Kotun ɗaukaka ƙara ba ta soke naɗin Sanusi II ba — Gwamnatin Kano
Published: 15th, March 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Kano, ta bayyana cewa Kotun Ɗaukaka Ƙara ba ta soke naɗin Muhammadu Sanusi II a matsayin Sarkin Kano ba.
Kwamishinan Shari’a kuma Babban Lauyan Jihar, Haruna Isa Dederi, ya bayyana cewa kotun kawai ta dakatar da aiwatar da hukuncinta har sai Kotun Ƙoli ta yanke hukunci a kan shari’ar.
Ya jaddada cewa kawai Kotun Ƙoli ce ke da ikon sauya hukuncin mayar da Sanusi kan karagar mulki.
“Kotun Ɗaukaka Ƙara ba ta soke hukuncinta na baya ba. Kawai dai ta dakatar da aiwatar da shi har sai Kotun Ƙoli ta yanke hukunci na ƙarshe,” in ji Dederi yayin da yake magana da manema labarai.
Ya ƙara da cewa kotun ta tabbatar da cewa gwamnatin jihar na da hurumin dawo da Sanusi kan sarautar Kano.
“Hukuncin da aka yanke a ranar 10 ga watan Janairu ya tabbatar da cewa Kotun Tarayya ta farko ba ta da ikon yanke hukunci kan wannan batu.
“Sanusi na nan a matsayin Sarki har sai Kotun Ƙoli ta yanke hukunci,” in ji shi.
Shari’ar ta samo asali ne bayan Aminu Baba DanAgundi, ɗaya daga cikin magoya bayan tsohon Sarki Aminu Ado Bayero, ya garzaya kotu tare da ƙalubalantar dawo da Sanusi a matsayin Sarkin Jihar.
Kotun Ɗaukaka Ƙara ta yanke hukunci cewa komai zai ci gaba da kasancewa yadda yake har sai Kotun Ƙoli ta yanke hukunci na ƙarshe kan lamarin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamnatinl Rikicin Masarauta har sai Kotun Ƙoli ta yanke hukunci
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun ceto mutum 7 da ’yan bindiga suka sace a Kano
Dakarun Sojin Najeriya, sun ceto wasu mutum bakwai da ’yan bindiga suka sace a Ƙaramar Hukumar Tsanyawa da ke Jihar Kano.
Wannan zuwa ne bayan mazauna Yankamaye Cikin Gari suka sanar da jami’an tsaro cewa ’yan bindiga sun shiga ƙauyensu a daren ranar Juma’a.
’Yan bindiga sun kashe tsohuwa, sun sace mutum 3 a Kano CAF ta ƙara yawan ’yan wasan ƙasashe zuwa 28 a gasar nahiyar AfrikaWannan na cikin wata sanarwar da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Kyaftin Babatunde Zubairu, ya fitar ranar Lahadi.
Ya ce sojin ƙasa tare da haɗin guiwar sojin sama da ’yan sanda sun garzaya wajen, inda suka yi artabu da ’yan bindigar, sannan suka ceto mutanen da abin ya shafa.
Sai dai Zubairu, ya ce ’yan bindigar sun riga sun kashe wata mata mai shekaru 60 kafin sojoji su isa yankin.
Ya ƙara da cewa bayan harin farko da suka kai, sojojin sun bi sahun ’yan bindigar zuwa yankin Rimaye, inda suka yi musu luguden wuta, wanda hakan ya tilasta musu barin mutanen da suka sace.
Sai dai har yanzu ba a gano inda mutane huɗu da suka sace suke ba.
Bayanai sun nuna cewar bayan ’yan bindigar sun tsere, sun nufi Ƙaramar Hukumar Kankia da ke Jihar Katsina, kuma jami’an tsaro na ci gaba da bibiyarsu.
Kwamandan rundunar, ya yaba da jarumtar sojojin, ya roƙi jama’a da su riƙa bai wa hukumomin tsaro sahihin bayanai a kan lokaci domin kawar da ’yan bindiga a jihar.