Shi ma, Manajan Darakta na CDI, Roland Oroh, ya goyi bayan wannan ra’ayi na Dakta Anyebe Idoga, inda ya sanar da cewa; wannan aiki, zai kara karfafa karfin Nijeriya wajen fitar da kaya zuwa ketare.

“Mun ji dadi kan fara wannan yarjejeniya da mu, domin wannan zuba hannun jari, zai taimaka wa Nijeriya wajen kara habaka fitar da ingantaccen nama zuwa ketare”, in ji Oroh.

Kazalika, an bijiro da wannan hadaka ce, sakamakon yadda Saudiyya ta nuna sha’awarta, na son shigar da nama zuwa kasarta daga Nijeriya, wanda ya kai tan 176,000 a duk shekara, tare da kuma ciyawar dabbobi ta alfalfa hay da abincin dabbobi da ake sarrafawa da kuma Waken Soya.

A yanzu haka, CDI na ci gaba da tattaunawa da SALIC, musamman domin cimma bukatar samar da naman, wanda hakan zai kara habaka tattalin arzikin Nijeriya.

Wannan hadaka a tsakanin sauran sassan gwamnati daban-daban da CDI ke jagoranta, manufar ita ce; domin fitar da nama ketare kimanin tan 35,200 zuwa karshen 2025.

Bugu da kari, masu ruwa da tsaki a sassan kula da ayyukan kula da dabbobi da kwararrun likitocin dabbobi, duk an sanya su a cikin wannan aiki.

Aikin mayankar na Jurassic, ya kai na dala miliyan 10; wanda kuma ake gudanar da shi a hekta 50 da ke Nasarawa Egon, cikin Jihar Nasarawa.

Ana sa ran, za a kammala wannan aikin a watan Satumban 2025, inda wajen aikin zai dauki yawan Shanun da za a yanka da suka kimanin 1,000 da kuma Akuyoyin da za a yanka a kullum.

Kazalika, aikin zai taimaka wajen samar da ayyukan yi na kai tsaye, sama da 20,000 da kuma ayyukan yi wadanda ba na kai tsaye ba, kimanin 100,000 tare da kara bunka tattalin arzikin Nijeriya da kuma daga darajar Naira.
A shirin fitar da Naman, an kiyasta samar da kudin shiga da ya kai kimanin dala miliyan 273, wanda ya yi daidai da Naira biliyan 451 kafin zuwa 2025.

Wannan hadakar ta nuna irin kokarin da Nijeriya ke yi, duba da cewa; hakan zai kara wajen ganin ana amfana da fannin na aikin noman, tare kuma da kara bunkasa tattalin arzikin kasar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Rahotanni suna nuna cewa farashin shinkafa, ɗaya daga cikin nau’ukan abincin da ’yan Najeriya suka fi ci, ya karye a wasu sassan ƙasar.

Sauyin farashin ya sa ana tambayoyi — shin me ya haifar da wannan sauyi? Kuma me hakan ke iya haifarwa a rayuwar talaka?

NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki” DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin Arewa

A kan wannan sauyi da dalilansa ne shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta sha alwashin ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Nijar
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • Za A Yi Allurar Rigakafi Ga Dabbobi Sama Da Miliyan Daya A Babura
  • Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar
  • Gwamna Namadi Ya Nada Aisha Mujaddadi Sabuwar Shugabar Hukumar InvestJigawa
  • NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya
  • Mutanen da talauci ya yi wa katutu zai ƙaru a Nijeriya — Bankin Duniya
  • Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan  Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai
  • Aikin Hajji: Za A Fara Jigilar Alhazan Jihar Kwara A Ranar 12 Ga Watan Mayu
  • NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”