Aminiya:
2025-09-18@05:40:29 GMT

Rasha ta amince da gwamnatin Taliban a Afghanistan

Published: 4th, July 2025 GMT

Rasha ta zama ƙasa ta farko da a hukumance ta amince da gwamnatin ƙungiyar Taliban da ke mulkin ƙasar Afghanistan.

Wannan na zuwa ne bayan Rashar ta karɓi takardun shaidar kama aiki na sabon jakadan Afghanistan, wanda hakan ya sa ta zama ƙasa ta farko da ta amince da gwamnatin Taliban a ƙasar.

Ambaliya da iska sun rushe gidaje 171 a watanni biyu a Gombe – SEMA Majalisar Mali ta ƙara wa Goita wa’adin mulkin shekara biyar

“Mun yi imani cewa wannan matakin na amincewa a hukumance da gwamnatin Daular Musulunci ta Afghanistan zai ba da damar haɓaka haɗin gwiwa mai amfani tsakanin ƙasashenmu a fannoni daban-daban,” in ji Ma’aikatar Harkokin Wajen Rasha a cikin wata sanarwa a ranar Alhamis.

Ma’aikatar Harkokin Wajen Afghanistan ta tabbatar da lamarin, tana mai cewa jakadan Rasha Dmitry Zhirnov ya gana da Ministan Harkokin Wajen Taliban Amir Khan Muttaqi, inda ya isar da wannan matakin na gwamnatin Rasha da ke nuna “muhimmancin wannan mataki”.

Zhirnov ya bayyana wannan a matsayin “mataki mai tarihi wajen ƙarfafa dangantaka tsakanin ƙasashen biyu.”

Ma’aikatar Harkokin Wajen Afghanistan ta ce: “Da wannan mataki, dangantakar ƙasashen biyu za ta ƙara faɗaɗa.”

Muttaqi ya nuna fatan cewa wannan zai haifar da ƙarin haɗin gwiwa da kuma ƙarfafa dangantaka tsakanin Afghanistan da Rasha.

Zhirnov ya shaida wa tashar talabijin ta gwamnati Rossiya-1 Shugaba Vladimir Putin ne ya ɗauki wannan matakin bisa shawarar Ministan Harkokin Wajen Rasha Sergey Lavrov. “Wannan yana nuna burin gaskiya na Rasha na kafa haɗin gwiwa mai ƙarfi da Afghanistan,” in ji shi.

Zuwa yanzu dai babu wata ƙasa mamba a Majalisar Ɗinkin Duniya da ta amince da gwamnatin riƙon ƙwarya ta Taliban tun dawowarta kan mulki a watan Agustan 2021.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dmitry Zhirnov Rasha ta amince da gwamnatin Harkokin Wajen

এছাড়াও পড়ুন:

Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono

Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Ondo ta tabbatar da kama wata mata mai suna Iluyemi Bosede bisa zargin kashe yayarta, Tewogboye Omowumi, a Akure, babban birnin jihar.

A cewar sanarwar da Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, Olayinka Ayanlade, ya fitar a ranar Talata, ya ce lamarin ya faru ne a ranar shida ga Satumba, 2025, bayan wata sa’insa da ta kaure tsakanin matar da marigayiyar kan Naira 800.

Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya

Jami’in ya bayyana cewa Bosede ta ture ’yar uwarta har ta faɗi ƙasa, lamarin da ya haifar da mutuwarta.

Ya ce, “Binciken farko ya nuna cewa Iluyemi Bosede ta je wurin yayar tata, Tewogboye Omowumi mai shekaru 35, domin karbar bashinta na N800 na kudin tumatir da barkono. Sai dai tankiyar da ta fara a matsayin ƙaramin sabani ta rikide zuwa tashin hankali, inda ake zargin Bosede ta riƙe kayan marigayiyar har ta faɗi ƙasa.”

“Abin takaici, duk da an garzaya da marigayiyar asibiti don samun kulawar gaggawa, likitoci sun tabbatar da mutuwarta tun kafin a fara ba ta taimako. Wannan lamari ya nuna yadda ƙaramin sabani zai iya rikidewa zuwa mummunar husuma idan ba a magance shi cikin lumana ba.”

Bayan faruwar lamarin, rundunar ta ce ta kama wadda ake zargi kuma tana tsare da ita a halin yanzu, yayin da bincike ke ci gaba.

Rundunar ta kuma tabbatar da cewa za a gurfanar da wadda ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike, domin ta girbi abin da ta shuka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
  • Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki Guda 5 A Wajen Taron Kolin kere-kere .
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne
  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha
  • Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila