Aminiya:
2025-10-16@13:29:48 GMT

Kotun ɗaukaka ƙara ba ta soke naɗin Sanusi II ba — Gwamnatin Kano

Published: 15th, March 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Kano, ta bayyana cewa Kotun Ɗaukaka Ƙara ba ta soke naɗin Muhammadu Sanusi II a matsayin Sarkin Kano ba.

Kwamishinan Shari’a kuma Babban Lauyan Jihar, Haruna Isa Dederi, ya bayyana cewa kotun kawai ta dakatar da aiwatar da hukuncinta har sai Kotun Ƙoli ta yanke hukunci a kan shari’ar.

MC Tagwaye ya fice daga APC zuwa SDP Baffa Bichi da Barau Jibrin sun gana a Abuja

Ya jaddada cewa kawai Kotun Ƙoli ce ke da ikon sauya hukuncin mayar da Sanusi kan karagar mulki.

“Kotun Ɗaukaka Ƙara ba ta soke hukuncinta na baya ba. Kawai dai ta dakatar da aiwatar da shi har sai Kotun Ƙoli ta yanke hukunci na ƙarshe,” in ji Dederi yayin da yake magana da manema labarai.

Ya ƙara da cewa kotun ta tabbatar da cewa gwamnatin jihar na da hurumin dawo da Sanusi kan sarautar Kano.

“Hukuncin da aka yanke a ranar 10 ga watan Janairu ya tabbatar da cewa Kotun Tarayya ta farko ba ta da ikon yanke hukunci kan wannan batu.

“Sanusi na nan a matsayin Sarki har sai Kotun Ƙoli ta yanke hukunci,” in ji shi.

Shari’ar ta samo asali ne bayan Aminu Baba DanAgundi, ɗaya daga cikin magoya bayan tsohon Sarki Aminu Ado Bayero, ya garzaya kotu tare da ƙalubalantar dawo da Sanusi a matsayin Sarkin Jihar.

Kotun Ɗaukaka Ƙara ta yanke hukunci cewa komai zai ci gaba da kasancewa yadda yake har sai Kotun Ƙoli ta yanke hukunci na ƙarshe kan lamarin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamnatinl Rikicin Masarauta har sai Kotun Ƙoli ta yanke hukunci

এছাড়াও পড়ুন:

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

 

A ɓangaren hauhawar farashin abinci a watan Satumba na 2025, ya dawo kashi 20.9 cikin 100 a maimakon kashi 37.77 cikin 100 a cikin watan Satumban 2024

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai 2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa October 15, 2025 Manyan Labarai ‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako October 15, 2025 Manyan Labarai Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara October 15, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotu ta daure kocin kwallon kafa a Kano shekara 8 saboda aikata luwadi
  • Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%
  • Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu
  • Kotun ta umarci a tono gawarwakin wadanda gobara ta kashe a Legas don yin bincike
  • Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta
  • Ni na nema wa Maryam Sanda yafiya —Mahaifin mijinta
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kammala Aikin Titin Abuja–Kaduna–Kano Shekara Mai Zuwa
  • Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet
  • Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA