Aminiya:
2025-07-04@03:43:23 GMT

Ambaliya da iska sun rushe gidaje 171 a watanni biyu a Gombe – SEMA

Published: 4th, July 2025 GMT

Hukumar Bayar da agajin gaggawa ta Jihar Gombe (SEMA) ta bayyana cewa, ambaliya da iska mai ƙarfi sun rushe da lalata gidaje 171 a yankunan jihar cikin watanni biyu da suka gabata, lamarin da ya haddasa asara da kuma mutuwar yara huɗu.

Sakataren zartarwa na Hukumar SEMA, Malam Abdullahi Haruna Abdullahi ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Gombe, inda ya ce iftila’in ya shafi ƙananan hukumomin Dukku da Kwami da Gombe da Akko.

Harin Filato: Remi Tinubu ta ba da gudummawar Naira biliya 1 Buhari ba ya cikin mawuyacin hali — Bashir Ahmad

“Mun samu rahoton rushewar gidaje 87 a Dukku, 27 a Kwami, 30 a Gombe da kuma 27 a Akko, ciki har da wata coci da ambaliya ta lalata.

Haka kuma yara huɗu sun rasa rayukansu, mafi yawansu yara ne,” in ji shi.

Ya bayyana cewa, rashin tsaftar muhalli da kuma yawan sare bishiyoyi na daga cikin abubuwan da suka taimaka wajen haddasa ibtila’in.

Ya yi kira ga al’umma da su daina zubar da shara a cikin magudanan ruwa, tare da amfani da wuraren zubar da shara da gwamnatin jihar ta gina.

“Akwai buƙatar kowa ya taka rawar gani wajen kare muhallinsa, musamman a lokacin damina.

Iyaye su kula da ‘ya’yansu, musamman ma yara ƙanana domin gudun afkuwar hatsarin faruwar hakan,” in ji Malam Abdullahi.

Sakataren SEMA ya kuma yi tir da yawan sare bishiyoyi domin yin gawayi na girki, yana mai cewa hakan yana ƙara haddasa fari da kuma rushewar muhalli.

Sai ya shawarci jama’a su ci gajiyar daminar da ake ciki wajen dasa bishiyoyi a gidajensu da unguwanninsu domin rage ƙarfi da haɗarin iska da kuma yaƙi da hamada.

Malam Abdullahi ya ƙara da cewa, Hukumar SEMA na shirin kai kayan tallafi ga waɗanda ibtila’in ya shafa a sassan jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kwami

এছাড়াও পড়ুন:

 Arakci Ya Mayar Wa Da Jami’ar Harkokin Wajen ” EU” Martani

Minstan harkokin wajen Iran Abbas Arakci ya mayar da martani da kakkausar murya akan furucin jami’ar diplomasiyya ta tarayyar turai Kaya Jallas na cewa Iran ta dakatar da shirinta na makamashin Nukiliya, yana mai cewa; Jallas ta jahilci abinda dokokin NPT su ka kunsa.

Abbas Arakci ya ce; Idan manufar ganawa da kwamitin hadin gwiwa akan yarjeniyar Nukilar iran shi ne kawo karshen Shirin makamashin Nukiliyar Iran, to kuwa Jallas ta jahilci abinda yake kunshe a cikin yarjejeniyar hana yaduwar makaman Nukiliya.

Ita dai babbar jami’ar harkokin wajen tarayyar turai Jallas ta rubuta sako a shafinta na X cewa; Ya zama wajibi a bude tattaunawa da sauri da Iran akan yadda za ta kawo karshen shirinta na makamashin Nukiliya, kuma ficewa daga yarjejeniyar NPT ba zai zama mai taimakawa ba wajen warware batun da yake da alaka da Shirin makamashin Nukiliyar Iran.

Arakci ya kuma ce ; Wannan yana nufin cewa; rawar da tarayyar turai da kuma Birtaniya za su taka a cikin duk wata tattaunawa a nan gaba, za ta zama maras ma’ana.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Jigawa Ta Isa Roni A Ci Gaba Da Rangadin Kananan Hukumomi
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Harin Kan Cibiyar Makamashin Nukiliya Cin Amanar Diflomasiyya Ce
  • Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
  •  Arakci Ya Mayar Wa Da Jami’ar Harkokin Wajen ” EU” Martani
  • An Hori Ma’aikatan Lafiya Su Kara Kokari Wajen Rike Aikin su
  • ’Yan sanda sun kama wani mutum da jabun kuɗi a Gombe
  • Ambaliya: Zulum ya bada umarnin tallafa wa mutanen Damboa da Askira-Uba
  • Karamar Hukumar Maru Ta Bukaci A Dauki Matakan Kariya Kan Cutar Kwalaraci
  • Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato