Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Harin Kan Cibiyar Makamashin Nukiliya Cin Amanar Diflomasiyya Ce
Published: 3rd, July 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Hare-haren da Amurka ta kai kan cibiyoyin nukiliyar Iran cin amanar diflomasiyya ce
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana harin da sojojin Amurka suka kai kan cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran na zaman lafiya a matsayin cin amanar diflomasiyya da kuma cewa wani mataki ne da ba a taba ganin irinsa ba ga tsarin doka da hakkin kasa da kasa da kuma tsarin hana yaduwar makaman nukiliya.
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi da Ronald Lamola, ministan hulda da kasa da kasa da hadin gwiwa na Jamhuriyar Afirka ta Kudu, sun tattauna batutuwan baya-bayan nan da ke faruwa a yankin Gabas ta Tsakiya bayan dakatar da hare-haren soji da yahudawan sahayoniyya da Amurka suka yi kan Iran a wata tattaunawa ta wayar tarho a ranar Laraba.
Araqchi ya bayyana jin dadinsa ga matsayin Afrika ta Kudu wajen yin Allah wadai da zaluncin sojin gwamnatin ‘yan sahayoniyya masu nuna wariyar al’umma suka dauka na kai wa kasar Iran hari, yana mai cewa: Hare-haren wuce gona da iri da gwamnatin ‘yan sahayoniyya ta dauka a kan Iran, sakamakon rashin hukunta ta ce da kuma gazawar kasashen duniya wajen mayar da martani kan laifukan da take aikatawa a Gaza da kuma hare-haren da take kai wa Lebanon da Siriya, kuma tabbas dukkanin masu goya mata baya suna da hannu wajen aikata laifukan da take aikatawa.
Ya yi nuni da cewa: Harin da sojojin yahudawan sahayoniyya suka kai wa Iran ya faru ne a cikin shawarwari da kuma goyon bayan gami da taimakon Amurka. Daga nan ne Amurka ta kaddamar da harin soji kan cibiyoyin nukiliyar Iran na zaman lafiya, tare da jaddada cewa matakin da Amurka ta dauka ya zama cin amanar diflomasiyya da kuma wani matakin da ba a taba ganin irinsa ba na rashin bin doka da oda, da take hakkin kasa da kasa, da kuma tsarin hana yaduwar makaman nukiliya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Uwargidar Gwamnan Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Noma Ga Mata Manoma
Hakazakika, an zakulo Mata dalibai daga wasu zababbun makarantun sakandare a jihar da kuma wasu daidaikun Mata a kananan hukumomi 23 na jihar Kaduna.
Da yake kaddamar da Rabon Kayan, Shugaban Ma’aikatar Fadar Gwamnatin jihar Kaduna Malam Liman Sani Kila, ya bayyana gamsuwarsa dangane da kokarin uwargidar shugaban kasa Remi Tinubu na tallafawa Mata Da Matasa a fadin kasar baki daya.
Hakazakika, ya jinjinawa Uwargidar Gwamnan jihar Kaduna Hajiya Hafsat Uba Sani bisa bubbasar da takeyi wajen tallafawa Mata Da dalibai Mata Da masa abin a Yaba ne Yana Mai bayar da tabbacin cewa gwamnatin jihar Kaduna Ta himmatu wajen ciyar da aikin Noma a jihar Kaduna.
Kila ya kuma jinjinawa Hajiya Hafsat Uba wajen jajircewata wajen Tabbatar da cewa duk wani tallafi na uwargidar shugaban kasa take aikowa Kaduna Yana kaiwa ga mata.
Yace Gwamnatin Uba Sani ta ware Kashi 70 cikin dari na kasafin kudin jihar wajen harkar bunkasa aikin Noma Wanda a tarihin jihar Kaduna ba’a taba samun Gwamnatin da tayi irin haka ba.
Ya bukaci wadanda suka amfana da tallafin da suyi amfani da Kayan wajen dogoro da kansu maimakon su sayar dasu.
Shugaban yace Babu shakka wannan Shirin zai taimakawa ci gaban rkyuwar Mata. Yace Rabon Kayan na wannan karon ba Mata zalla kadai bane Zasu amfana yarda dalibai maza da mata a fadin jihar Kaduna baki daya.
Da take nata jawabin uwargidar Gwamnan jihar Kaduna Hajiya Hafsat Uba Sani ta bayyana cewa uwargidar shugaban kasa Remi Tinubu tana da burin tallafawa ci rkyuwar Mata da Yara domin farfado da tattalin arzikin jihar Kaduna Ta bangarori da dama.
Tace wannan Shirin zai tamaka wajen bunkasa ci gaban rkyuwar Mata da Yara a fadin jihar Kaduna tana Mai cewa ya zama wajibi daukacin matan jihar Kaduna su nuna goyon bayansu da uwargidar shugaban kasa a kokarin da take da inganta rayuwarsa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp