Yadda jami’an tsaron Vatican suka hana Seyi zuwa wajen Tinubu da Fafaroma
Published: 19th, May 2025 GMT
Seyi Tinubu, ɗan Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, na cikin tawagar mahaifinsa da ta ziyarci fadar Vatican a ranar Lahadi domin halartar bikin rantsar da sabon Fafaroma, Leo XIV.
A yayin ziyarar, Shugaba Tinubu ya gana da Fafaroma har suka gaisa.
Yadda Boko Haram ta kashe manoma 90 a Borno cikin wata 5 NAJERIYA A YAU: Mece ce Makomar Dimokuraɗiyya Idan Aka Wajabta Kada Kuri’a?Amma abin da ya ja hankalin mutane shi ne lokacin da Seyi ya yi ƙoƙarin zuwa wajen mahaifinsa yayin da yake gaisawa da Fafaroma.
A wani bidiyo da ya karaɗe shafukan sada zumunta, an ga wani jami’in tsaro ya dakatar da Seyi cikin ladabi, yana nuna masa cewa bai kamata ya matsa kusa da wajen da suke ba.
Seyi na sanye da baƙar kwat kamar yadda mahaifinsa ya sanya, ya yi ƙoƙarin isa waje shugaban ƙasa, amma jami’in tsaron ya hana shi.
Wannan lamari ya jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta, inda mutane ke yabawa da yadda jami’an tsaron Vatican ke aiki da tsari da ƙa’ida.
Shugaba Tinubu ya kuma gana da tsohon abokin hamayyarsa a zaɓen 2023, Peter Obi, wanda ya kayar da shi a Jihar Legas a lokacin zaɓen.
Kalli bidiyon a nan ƙasa:
https://aminiya.ng/wp-content/uploads/2025/05/vid-20250519-wa0023.mp4উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Fadar Vatican Jami an Tsaro Sabon Fafaroma
এছাড়াও পড়ুন:
Juventus ta ɗauki tsohon kociyan Italiya, Luciano Spalleti
Kungiyar ƙwallon ƙafa ta Juventus ta naɗa Luciano Spalletti a matsayin sabon kociya bayan sallamar Igor Tudor da ta yi a farkon makon nan.
Juventus ta ƙulla yarjejeniya da tsohon kociyan na Inter Milan da Roma da Udinese da Zenit St Petersburg da kuma tawagar ƙasar Italiya, har zuwa ƙarshen wannan kakar, yayin da take fatan samu gurbin zuwa gasar Kofin Zakarun Turai ta Champions League ta baɗi.
Babu wani uzuri da za a yi wa sabbin hafsoshi kan matsalar tsaron Nijeriya — Tinubu Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – ZulumSpalletti, shi ne kociyan da ya jagoranci Napoli wajen lashe gasar Serie A a 2023, wadda ita ce karon farko cikin shekaru 33, inda a yanzu ake fatan zai ƙara daidaita Juventus da ke fama da rashin katabus da matsalolin kuɗi tun daga 2022.
Spalletti, wanda aka sani da ƙwarewa wajen gina ƙungiya mai ƙarfi, ya dawo horaswa bayan gazawar da ya yi a matsayin kociyan Italiya a gasar Euro 2024, da kuma shan kashi a hannun Norway yayin wasan farko na neman tikitin Gasar Kofin Duniya ta 2026.
Zuwa yanzu dai Juventus tana matsayi na bakwai a gasar Serie A da tazarar maki shida tsakaninta da Napoli da ke saman tebur, inda wasan farko da Spalletti mai shekaru 66 zai ja ragama shi ne da Cremonese.