Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [7]
Published: 15th, March 2025 GMT
1. Godiya da harshe:
Wannan yana nufin yabon Allah da faɗar ni’imominsa da kuma ambatonsa a cikin kalmomi. Wannan yana da muhimmanci saboda yana nuni da cewa mutum ya gane cewa Allah ne mai bayar da ni’ima. Hadisin da aka kawo yana nuna cewa mutum idan ya bayyana ni’imomin Allah, to yana cikin masu godiya.
2. Godiya da gaɓɓai:
Wannan yana nufin amfani da dukkan gabban jiki wajen yin biyayya ga Allah da nisantar saɓon Sa. Misali, idan mutum yana da lafiyar jiki, to ya yi amfani da lafiyar wajen aikata kyawawan ayyuka kamar sallah, azumi, sadaƙa, da taimakon jama’a. Idan kuma mutum yana da arziki, ya yi amfani da shi wajen tallafa wa marasa hali da hidimtawa addini. Wannan yana tabbatar da cewa godiya ga Allah ba kawai yana cikin harshe ba, har ma yana cikin aiki.
3. Godiya da zuciya:
Wannan yana da alaƙa da imani da ilimi. Yana nufin mutum ya gane cewa duk wata ni’ima daga Allah take, ba wai saboda ya cancanta a ba shi ba saboda wani abu da ya yi wa Allah, a a sai dai domin Allah yana da rahama da falala da jin ƙai. Wannan yana hana girman kai da alfahari, domin mutum zai fahimci cewa Allah Yana bayar da ni’ima a matsayin kyauta, ba lallai ne saboda ibadarsa ba. Wannan yana ƙarfafa tawali’u da jin haƙuri idan mutum bai samu abin da yake so ba.
A taƙaice, maganar Ibnu Juzai tana koyar da cewa godiya ba kawai fadar “Alhamdulillahi” ba ce kawai, a a, tana da sassa guda uku: da suka haɗa da harshe, da aiki, da kuma zuciya. Idan mutum yana godiya ta waɗannan hanyoyi, to zai zama cikakken mai godiya ga Allah. Wannan yana ƙarfafa imani, yana ƙara ni’ima, kuma yana kusantar da bawa ga Ubangijinsa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan Wannan yana
এছাড়াও পড়ুন:
Ɗan Majalisar Wakilai daga Kano Sagir Ƙoƙi ya fice daga NNPP
Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar mazabar Birnin Kano da Kewaye, Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi, ya bayyana ficewarsa a hukumance daga jam’iyyar NNPP.
Ƙoƙ8 inda ya danganta hakan da rikicin shugabanci da ke kara tsananta a cikin jam’iyyar.
PDP ta sha alwashin gudanar da babban taronta duk da umarnin kotu Abdulmumin Jibrin ya koma APC wata 2 bayan NNPP ta dakatar shiA cikin wata wasika mai dauke da kwanan wata 11 ga Nuwamba, 2025, wacce aka aika wa Shugaban jam’iyyar a Unguwar Zaitawa a Karamar Hukumar ta Birni, Koki ya ce ya dauki wannan mataki ne bisa hakkin sa na kundin tsarin mulki na ’yancin shiga ko ficewa daga kowace jam’iyya.
“Bisa ga hakkin da kundin tsarin mulkin Tarayyar Najeriya na 1999 (wanda aka yi wa gyara) ya bani a sashe na 40, da kuma sashe na 7.1 na kundin tsarin mulkin NNPP da sauran dokoki, ina sanar da ficewata daga jam’iyyar NNPP daga ranar Talata, 11 ga Nuwamba, 2025,” in ji shi a cikin wasikar.
Ya bayyana cewa rikicin cikin gida da ya dabaibaye shugabancin jam’iyyar a matakin kasa ya sa shi a tsaka mai wuya, har ma ya zama kusan ba zai iya ci gaba da gudanar da aikinsa yadda ya kamata ba, da kuma samar da ingantaccen wakilci ga al’ummar mazaɓarsa a majalisar.
“Ficewa daga NNPP ya zama dole saboda rikicin shugabanci a matakin ƙasa ya sanya ba zan iya ci gaba da gudanar da aikina ba tare da kawo wakilci nagari ga mutanen Birnin Kano da Kewaye,” in ji shi.
Koki, wanda aka zabe shi a karkashin jam’iyyar NNPP a zaben 2023, ya nuna godiya ga jam’iyyar bisa damar da ta ba shi ya yi aiki, inda ya ce goyon baya da amincewar da ya samu daga ’ya’yan jam’iyyar sun kasance abin alfahari.
“Ina godiya matuka ga jam’iyyar bisa damar da ta bani na yi aiki a karkashinta. Goyon baya, amincewa da kwarewar da na samu a lokacin zama na dan jam’iyya sun kasance masu matukar muhimmanci, kuma ina godiya ga shugabanni da ’ya’yan jam’iyyar a dukkan matakai,” ya kara da cewa.
Sai dai har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ɗan majalisar bai bayyana matakin siyasa na gaba ba ko jam’iyyar da zai shiga ba.
Dama dai tun a watannin baya an sha jin ’yan jam’iyyar ta NNPP na ɗaga masa yatsa saboda yadda suka ce ya cika yin mu’amala da ’yan jam’iyyar APC.
Matakin nasa kuma ma zuwa ne kwana biyu bayan takwaransa naazabar Kiru/Bebeji daga jihar, Abdulmumin Jibrin Kofa, ya sanar da komawa APC watanni biyu bayan an kore daga NNPP.
Kazalika, kafin nan ma, jam’iyyar ta yi asarar Sanata da wasu ’yan majalisar tarayyar guda uku da su ma suka koma APC.