Aminiya:
2025-09-17@23:12:45 GMT

Harin Filato: Remi Tinubu ta ba da gudummawar Naira biliya 1

Published: 3rd, July 2025 GMT

Uwargidan shugaban ƙasa, Remi Tinubu ta bayar da gudummawar Naira biliyan ɗaya ga waɗanda harin ya rutsa da su a wasu yankunan Jihar Filato.

Uwargidan shugaban ƙasar wacce ta bayyana bayar da tallafin a yayin ziyarar jaje da ta kai jihar a ranar Alhamis, ta ce kuɗaɗen da ta bayar ba na gwamnati ba ne, kuɗin ta ne da ta tara don taimakawa wasu.

Buhari ba ya cikin mawuyacin hali — Bashir Ahmad ’Yan Majalisar Wakilai bakwai na Akwa Ibom sun koma APC

“A yau na zo da gudunmawar Naira biliyan 1 don shirin sabuwar Najeriya (Renewed Hope Initiative), ba ni da maƙudan kuɗaɗe, amma abin da nake da shi shi ne in taimaki rayuwar wasu, ba wai in zuba kuɗi a kwandon ajiya ba.

“Idan da na ajiye kuɗi don amfanin kaina, hakan zai taimaka ne kawai don biyan buƙata ta kawai, amma burina shi ne in yi amfani da kadarar da nake da su wajen kyautatawa ƙasar nan, don ci gaban ƙasar nan, ba wai in ɓarnatar da su ba.

“Don Allah ku fahimci cewa kuɗin da nake da shi na wannan shiri ba na gwamnati ba ne, kuɗi ne na kaina da na tara don in taimaka wa wasu, yayin da nake ci gaba da tafiye-tafiye na ga tasirin ayyukanmu, ina roƙon ku da ku yi addu’a domin mu kawo canji mai ɗorewa.

“Na yi ta addu’a musamman ga waɗanda ambaliyar ruwa ta shafa a wasu wurare ma, na yi ta addu’a cewa damina ta ciyar da ƙasa da abinci kada ta lalata amfanin gonar, Ubangiji ya ji addu’armu, kuma za mu ziyarci wasu wuraren da ake buƙatar tallafi kamar Binuwai da Neja.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu

এছাড়াও পড়ুন:

An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin

Hukumar jin daɗin jama’a ta Jihar Kwara tare da haɗin gwiwar Hukumar Gyaran Hali ta Najeriya sun kama wasu mabarata a titunan Ilorin, ciki har da wasu da aka samu da kuɗaɗen ƙasashen waje.

Daga cikin waɗanda aka kama akwai wani mabaraci mai suna Musa Mahmud daga Jihar Kano, wanda aka samu da takardar daloli.

Musa Mahmud ya shaida wa manema labarai cewa wani ne ya ba shi takardar Dala a Abuja.

Jami’ai sun bayyana damuwa kan yadda masu bara ke riƙe da kuɗaɗen da ba su dace da yanayin rayuwarsu ba.

Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki Cire tallafin man fetur shi ne abin da ya dace —Sarki Sanusi II

“Za mu bincika asalin waɗannan kuɗaɗen da kuma dalilin da ya sa suke da su,” in ji Adebayo Okunola, shugaban cibiyar gyaran hali a Jihar Kwara.

Jami’an gwamnati sun kwashe kusan mutane 40 daga wuraren da suka haɗa da Tipper Garage, Offa Garage, Tank da Geri Alimi Roundabout.

Jami’an sun ce bakwai daga cikin waɗanda aka kama an taɓa kama su a baya, amma sun koma tituna bayan an sako su.

Kwamishinar jin daɗin jama’a ta jihar, Dakta Mariam Imam, ta ce adadin masu bara da aka kama ya ragu sosai idan aka kwatanta da na baya, inda ta ce suna sauya dabaru don su guje wa kama.

Ta roƙi jama’a da su daina ba wa masu bara kuɗi kai tsaye, su maida gudummawarsu ta hanyar wuraren  ibada da gidajen marayu.

Jami’an gyaran hali sun ce za a tilasta wa waɗanda aka kama su yi aikin tsaftace tituna a matsayin horo da kuma darasi.

Wasu daga cikin masu barar sun roƙi gwamnati da ta tausaya musu, ba su da wata hanyar rayuwa sai bara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
  • Iran Ta Bukaci IAEA Tayi Tir Da Harin Da Isra’ila Ta Kai A Tashoshin Nukiyarta.
  • Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin
  • Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar
  • Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya