Shi ma, Manajan Darakta na CDI, Roland Oroh, ya goyi bayan wannan ra’ayi na Dakta Anyebe Idoga, inda ya sanar da cewa; wannan aiki, zai kara karfafa karfin Nijeriya wajen fitar da kaya zuwa ketare.

“Mun ji dadi kan fara wannan yarjejeniya da mu, domin wannan zuba hannun jari, zai taimaka wa Nijeriya wajen kara habaka fitar da ingantaccen nama zuwa ketare”, in ji Oroh.

Kazalika, an bijiro da wannan hadaka ce, sakamakon yadda Saudiyya ta nuna sha’awarta, na son shigar da nama zuwa kasarta daga Nijeriya, wanda ya kai tan 176,000 a duk shekara, tare da kuma ciyawar dabbobi ta alfalfa hay da abincin dabbobi da ake sarrafawa da kuma Waken Soya.

A yanzu haka, CDI na ci gaba da tattaunawa da SALIC, musamman domin cimma bukatar samar da naman, wanda hakan zai kara habaka tattalin arzikin Nijeriya.

Wannan hadaka a tsakanin sauran sassan gwamnati daban-daban da CDI ke jagoranta, manufar ita ce; domin fitar da nama ketare kimanin tan 35,200 zuwa karshen 2025.

Bugu da kari, masu ruwa da tsaki a sassan kula da ayyukan kula da dabbobi da kwararrun likitocin dabbobi, duk an sanya su a cikin wannan aiki.

Aikin mayankar na Jurassic, ya kai na dala miliyan 10; wanda kuma ake gudanar da shi a hekta 50 da ke Nasarawa Egon, cikin Jihar Nasarawa.

Ana sa ran, za a kammala wannan aikin a watan Satumban 2025, inda wajen aikin zai dauki yawan Shanun da za a yanka da suka kimanin 1,000 da kuma Akuyoyin da za a yanka a kullum.

Kazalika, aikin zai taimaka wajen samar da ayyukan yi na kai tsaye, sama da 20,000 da kuma ayyukan yi wadanda ba na kai tsaye ba, kimanin 100,000 tare da kara bunka tattalin arzikin Nijeriya da kuma daga darajar Naira.
A shirin fitar da Naman, an kiyasta samar da kudin shiga da ya kai kimanin dala miliyan 273, wanda ya yi daidai da Naira biliyan 451 kafin zuwa 2025.

Wannan hadakar ta nuna irin kokarin da Nijeriya ke yi, duba da cewa; hakan zai kara wajen ganin ana amfana da fannin na aikin noman, tare kuma da kara bunkasa tattalin arzikin kasar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe

Dakarun Operation Haɗin Kai sun kama mut biyar da ake zargin suna taimaka wa ’yan ta’adda da kayan aiki.

Daga cikinsu har da wani ɗan ƙasar China da ya ce shi mai harkar ma’adinai ne.

Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya

An kama su ne a lokacin kai wani samame da aka gudanar daga 5 zuwa 7 ga watan Yuni a ƙananan hukumomin Kukawa da Ngala na Jihar Borno, da kuma Geidam a Jihar Yobe.

A lokacin wannan aiki, dakarun sun ƙwato wasu kayayyaki da suka haɗa da mota, babur, wayoyin salula, fasfo na ƙasar China, da kuma kuɗi Naira 10,000.

Shugaban sashen yaɗa labaran tsaro, Manjo Janar Edward Markus Kangye, ya bayyana hakan a wata ganawa da manema labarai a Abuja.

Ya ce sojojin sun kuma kai farmaki wasu yankuna bisa bayanan sirri da suka samu, ciki har da Gwoza da Abadam a Borno da kuma Nangere a Yobe, daga 6 zuwa 9 ga watan Yuni.

Ya ƙara da cewa daga 6 zuwa 11 ga watan Yuni, wasu maza da mata da yara da dama sun miƙa wuya ga dakarun Najeriya.

Kangye ya bayyana cewa rundunar ta kuma kai wasu hare-hare tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro a Ngala, Marte, Gwoza a Jjihar Borno da Bade da Gujba a Jihar Yobe daga 6 zuwa 10 ga watan Yuni.

A wannan lokaci, sun lalata sansanonin ’yan ta’adda, sun ƙwato makamai da alburusai.

Manjo Janar Kangye ya ce sojojin Najeriya za su ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin ’yan ƙasa tare da tabbatar da doka da oda.

“Mun ƙudiri aniyar kare martabar Najeriya da tabbatar da zaman lafiya a kowane yanki na ƙasar nan. Wannan aiki namu na ci gaba da yin tasiri,” in ji shi.

Ya buƙaci haɗin kan jama’a wajen taimaka wa sojoji su ci gaba da yaƙi da ’yan ta’adda.

Ya ce idan jama’a da hukumomi suka haɗa kai, Najeriya za ta samu zama lafiya da wadata.

“Zamu ci gaba da sanar da al’umma duk wani ci gaba da muka samu wajen yaƙar ta’addanci,” in ji Kangye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Shaida Gamsuwa Da Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
  • HKI Ta Rufe Filin Saukar Jiragen Sama Na Ben Gorion Tare Da Dauke Jiragenta  Zuwa Waje
  • Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
  • Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
  • Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
  • Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa
  • 12 ga Yuni: Najeriya na bikin ranar dimokuraɗiyya