Rahoton Majalisar Dinkin Duniya mai ban tsoro ya bayyana cewa: Manyan kamfanoni suna da hannu wajen aiwatar da kisan kare dangi a Gaza

Wani rahoto da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar ya bayyana sunayen wasu manyan kamfanoni na duniya sama da 60 da ke da hannu a tallafawa wajen gine-ginen matsugunan yahudawa ‘yan kaka gida a yankunan gabar yammacin kogin Jordan da kuma hare-haren wuce gona da iri kan Zirin Gaza.

Rahoton wanda wakiliyar Majalisar Dinkin Duniya na musamman kan halin da ake ciki na kare hakkin bil adama a yankunan Falasdinawa da aka mamaye, Francesca Albanese, ta wallafa ya samo asali ne daga bayanai sama da 200 daga kasashe, kungiyoyin kare hakkin bil adama, masana ilimi da kamfanoni. Ta yi kira ga kamfanonin da su daina kasuwanci da haramtacciyar kasar Isra’ila, ta kuma yi tambayar cewa saboda rike harkokin gudanarwar kudade da kuma doka da oda don fa’idarsu da suke samu daga hare-haren da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke kai wa yankunan Falasdinawa.

Daga cikin kamfanonin da aka ambata a cikin rahoton, mafiya shahararsu akwai kamfanonin Amurka: Google, Microsoft, IBM, Caterpillar, a heavy equipment manufacturer, Lockheed Martin, a military manufacturer, da Hyundai na kasar Koriya ta Kudu. Rahoton ya zarge su da hannu a ayyukan danniya, kera makamai, da lalata dukiyoyi a yankunan Falasdinu.

Rahoton yana wakiltar fadada jerin sunayen da aka baiwa  Majalisar Dinkin Duniya a shekara ta 2023 wanda ya mayar da hankali kawai kan kamfanonin da ke da alaka gwamnatin mamaya, yayin da sabon rahoton ya kunshi bangarori masu fadi da ke da alaka da cin zarafi a Gaza. Albanese ta gabatar da wannan zargi a cikin wani cikakken bayani game da rikicin Falasdinu: “Yayin da ake kashe rayuka a Gaza kuma ake ci gaba da kara kashe-kashen a gabar yammacin kogin Jordan, wannan rahoto ya nuna cewa kisan kiyashin da ake kira ya ci gaba ne kawai saboda yana da riba ga bangarori da yawa.”

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Majalisar Dinkin Duniya

এছাড়াও পড়ুন:

Kudurorin Kafa Hukumomi 3 Sun Tsallake Karatu Na 2 A Majalisar Dokokin Jihar Jigawa

Wasu kudurori guda 3 da ke dauke da bukatun kafa wasu hukumomi 3 sun samu karatu na biyu a zauren majalaisar dokokin jihar Jigawa.

Kudurorin guda 3 sun hada da na kafa Hukumar Samar da Hanyoyin Mota a yankunan karkara, da na kafa Hukumar Samar da Kudade Domin Ayyukan Hanyoyin Mota a yankunan karkara da Kuma na Hukumar Bunkasa Kwazon Malamai ta jihar Jigawa.

A lokacin ya ke gabatar da kudurorin domin neman goyon baya kan bukatar kafa hukumar bunkasa kwazon malamai, mataimakin shugaban masu rinjaye na majlaisar, Alhaji Sani Sale Zaburan ya ce gwamnatin jihar na da nufin inganta aikin koyarwa ta hanyar kafa hukumar da za ta rinka horas da malamai akai akai.

Da su ke tattaunawa kan wannan batu, wakilan mazabar Kanya Babba da na Fagam da na Sule Tankarar da na Guri, sun lura cewa kafa wannan hukumar zai maye gurbin ayyukan kwalejin horas da malamai da aka rushe a can baya, abin da zai kawo ingancin harkonin koyo da koyarwa a halin yanzu.

Kazalika da ya ke gabatar da kudurin neman goyon baya kan batun kafa hukuma da kuma asusun samar da hanyoyin mota a yankunan karkara, mataimakin shugaban masu rinjaye na majalisar, Alhaji Sani Sale Zaburan ya ce daukar wannan mataki zai karfafa yunkurin gwamnatin jihar na inganta harkokin sufuri ga jama’ar karkara.

Da su ke bada gudummawa kan wannan batu, wakilin mazabar Gwaram da na Kiri Kasamma da na Guri da kuma wakilin mazabar Fagam sun bayyana kudurorin biyu a matsayin wata alama da ke nuni da kyakkyawan kudurin gwamnatin Malam Umar Namadi wajen samar da hanyoyin mota ga yankunan karkara, inda fiye da kaso 60 na jama’ar jihar ke zaune.

Bayan samun goyon baya da gagarumin rinjaye sai aka yiwa kudurorin 3 karatu na 2, daga nan kuma shugaban majalisar dokokin jihar, Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin ya mika kudurori 2 na hanyoyin mota a yankunan karkara ga kwamatin muhalli, yayin da kudurin kafa hukumar inganta kwazon malamai ya je ga kwamatin ilimi mai zurfi da na ilimi matakin farko, wanda dukkan su aka bai wa makonni 4 domin mika rahotannin su.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kudurorin Kafa Hukumomi 3 Sun Tsallake Karatu Na 2 A Majalisar Dokokin Jihar Jigawa
  • A Lokacin Yaki, Iran Ta Tarwatsa Wata Cibiyar Leken Asirin Yahudawan Sahayoniyya Da Ke Yankin Farar Hula
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Bayyana Cewa: Sake Gina Gaza Zai Ci Dala Biliyan 70
  • Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata
  • Cirar kudin kwastoma: Majalisa ta gayyaci CBN da bankuna
  • Rasha ta kai wa tawagar kayan agajin MDD hari a Ukraine
  • Mahalarta Taron ‘Sherm-Sheikh” Sun Rattaba Hannu Akan Yarjejeniyar Zaman Lafiya
  • Falasdinawa Sun Gano Gawakin Wadanda HKI Ta Kashe A gaza  Fiye Da 320 Cikin Kwanaki Biyu Kacal
  • Yaƙin Gaza: Hamas da Isra’ila sun fara sakin fursunoni
  • Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth