Babban magatakardar MDD Antonio Gutress ta sanar da kaduwarsa da kuma jin haushin yadda wahalhalun Falasdinawa a Gaza suke karuwa, yana mai cewa: Sauran abinda ya rage da zai rike rayuwa a Gaza, ya kusa karewa saboda rufe hanyoyin da suke shiga Gaza da HKI ta yi.

Kakakin babban magatakardar na MDD  Stephen Dujarric, ne ya ambato maigidan nasa yana fadin haka akan yanayin da zirin Gaza yake ciki, tare da kuma da cewa; MDD tana son ganin an bai wa fararen hula kariya da kuma biya musu bukatunsu.

Antonio Guterres ya kuma bayyana firgitarsa a lokaci daya kuma da bacin ransa akan yadda Falasdinawan Gaza su ka cikin mawuyacin hali, yana mai kara da cewa da akwai adadi mai yaw ana Falasdinawan da aka kashe a cikin kwanakin bayan nan saboda hare-haren Isra’ila a cikin sansanon da ‘yan hijira suke rayuwa a ciki, haka nan kuma Falasdinawan da suke kokarin samun taimakon abinci.

Babban magatakardar MDD ya yi Allawadai da kashe fararen hula yana mai kara da cewa; A cikin wannan makon kadai, Falasdinawan da su ka yi hijirar dole sun kai 30,000 bayan da Isra’ila ta umarce su, su fice daga yankunansu a ranar Lahadin da ta gabata.

Hakan nan kuma Guttress ya ambaci rashin mafaka da abinci a Gaza, kuma babu magunguna da ruwan sha.

Bugu da kari ya ce yanzu an dauki makwanni 17 ba a shigar da makamashi cikin yankin na Gaza ba, tare da cewa, abinda yake rike rayuwa a cikin yankin yana gab da karewa.

Tun a watan Oktoba na 2023 ne dai HKI take tafka laifukan yaki akan al’ummar Falasdinu babu kakkautawa. Ya zuwa yanzu adadin Falasdinawan da su ka yi shahada sun kai 100,000, wadanda su ka jikkata dubun dubata ne, mafi yawancinsu mata da kananan yara.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Falasdinawan da

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza

Gwamnatin mamayar Isra’ila ta yanke hukuncin kisa kan masu fama da cutar kansa da kuma waɗanda suke fama da matsalar koda na mutuwa a Gaza domin hana fitar da su wata kasa don neman magani

Cibiyar Kare Hakkin Dan Adam ta Gaza ta bayyana matukar damuwarta game da tabarbarewar lafiyar marasa lafiya da ke fama da cutar kansa da kuma cutar koda a Zirin Gaza. Wadannan cututtuka sun kara ta’azzara ne sakamakon hare-haren sojojin mamayar Isra’ila kan Gaza da kuma ci gaba da killace yankin bayan tsagaita bude wuta, gami da hana shigar dq magunguna da kayayyakin ayyukan likitanci masu muhimmanci cikin yankin. Cibiyar ta kuma yi nuni da tsauraran matakan fitar da marasa lafiya zuwa ƙasashen waje don neman magani.

A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Lahadi, Cibiyar ta tabbatar da cewa, wannan yanayin ba shi da wata shakka cewa Isra’ila na aiwatar da manufar kisan gilla a kan dubban marasa lafiya ta hanyar hana su ‘yancinsu na rayuwa da magani da gangan, da kuma canza wahalarsu zuwa wani nau’in hukunci na gama gari.

Cibiyar ta ambaci majiyoyin lafiya da ke tabbatar da cewa, akwai marasa lafiya 12,500 da ke fama da cutar kansa a Zirin Gaza, ciki har da ƙananan yara. Ta lura cewa mata sun kai kusan kashi 52% na dukkan masu cutar kansa a Gaza.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher November 2, 2025 IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya November 2, 2025 Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci November 2, 2025 Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza November 2, 2025 Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran November 2, 2025 Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari November 2, 2025 Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon November 2, 2025 Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya November 2, 2025 Shugaban AmurkaTrump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya November 2, 2025 Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar November 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Maganin Nankarwa (3)
  • Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza
  • Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan
  • Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar