Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka
Published: 3rd, July 2025 GMT
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp.এছাড়াও পড়ুন:
Yadda matata ta ɓace a Abuja aka tsince ta a Sakkwato
Wani magidanci, Malam Jibrin Rabi’u, ya bayyana yadda matarsa, Khadijat Ado, ta ɓace a gidansu da ke unguwar Life Camp a Abuja a ranar Alhamis da ta gabata, sannan kuma aka gano ta a Sakkwato washegari.
Ya shaida wa wakilinmu da yammacin Lahadi, cewa ya dawo gida a ranar Alhamis, sai ya tarar da matarsa ba ta nan.
Malam Jibril ya ce, ya kira wani abokinsa ɗan sanda, wanda ya sanar da ofishin ’yan sanda na Life Camp, Gwarinpa da sauran sassan yankin bayan bincike na farko ya gagara gano inda take.
A cewarsa, na’urar CCTV da ke gidansu ta nuna yadda matarsa ta fita daga gidan cikin natsuwa, har sai da ta fita daga inda kyamarar ke iya ɗauka.
Allah Ya yi wa Malam Nata’ala rasuwa Fursunan da aka yanke wa hukuncin kisa ya tsere daga gidan yari a YobeMalam Jibrin ya ce duk da ƙoƙarin da suka yi na gano ta a ranar Alhamis ɗin, ba su samu nasara ba.
Sai dai ya ce da yammacin Juma’a aka kira shi aka shaida masa cewa an gano matarsa a Sakkwato, amma ba ta iya magana.
Ya ce, “Yanzu ma har yanzu ba ta iya magana ba, amma ta dawo cikin hayyacinta. Muna tattaunawa ta hanyar rubutu ne kawai.”
Ya bayyana cewa matarsa ta rubuto masa cewa a ranar da ta ɓace, ta ji kamar wani ana kiranta ne, sai ta buɗe ƙofa ta fita — daga nan kuma ba ta san abin da ya faru ba, sai da ta tsinci kanta a Sakkwato.
A cewar Malam Jibrin, “Ta ce da ta isa Sakkwato, ta haɗu da wata mace wadda ta roƙi takarda da biro, sannan ta rubuta mata abin da ya faru domin ba ta iya magana.”
Ya ce daga nan ne wannan matar ta kira shi, inda ya nemi ta da ta kai matarsa wurin danginsa da ke Sakkwato.
Malam Jibrin ya ce har yanzu matarsa tana Sakkwato, kuma ba ta samu damar yin magana ba, amma ya shirya tafiya Sakkwato yau domin ya dawo da ita gida.
Wata majiyar ’yan sanda a Life Camp ya tabbatar da cewa an kawo rahoton ɓacewar a ranar Alhamis, amma ya ce duk wani ƙarin bayani sai an tuntuɓi hedikwatar rundunar.
An kuma bayyana cewa kiraye-kirayen da aka yi wa jami’ar hulɗa da jama’a ta rundunar ’yan sanda ta Abuja, DSP Josephine Adeh, ba ta ɗaga wayarta ba.