Sojojin mamayar Isra’ila sun kai munanan hare-hare kan Falasdinawa da suka rasa gidajensu da fama da masifar yunwa, lamarin da ya yi sanadiyar shahadan mutane da dama

Gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila tana ci gaba da aiwatar da kisan kiyashi kan ‘yan gudun hijira da kuma wadanda ke jiran agaji a zirin Gaza, inda a daren jiya zuwa safiyar Alhamis, hare-haren wuce gona da irinsu suka yi sanadiyar shahadan Falasdinawa da dama, tare da jikkata wasu baya ga bacewar wai adadi mai yaw ana mutane a karkashin baraguzan gine-gine.

Asibitin Al-Shifa ya sanar da shahadan fararen hula 11 da suka hada da yara da mata a wani sabon kisan kiyashi da sojojin mamayar Isra’ila suka aikata ta hanyar kai hare-haren bama-bamai kan makarantar Mustafa Hafez da ke matsayin mafaka ga ‘yan gudun hijira a yammacin birnin Gaza.

Sannan a wani kisan kiyashi kuma, fararen hula 13 da suka hada da mata da kananan yara ne suka yi shahada a lokacin da jiragen yakin mamayar Isra’ila suka kai hare-hare kan wani tanti da ‘yan uwa Abu Asi suka yi gudun hijira ciki, kusa da masallacin Al-Aqqad da ke unguwar Mawasi a Khan Yunis. Wasu da dama kuma suka jikkata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa

 

‘Yan sa’o’i kafin sanarwar da Jam’iyyar ta RN ta yi ne dai, tsohon Firaministansa Edouard Philippe ya ce yana goyon bayan shirya sabon zaben shugaban kasa a gaggauce.

 

Wannan matsin lamba dai kari ne kan wadda shugaban na Faransa ke fusakanta daga bangaren masu sassaucin ra’ayi, wadanda su kuma bukatarsu ita ce a zabi sabon Firaminista daga cikinsu.

 

Sai dai a iya cewa akwai ragowar fatan kawo karshen rudanin da siyasar Faransar ta shiga, la’akari da bayanan da suka ce a dazu an shiga tattaunawa tsakanin jagoran jam’iyyar masu ra’ayin ‘yan mazan jiya Bruno Retailleau da Firaminista Lecournu, kwana guda bayan murabus din da ya yi. Yayin da kuma a gefe guda rahotanni suka ce a gobe Laraba wakilan masu sassaucin ra’ayi na jam’iyyar Socialist za su gana da Firaminista Lecournun mai murabus.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Ko Afirka Za Ta Samu Kujerar Dindindin A Kwamitin Tsaro Na Majalisar Dinkin Duniya? October 12, 2025 Manyan Labarai Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna  October 12, 2025 Rahotonni Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya October 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Madagaska sun karbe mulkin kasar
  • Ya kamata ‘yan fim su rika taimaka wa kananan cikinsu-Rukayya Abdullahi
  • Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano
  • Yaƙin Gaza: Hamas da Isra’ila sun fara sakin fursunoni
  • Yemen Ta Gargadi Isra’ila Kan Fuskantar Hare-Hare Idan Ta Karya Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta
  • ‘Yan Kamaru na kada kuri’a a zaben shugaban kasar
  • Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka
  • Arachi: HKI Ba Abar Amincewa Ba Ce, Falasdinawa Su Yi Hattara
  • An Gudanar Da Taron ‘Farkawar Musulmi’ A Nan Tahren Inda Ka Tattauna Batun Falasdinu
  • Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa