Dantsoho wanda ya samu wakilicin Babban Manajan a Hukumar ta NPA Femi Oyewole, ya bayyana cewa, Shugaban Hukumar ta NPA, Hukumar ta mayar da hankali wajen ganin cewa, ana kare kimar Tekunan kasar.

“Hadurran zuba baraguzan kusan a kurkusa suke, wanda kuma, suke ci gaba da karuwa, wanda hakan ya nuna cewa, akwai matukar bukatar a dakile yadda ake duba baragunzan, a cikin Tekunan, baki daya,” Inji Dantsoho.

Ya ci gaba da cewa, Hukumar ta NPA bata yi kasa a guiwa ba, wajen daukar matakan da suka kamata, domin magance wannan matsalar.

“Duba da cewa, muna gudanar da ayyukan NPA yadda ya kamata da kuma bin ka;idojin da ke tafiyar da Hukumar, musamman wajen bai wa kayan Hukumar da ke a daukacin Tashoshin Jiragen Ruwan kasar kariya, kamar yadda suka kasance a matakin na kasa da kasa na dakile gurbatar da Jiragen Ruwa ke janyo wa, musamman duba da kundin tsari na (MARPOL 73/78), za mu ci gaba da lalubo da mafita kan zubar baraguzai a Tekunan kasar,” A cewarsa.

Shugaban ya kara da cewa, kayan aikin NPA na bukatar a samar masu kariyar da kamata, musamman ta hanyar bai wa Jiragen ruwa da ke tsayawa a Tashoshin kariyar da ta kamata.

Dantsoho ya bayyana cewa, NPA akai-akai ta kan tabbatar da ana ci gaba da tsaftace Tekunan daga kalubalen baraguzan da duk wata bola, da ake zubawa a cikin Tekunan kasar a daukacin Tashohin Jiragen Ruwan kasar.

Shugaban ya yi nuni da cewa, ta hanyar kwashe baraguzan da sauran bolar robobin da ake zubawar a cikin Tekunan ne, kadai, za a iya kare rayuwar dabbobin da ke rayuwa a cikin Tekunan tare da kuma samar wa Jiragen Ruwan saukin yin zirga-zirga a kan Tekunan kasar.

Shi kuwa a na sa jawabin a wajen taron Babab Sakataren Cibiyar kungiyar masu fito kaya a Jiragen Ruwa na kasa Dakta Pius Akutah, yabawa kungiyar ta wakilan masu wallafa rahotanin a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar kan zabo wannan maudu’in domin a tattauna a kansa

Ya kuma jaddda bukatar da a tabbatar da ana tsaftace hanyoyin Ruwa da ke a Tekunan kasar, musamman domin Jiragen Ruwan da ke hawansu, su samu saukin tafiya akai ba tare da wata tangarda ba.

Akutah, wanda Mataimakin Darakata a sashen sanya ido na cibiyar ya wakilce shi a wajen taron Adeshina Sarumi, ya yi nuni da cewa, samun baraguzan a hanyoyin Ruwan na haifar da cikas ga zirga-zirgar Jiragen Ruwan.

Shi kuwa Manajin Darakta na Hukumar NIWA Bolaji Oyebamiji, ya bukaci masu ruwa da tsaki a fannin da su yi dukkan mai yuwa, domin a dakile wannan kalubalen da ake fuskanta, musaman ta hanyar wyar da kan alummar da ke da zama a daura da Tekunan kasar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: a Jiragen Ruwa Jiragen Ruwan Tekunan kasar

এছাড়াও পড়ুন:

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

A ƙalla fasinjoji 17 ne suka rasa rayukansu bayan wata motar haya ta faɗa cikin wata gada da ta ruguje a kan titin Gwalli da ke ƙaramar hukumar Gummi, jihar Zamfara.

A cewar hukumar kiyaye haɗura ta ƙasa (FRSC) reshen Zamfara, hatsarin ya faru ne a daren Lahadi lokacin da motar ɗauke da kaya da fasinjoji ta faɗa cikin gadar da ta ruguje. Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, SRC Isah Aliyu, ya tabbatar da lamarin a wata sanarwa da ya fitar.

Kwamandan FRSC na jihar, CC Aliyu Magaji, wanda ya ziyarci wurin hatsarin, ya bayyana matuƙar baƙin cikinsa da asarar rayukan, inda mafi yawansu mata ne. Ya ce hatsarin ya biyo bayan nauyin da aka ɗora wa motar fiye da ƙima da kuma tafiya da daddare.

Hukumar ta gode wa mazauna yankin da suka gaggauta taimakawa wajen ceto wasu daga cikin waɗanda hatsarin ya rutsa da su. Kwamanda Aliyu ya yi ta’aziyya ga gwamnatin Zamfara da al’ummar Gummi, tare da yin kira ga direbobi su rika bin ƙa’idojin hanya da kuma guje wa tuƙa mota da dare domin kare rayuka.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaidai Dake Kasar Yamen
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara