Aminiya:
2025-09-17@23:24:33 GMT

Ambaliya da iska sun rushe gidaje 171 a watanni biyu a Gombe – SEMA

Published: 4th, July 2025 GMT

Hukumar Bayar da agajin gaggawa ta Jihar Gombe (SEMA) ta bayyana cewa, ambaliya da iska mai ƙarfi sun rushe da lalata gidaje 171 a yankunan jihar cikin watanni biyu da suka gabata, lamarin da ya haddasa asara da kuma mutuwar yara huɗu.

Sakataren zartarwa na Hukumar SEMA, Malam Abdullahi Haruna Abdullahi ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Gombe, inda ya ce iftila’in ya shafi ƙananan hukumomin Dukku da Kwami da Gombe da Akko.

Harin Filato: Remi Tinubu ta ba da gudummawar Naira biliya 1 Buhari ba ya cikin mawuyacin hali — Bashir Ahmad

“Mun samu rahoton rushewar gidaje 87 a Dukku, 27 a Kwami, 30 a Gombe da kuma 27 a Akko, ciki har da wata coci da ambaliya ta lalata.

Haka kuma yara huɗu sun rasa rayukansu, mafi yawansu yara ne,” in ji shi.

Ya bayyana cewa, rashin tsaftar muhalli da kuma yawan sare bishiyoyi na daga cikin abubuwan da suka taimaka wajen haddasa ibtila’in.

Ya yi kira ga al’umma da su daina zubar da shara a cikin magudanan ruwa, tare da amfani da wuraren zubar da shara da gwamnatin jihar ta gina.

“Akwai buƙatar kowa ya taka rawar gani wajen kare muhallinsa, musamman a lokacin damina.

Iyaye su kula da ‘ya’yansu, musamman ma yara ƙanana domin gudun afkuwar hatsarin faruwar hakan,” in ji Malam Abdullahi.

Sakataren SEMA ya kuma yi tir da yawan sare bishiyoyi domin yin gawayi na girki, yana mai cewa hakan yana ƙara haddasa fari da kuma rushewar muhalli.

Sai ya shawarci jama’a su ci gajiyar daminar da ake ciki wajen dasa bishiyoyi a gidajensu da unguwanninsu domin rage ƙarfi da haɗarin iska da kuma yaƙi da hamada.

Malam Abdullahi ya ƙara da cewa, Hukumar SEMA na shirin kai kayan tallafi ga waɗanda ibtila’in ya shafa a sassan jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kwami

এছাড়াও পড়ুন:

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Hukumar NDLEA ta bayyana cewa wata ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi ce a filin jirgin sama na Kano ta boye jakunkunan ƙwayoyi a cikin kayan matafiyan.

An kama shugaban ƙungiyar, Ali Abubakar Mohammed (wanda aka fi sani da Bello Karama), tare da wasu abokan aikinsa.

Hukumar ta ce mutanen ukun ba su da laifi kuma an zalunce su ne kawai.

An saki su ne bayan bincike da kuma ƙoƙarin diflomasiyya na tsawon makonni.

Lamarin ya tayar da hankali kan tsaro a filayen jirgin sama a Nijeriya da yadda masu aikata laifuka ke amfani da fasinjoji marasa laifi.

Hukumar ta ce za a ɗauki ƙarin matakai don hana faruwar irin wannan lamari.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku
  • Burkina Faso: Masu Ikirarin Jihadi Sun Kashe Fararen Hula 50 A Cikin Watanni Hudu
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha