Leadership News Hausa:
2025-11-24@00:13:08 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [7]

Published: 15th, March 2025 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [7]

1. Godiya da harshe:
Wannan yana nufin yabon Allah da faɗar ni’imominsa da kuma ambatonsa a cikin kalmomi. Wannan yana da muhimmanci saboda yana nuni da cewa mutum ya gane cewa Allah ne mai bayar da ni’ima. Hadisin da aka kawo yana nuna cewa mutum idan ya bayyana ni’imomin Allah, to yana cikin masu godiya.

Wannan na iya kasancewa ta hanyar zikirai, du’a’i, da yabonsa da albarkar da yake bayarwa, da cewa Allah Ya yi min ni’ima iri kaza da kaza.

2. Godiya da gaɓɓai:
Wannan yana nufin amfani da dukkan gabban jiki wajen yin biyayya ga Allah da nisantar saɓon Sa. Misali, idan mutum yana da lafiyar jiki, to ya yi amfani da lafiyar wajen aikata kyawawan ayyuka kamar sallah, azumi, sadaƙa, da taimakon jama’a. Idan kuma mutum yana da arziki, ya yi amfani da shi wajen tallafa wa marasa hali da hidimtawa addini. Wannan yana tabbatar da cewa godiya ga Allah ba kawai yana cikin harshe ba, har ma yana cikin aiki.

3. Godiya da zuciya:
Wannan yana da alaƙa da imani da ilimi. Yana nufin mutum ya gane cewa duk wata ni’ima daga Allah take, ba wai saboda ya cancanta a ba shi ba saboda wani abu da ya yi wa Allah, a a sai dai domin Allah yana da rahama da falala da jin ƙai. Wannan yana hana girman kai da alfahari, domin mutum zai fahimci cewa Allah Yana bayar da ni’ima a matsayin kyauta, ba lallai ne saboda ibadarsa ba. Wannan yana ƙarfafa tawali’u da jin haƙuri idan mutum bai samu abin da yake so ba.

A taƙaice, maganar Ibnu Juzai tana koyar da cewa godiya ba kawai fadar “Alhamdulillahi” ba ce kawai, a a, tana da sassa guda uku: da suka haɗa da harshe, da aiki, da kuma zuciya. Idan mutum yana godiya ta waɗannan hanyoyi, to zai zama cikakken mai godiya ga Allah. Wannan yana ƙarfafa imani, yana ƙara ni’ima, kuma yana kusantar da bawa ga Ubangijinsa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan Wannan yana

এছাড়াও পড়ুন:

Obi ya yi watsi da hukuncin ɗaurin rai da rai da aka yi wa Kanu

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a zaɓen 2023, Peter Obi, ya soki hukuncin da kotu ta yanke wa jagoran ’yan awaren ƙungiyar Biyafara (IPOB), Nnamdi Kanu.

Obi ya bayyana hukuncin matsayin “abun takaici” kuma alamar gazawar jagoranci.

Sace ɗalibai: An rufe makarantu a Katsina da Taraba Gobara ta lalata gidaje 40 a sansanin ’yan gudun a Borno

A ranar Alhamis ne wata Kotun Tarayya da ke Abuja, ta yanke wa Kanu hukuncin ɗaurin rai da rai bayan samun sa da laifukan ta’addanci.

Sai dai Obi ya ce Gwamnatin Tarayya ta yi kuskure tun daga farko wajen tafiyar da lamarin, kuma bai kamata ya kai wannan mataki ba.

Ya ce Najeriya na fuskantar matsaloli da dama ciki har da tsadar rayuwa, rashin tsaro, da rashin shugabanci na gari, kuma wannan hukunci na iya ƙara tayar da hankali.

“Ƙorafe-ƙorafen da Kanu ya yi ba sabbi ba ne. Suna buƙata hikima, tausayi da sauraro. A wasu ƙasashen, irin waɗannan koke-koke ana magance su ta hanyar tattaunawa da gyare-gyare domin ƙarfafa haɗin kai,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa ƙasashe da dama suna amfani da hanyar siyasa ko sulhu idan hukuncin kotu kaɗai ba zai kawo zaman lafiya ba.

“Wannan abun takaici na iya ƙara tsananta rashin tsaro. Kama shi, tsare shi da hukunta shi alama ce ta gazawar jagoranci da rashin fahimtar matsalar tun da farko,” in ji Obi.

Obi ya yi kira ga gwamnati, dattawa, da shugabannin ƙasa su yi aiki don nemo mafita game da zaman lafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun ƙaryata jita-jitar kai wa coci hari a Gombe
  • An ceto mutum 38 da aka sace a cocin Kwara — Tinubu
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 161
  • Fiye da yara miliyan 400 na fama da talauci a duniya — UNICEF
  • An rufe makarantun Filato saboda matsalar tsaro
  • ’Yan sanda sun daƙile harin ’yan bindiga, sun ceto mutum 25 a Zamfara
  • Obi ya yi watsi da hukuncin ɗaurin rai da rai da aka yi wa Kanu
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 160
  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da sace ɗalibai a Neja
  • ’Yan Bindiga Sun Nemi Miliyan 100 Kudin Fansa Kan Kowane Mutum Ɗaya da Suka Sace a Kwara