Sojojin mamayar Isra’ila sun kai munanan hare-hare kan Falasdinawa da suka rasa gidajensu da fama da masifar yunwa, lamarin da ya yi sanadiyar shahadan mutane da dama

Gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila tana ci gaba da aiwatar da kisan kiyashi kan ‘yan gudun hijira da kuma wadanda ke jiran agaji a zirin Gaza, inda a daren jiya zuwa safiyar Alhamis, hare-haren wuce gona da irinsu suka yi sanadiyar shahadan Falasdinawa da dama, tare da jikkata wasu baya ga bacewar wai adadi mai yaw ana mutane a karkashin baraguzan gine-gine.

Asibitin Al-Shifa ya sanar da shahadan fararen hula 11 da suka hada da yara da mata a wani sabon kisan kiyashi da sojojin mamayar Isra’ila suka aikata ta hanyar kai hare-haren bama-bamai kan makarantar Mustafa Hafez da ke matsayin mafaka ga ‘yan gudun hijira a yammacin birnin Gaza.

Sannan a wani kisan kiyashi kuma, fararen hula 13 da suka hada da mata da kananan yara ne suka yi shahada a lokacin da jiragen yakin mamayar Isra’ila suka kai hare-hare kan wani tanti da ‘yan uwa Abu Asi suka yi gudun hijira ciki, kusa da masallacin Al-Aqqad da ke unguwar Mawasi a Khan Yunis. Wasu da dama kuma suka jikkata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Aragchi: Iran Ba zata Taba Daina Tace Makamashin Uranium A Cikin Gida Ba

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa shirin makamashin nukliya na kasar Iran kuma na zaman lafiya ya zama abin alfakhari ga mutanen kasar da daukaka. Don haka gwamnati mutanen kasar ba zasu taba yarda a barshi ba.

Ministan ya bayyana haka ne a lokacin da yake hira da tashar talabijin ta CBS news na kasar Amurka dangane da hare-haren da HKI da kuma Amurka suka kaiwa kasar a cikin watan yuni da ya gabata. Hare-haren  da aka kaiwa kasar a dai-dai lokacinda take tattaunawa da Amurka.

A wani bangare a maganars Aragchi ya bayyana cewa baya ganin Iran zata farfado da tattaunawa da kasar Amurka nan kusa.

Ya ce: Idan har zamu sake shiga tattaunawa da Amurka sai mun tabbatar da cewa Amurka ba zata kuma kai mana hare-hare a dai-dai lokacinda muke tattaunawa ba.

Ya kara da cewa, tare da wannan tunanin muna ganin sake zama da Amurka kan teburin tattauna ba nan kusa ba. Daga karshe ya ce: a duk sanda muka ga dama ta samu, bama rufe kofar tattaunawa da kowa .

Da aka tamabaye shi dangane da shirin makamashin Nukliya na kasar bayan bom da aka jefa masu. Ministan ya ce: Ai ba’a kauda shirin nukliya da bom. Ko babu shi kwata-kwata zamu sake gina wani daga farko. Sannan idan sun baci ne muna iya sake gyaransu sai mu ci gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwamandan Sojojin Iran Ya Ziyarci Gidan Babban Jami’in Sojin Kasar Da Ya Yii Shahada Lokacin Yakin Baya-Bayan Nan
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Fitar Da Rahoton Wadanda Suke Taimakawa ‘Yan Sahayoniyya Wajen Murkushe Falasdinawa
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Irin Aniyar Da Gwamantinsa Ta Kudurta Wajen Kare Tsaron Kasa Da Al’ummarta
  • Kasar Iran Ta Nuna Ire-Iren Makamai Masu Linzami Da Ta Mayar Da Martani Da Su Kan ‘Yan Mamaya
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Yi Luguden Bama-Bamai Kan Falasdinawa Da Suka Janyo Shahada Da Jikkata
  • Aragchi: Iran Ba zata Taba Daina Tace Makamashin Uranium A Cikin Gida Ba
  • Wakilan Kasashen Duniya Da Kungiyoyin Sun Je Ta’aziyya Mutanen Da Suka Yi Shahada A Yakin Iran Da H.K.Isra’ila
  • Magajin Garin Birnin Tehran Ya Karyata Da’awar ‘Yan Sahayoniyya
  • An Kashe Kusan Mutane 1500 Kan Sabanin Mazhaba A Kasar Siriya A Wata Guda