Aminiya:
2025-07-03@21:06:49 GMT

’Yan Majalisar Wakilai bakwai na Akwa Ibom sun koma APC

Published: 3rd, July 2025 GMT

A ci gaba da sauya sheƙar da ’yan Majalisar Wakilai na Tarayya ke yi a ranar Alhamis wasu mambobi bakwai daga Jihar Akwa Ibom sun sanar da sauya sheƙa zuwa Jam’iyyar APC mai mulki.

Cikin waɗanda suka sauya sheƙa sun haɗa da shida daga Jam’iyyar PDP da kuma ɗaya daga Jam’iyyar YPP.

’Yan Najeriya sun fara begen Buhari saboda azabar Tinubu – Amaechi Gwamnatin Yobe ta rufe kasuwanni 3 saboda matsalar tsaro

Shugaban Majalisar Wakilan Tarayya Tajudeen Abbas ne ya karanta wasiƙunsu na sauya sheƙa a zauren Majalisar a ranar Alhamis yayin zaman majalisar.

’Yan majalisar dai sun yi nuni da ƙara samun rarrabuwar kawuna da rigingimun cikin gida a cikin Jam’iyyar PDP a matsayin dalilin da ya sa suka yanke shawarar ficewa daga jam’iyyar.

Waɗanda suka sauya sheƙa daga PDP sun haɗa da: Paul Ekpo da Unyime Idem da Martins Etim da Okpolu Ukpong Etteh da Uduak Odudoh da Okon Ime Bassey.

Shi ma ɗan Majalisa Emmanuel Ukpong-Udo na Jam’iyyar YPP ya koma APC.

’Yan majalisar dai sun ce rikicin da ya ɓarke a Jam’iyyar PDP a Akwa Ibom da ma ƙasa baki ɗaya ya sa ba su iya wakiltar mazaɓarsu yadda ya kamata.

Ficewar ta zo ne makonni kaɗan bayan gwamnan Jihar Akwa Ibom, Umo Eno ya koma APC.

Da yake mayar da martani game da sauya sheƙar, shugaban marasa rinjaye na majalisar, Kingsley Chinda ya nuna baƙin cikinsa game da ci gaban da aka samu.

Chinda ya ce, iƙirarin rarrabuwar kawuna a cikin Jam’iyyar PDP bai dace ba kuma ya saɓawa doka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Akwa Ibom Jam iyyar PDP Yan majalisar Yan Majalisar sauya sheƙa a Jam iyyar

এছাড়াও পড়ুন:

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

Shugabannin jam’iyyar APC a matakin gunduma na Gayam, cikin ƙaramar hukumar Lafia, sun dakatar da shugaban jam’iyyar a matakin jiha, Hon. Aliyu Bello. Sun zarge shi da aikata abubuwan da suka saɓa da kundin tsarin mulki na jam’iyyar, musamman sashe na 21 (D)(i–iii), wanda ya haɗa da cin amanar jam’iyya da goyon bayan ɗan takarar wata jam’iyya daban.

Shugaban gundumar, Ibrahim Ilyasu, ya bayyana cewa matakin dakatarwar ya fara aiki nan take, kuma Hon. Bello ba zai iya wakiltar kansa ko amfani da matsayin sa a matsayinsa na mamba na APC daga Gayam ba, har sai an warware batutuwan da aka gabatar. Sun kuma zarge shi da jawo wa jam’iyyar tozarci da keta mutuncinta a idon jama’a.

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC Sanusi II Ya Gudanar Da Hawan Nassarawa Duk Da Umarnin ‘Yansanda A Kano

Sai dai wasu daga cikin jiga-jigan jam’iyyar a jihar sun ce wannan matakin wani yunkuri ne daga wani ɓangare na ƙungiyar siyasa da ke ƙoƙarin kifar da Bello daga kujerarsa, musamman bisa alaƙa da wani ɗan takarar gwamna a jihar. Sun ce wannan rikici ya ƙara bayyana rabuwar kai da rikicin cikin gida a jam’iyyar.

A wata ganawa da wasu shugabannin jam’iyyar a Lafia, an kaɗa ƙuri’ar nuna goyon baya da amincewa da shugabancin Hon. Bello, wanda hakan ke nuna cewa har yanzu akwai sassa a jam’iyyar da ke goyon bayansa, duk da dakatarwar da aka sanar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Mali ta ƙara wa Goita wa’adin mulkin shekara biyar
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Fitar Da Rahoton Wadanda Suke Taimakawa ‘Yan Sahayoniyya Wajen Murkushe Falasdinawa
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Fitar Da Rahoton Wadanda Suke Taimakawa Yahudawan Sahayoniyya Wajen Murkushe Falasdinawa
  • ‘Mutum 600 da suka bace a ambaliyar Mokwa sun mutu’
  • Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC
  • Majalisar Dokokin Filato ta zaɓi sabon shugaba
  • An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa
  • Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma
  • Wakilan Kasashen Duniya Da Kungiyoyin Sun Je Ta’aziyya Mutanen Da Suka Yi Shahada A Yakin Iran Da H.K.Isra’ila