Babban magatakardar MDD Antonio Gutress ta sanar da kaduwarsa da kuma jin haushin yadda wahalhalun Falasdinawa a Gaza suke karuwa, yana mai cewa: Sauran abinda ya rage da zai rike rayuwa a Gaza, ya kusa karewa saboda rufe hanyoyin da suke shiga Gaza da HKI ta yi.

Kakakin babban magatakardar na MDD  Stephen Dujarric, ne ya ambato maigidan nasa yana fadin haka akan yanayin da zirin Gaza yake ciki, tare da kuma da cewa; MDD tana son ganin an bai wa fararen hula kariya da kuma biya musu bukatunsu.

Antonio Guterres ya kuma bayyana firgitarsa a lokaci daya kuma da bacin ransa akan yadda Falasdinawan Gaza su ka cikin mawuyacin hali, yana mai kara da cewa da akwai adadi mai yaw ana Falasdinawan da aka kashe a cikin kwanakin bayan nan saboda hare-haren Isra’ila a cikin sansanon da ‘yan hijira suke rayuwa a ciki, haka nan kuma Falasdinawan da suke kokarin samun taimakon abinci.

Babban magatakardar MDD ya yi Allawadai da kashe fararen hula yana mai kara da cewa; A cikin wannan makon kadai, Falasdinawan da su ka yi hijirar dole sun kai 30,000 bayan da Isra’ila ta umarce su, su fice daga yankunansu a ranar Lahadin da ta gabata.

Hakan nan kuma Guttress ya ambaci rashin mafaka da abinci a Gaza, kuma babu magunguna da ruwan sha.

Bugu da kari ya ce yanzu an dauki makwanni 17 ba a shigar da makamashi cikin yankin na Gaza ba, tare da cewa, abinda yake rike rayuwa a cikin yankin yana gab da karewa.

Tun a watan Oktoba na 2023 ne dai HKI take tafka laifukan yaki akan al’ummar Falasdinu babu kakkautawa. Ya zuwa yanzu adadin Falasdinawan da su ka yi shahada sun kai 100,000, wadanda su ka jikkata dubun dubata ne, mafi yawancinsu mata da kananan yara.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Falasdinawan da

এছাড়াও পড়ুন:

Za mu ɗauki mataki kan mambobinmu da ke shirin shiga haɗakar ADC — PDP

Babbar jam’iyyar hamayya a Nijeriya, PDP ta ce za ta ɗauki tsattsauran mataki kan mambobinta da ke ƙoƙarin shiga sabuwar haɗaka da jam’iyyar ADC.

Yayin da yake jawabi ga manema labarai bayan taron kwamitin amintattun jam’iyyar, shugaban jam’iyyar na ƙasa Ambasada Iliya Damagum ya ce jam’iyyar tana gargaɗi ’yan’yanta da ke shirin shiga sabuwar haɗakar ADC.

Damagum ya ce ƙoƙarin da haɗakar ke shirin yi ba zai yi tasiri ba, yana mai cewa da dama daga cikin mambobin haɗakar za su koma jam’iyyunsu.

“Yana da kyau su sani cewa babu inda ya kamata a haɗu domin tunkarar gwamnatin APC da ya wuce jam’iyyar PDP, amma in suna ganin ba haka ba, to su je su gwada su gani, amma dai na san dole za su dawo”, in ji shi.

Shugaban riƙon ya kuma gargaɗi ’yan PDP da ya ce suna ƙoƙarin “sayar da jam’iyyar”.

Kawo yanzu dai akwai jiga-jigan PDP cikin sabuwar haɗakar ta ADC, ciki har da tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar a zaɓen da ya gabata, Atiku Abubakar.

A farkon makon nan ne dai jam’iyyar PDP ta gudanar da taronta na Kwamitin Zartaswa da a ciki ta ce ta ɗinke ɓarakar da ta ɗauki tsawon lokacin tana fama da ita a cikin jam’iyyar.

Mun shirya fito-na-fito da APC — Malami

Shi ma dai tsohon Ministan Shari’a, Abubakar Malami ya ce a shirye haɗakar ADC take wajen yaƙi da gwamnatin APC domin kawo “gyara kan yadda ake tafiyar da gwamnati.”

Malami —wanda ya kasance minista a zamanin gwamnatin tsohon shugaban Nijeriya, Mumammadu Buhari — ya ce ukuɓar da gwamnati Tinubu ta sanya talakawan Nijerya a ciki ba za ta misaltu ba.

A hirarsa da BBC, Abubakar Malami ya ce sun fito fili ne domin su yaƙi jam’iyyar APC mai mulki, musamman yadda ta bar abubuwa da dama sun tabarbare a ƙasar, ciki har da tsaro da tattalin arziki da kuma sauran dangogin wahalhalu da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta jefa talakawa.

“A duk lokacin da wata tarayya ta zo da wasu tsare-tsare na ƙuntata wa al’umma, da sanya su cikin halin wahala to wajibi a taru wuri guda su dauki mataki domin kawo sauyi ta hanyar maido da kaykkyawan tsari, da zai ɗaɗa wa mutane”, in ji shi.

“Mun yanke hukuncin ɗaukar mataki domin yaƙi da rashin tsaro da ynuwa domin maido da Nijeriya kan turba mai kyau da tsari”, in ji Malami.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi
  • ‘Yan Nijeriya Na Kewar Gwamnatin Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi
  • Jalali: Mun  Hana Fitowar Sanadarorin Nukiliya Ta Hanyar Aiki Da Ka’idojin Tsaro
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Fitar Da Rahoton Wadanda Suke Taimakawa ‘Yan Sahayoniyya Wajen Murkushe Falasdinawa
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Fitar Da Rahoton Wadanda Suke Taimakawa Yahudawan Sahayoniyya Wajen Murkushe Falasdinawa
  • Ben Gafir Ya Bukaci Gwamnatin HKI Ta Mamaye Yankin Gaza Gaba daya
  • Za mu ɗauki mataki kan mambobinmu da ke shirin shiga haɗakar ADC — PDP
  • Isra’ila na bincike kan harin dakarunta da ya kashe fararen hula a Gaza
  • Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba