Ministan Tsaro December 2, 2025 Nigeria Ta Bai Wa Dan Takarar Shugabancin Kasar Guine Bissau Mafakar Siyasa December 2, 2025 Palasdinu: Sojojin “Isra’ila” 3 Su Ka Jikkata Sanadiyyar Taka Su Da Mota December 2, 2025 Hamas Ta Caccaki Isra’ila Game Da Hana Shigar Da Kayayyakin Agaji A Yankin Gaza December 2, 2025 Ministan Tsaron Najeriya Ya Mika Takardar Ajiye Aiki Ga Shugaban Kasa Ahmad Tinubu. December 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci