Leadership News Hausa:
2025-11-25@14:00:26 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [7]

Published: 15th, March 2025 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [7]

1. Godiya da harshe:
Wannan yana nufin yabon Allah da faɗar ni’imominsa da kuma ambatonsa a cikin kalmomi. Wannan yana da muhimmanci saboda yana nuni da cewa mutum ya gane cewa Allah ne mai bayar da ni’ima. Hadisin da aka kawo yana nuna cewa mutum idan ya bayyana ni’imomin Allah, to yana cikin masu godiya.

Wannan na iya kasancewa ta hanyar zikirai, du’a’i, da yabonsa da albarkar da yake bayarwa, da cewa Allah Ya yi min ni’ima iri kaza da kaza.

2. Godiya da gaɓɓai:
Wannan yana nufin amfani da dukkan gabban jiki wajen yin biyayya ga Allah da nisantar saɓon Sa. Misali, idan mutum yana da lafiyar jiki, to ya yi amfani da lafiyar wajen aikata kyawawan ayyuka kamar sallah, azumi, sadaƙa, da taimakon jama’a. Idan kuma mutum yana da arziki, ya yi amfani da shi wajen tallafa wa marasa hali da hidimtawa addini. Wannan yana tabbatar da cewa godiya ga Allah ba kawai yana cikin harshe ba, har ma yana cikin aiki.

3. Godiya da zuciya:
Wannan yana da alaƙa da imani da ilimi. Yana nufin mutum ya gane cewa duk wata ni’ima daga Allah take, ba wai saboda ya cancanta a ba shi ba saboda wani abu da ya yi wa Allah, a a sai dai domin Allah yana da rahama da falala da jin ƙai. Wannan yana hana girman kai da alfahari, domin mutum zai fahimci cewa Allah Yana bayar da ni’ima a matsayin kyauta, ba lallai ne saboda ibadarsa ba. Wannan yana ƙarfafa tawali’u da jin haƙuri idan mutum bai samu abin da yake so ba.

A taƙaice, maganar Ibnu Juzai tana koyar da cewa godiya ba kawai fadar “Alhamdulillahi” ba ce kawai, a a, tana da sassa guda uku: da suka haɗa da harshe, da aiki, da kuma zuciya. Idan mutum yana godiya ta waɗannan hanyoyi, to zai zama cikakken mai godiya ga Allah. Wannan yana ƙarfafa imani, yana ƙara ni’ima, kuma yana kusantar da bawa ga Ubangijinsa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan Wannan yana

এছাড়াও পড়ুন:

Slot na fuskantar matsin lamba saboda rashin kataɓus a Liverpool

Kociyan ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Liverpool, Arne Slot, na fuskantar matsin lamba saboda rashin kataɓus da ƙungiyar ke fama da shi a bayan nan.

A yammacin jiya Lahadi ne Nottingham Forest ta je har filin wasa na Anfield, inda ta lallasa Liverpool da ci 3-0 a wasan mako na 12 na gasar Firimiyar Ingila.

Mayaƙan Boko Haram sun file kan mata 2 a Borno Ɗaya daga cikin ’yan matan da ISWAP ta sace a Borno ta tsere

Forest ta samu nasarar ce ta hannun Murillo a minti na 33, sai Nicolo Savona a minti na 46, sannan Morgan Gibbs-White ya ƙara na uku a minti na 78.

Sakamakon wannan rashin nasarar, Liverpool ta sauka zuwa mataki na 11 da maki 18, yayin da ita kuwa Nottingham Forest ta matsa zuwa mataki na 16 da maki 12 a teburin gasar.

Kawo yanzu dai, cikin wasanni 12 da Liverpool ta buga a gasar Firimiya, ta samu nasara a wasanni 6 ne kaɗai, sannan an doke ta a sauran 6.

Wannan mummunar rashin nasara ta sake dagula wa mai horar da ƙungiyar, Arne Slot, al’amura, musamman ganin irin matsin lambar da yake fuskanta daga magoya bayan ƙungiyar a bana.

A yanzu, hankalin mai horarwar ya koma kan wasan Champions League da za su yi da PSV a ranar Laraba.

Samun nasara a wannan wasa na iya zama abin da zai ba shi damar sauƙin numfasawa; akasin haka kuma, na iya haifar masa da babbar matsala daga mahukuntan kulob ɗin da magoya bayan da ke ƙara nuna rashin haƙuri.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Titi Mai Tsawon Kilomita 13 a ‘Yankwashi
  • An rufe duk makarantu a Jihar Bauchi saboda matsalar tsaro
  • Slot na fuskantar matsin lamba saboda rashin kataɓus a Liverpool
  • Ɗaya daga cikin ’yan matan da ISWAP ta sace a Borno ta tsere
  • An rufe duk makarantu a Jihar Bauchi na saboda matsalar tsaro
  • ’Yan sanda sun ƙaryata jita-jitar kai wa coci hari a Gombe
  • An ceto mutum 38 da aka sace a cocin Kwara — Tinubu
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 161
  • Fiye da yara miliyan 400 na fama da talauci a duniya — UNICEF
  • ’Yan sanda sun daƙile harin ’yan bindiga, sun ceto mutum 25 a Zamfara