Aminiya:
2025-05-19@19:56:50 GMT

Mawaƙan APC sun zargi gwamnati da watsi da su a Jigawa

Published: 19th, May 2025 GMT

Wasu mawaƙan jam’iyyar APC da ke Jihar Jigawa, sun bayyana ɓacin ransu kan yadda gwamnatin jihar ta yi watsi da su, duk da irin gudunmawar da suka bayar wajen samun nasarar jam’iyyar a zaɓen 2023.

Mawaƙan wajen su 35, sun gudanar da wani taro, inda suka bayyana damuwarsu da kuma sanar da cewa sun janye daga duk wata hulɗa da gwamnatin jihar, har sai an ba su kulawar da ta dace.

Hajji: Gwamnan Gombe ya yi bankwana da maniyyata 966, ya bai wa kowa kyautar Riyal 200 NAJERIYA A YAU: Mece ce Makomar Dimokuraɗiyya Idan Aka Wajabta Kada Kuri’a?

Shugaban mawaƙan jihar, Lawan Gujungu Mai Babban Gandu ne, ya jagoranci taron, inda ya shaida wa manema labarai cewa tun bayan da sabon gwamnan ya hau mulki sama shekara biyu, har yanzu ba su sharɓi romon dimokuraɗiyya ba.

Ya ce mawaƙan sun yi haƙuri na tsawon lokaci suna sa ran za a saka musu, amma abin ya gagara.

A cewarsa: “Mun shiga mawuyacin hali. Muna cikin APC tun asali, mun yi wa jam’iyya hidima sosai a lokacin yaƙin neman zaɓe, mun ƙirƙiri waƙoƙi da dama don tallata manufofin jam’iyyar da kwatanta cancantar ’yan takararta.

“Amma yanzu da muka ci zaɓe kuma muka kafa gwamnati, an watsar da mu tamkar ba mu da wata ƙima.”

Lawan, ya ƙara da cewa daga yanzu mawaƙan za su nisanci duk wani taro ko aikin da ya shafi gwamnati, har sai an saurare su tare da mutunta su da irin gudunmawar da suka bayar.

Wannan bore ya fito fili ne a daidai lokacin da ake buƙatar jituwa da haɗin kai tsakanin masu ruwa da tsaki a cikin jam’iyyar da kuma gwamnatin jihar domin ci gaban al’umma.

Wasu daga cikin mawaƙan da suka halarci taron sun bayyana cewa suna fatan gwamnan zai ji ƙorafinsu kuma ya ɗauki matakin da ya dace, domin ci gaba da gina jam’iyya da gwamnatin da kowa ke alfahari da ita.

Tuni dai wannan batu ya jawo ce-ce-ku-ce a cikin jam’iyyar APC a Jihar Jigawa, inda wasu ke ganin cewa ya kamata gwamnati ta sake duba rawar da waɗanda suka ba da gudunmawa kafin kafa gwamnati, domin gudun fuskantar tawaye.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnati Jigawa Ƙorafu Mawaƙa taro

এছাড়াও পড়ুন:

Kwamishiniya ta nemi a hukunta wanda ake zargi da yi wa ’yar matarsa fyaɗe a Gombe

Kwamishiniyar Harkokin Mata da Ci gaban Jama’a ta Jihar Gombe, Asma’u Muhammad Iganus, ta ce gwamnati za ta tabbatar da an yi wa ’yar shekara biyu, Maryam Buba da ake zargin mijin mahaifiyarta, Muhammad Magaji mai shekara 47, da yi mata fyaɗe.

Kwamishiniyar tare da tawagarta sun kai ziyara gidan iyalan yarinyar da ke unguwar Jauro Innayo a Gombe, inda ta tausaya mata tare da ba su kayan tallafi kamar su pampers, sabulai da kuma kuɗi.

’Yan bindiga sun kashe mutum 3, sun sace 26 a ƙauyukan Zamfara Mawaƙan APC sun zargi gwamnatin Jigawa da yin watsi da su

Asma’u ta sha alwashin cewa za a bi duk matakan shari’a domin ganin wanda ake zargi ya fuskanci hukunci.

Ta ce gwamnati na mara wa ɓangaren shari’a baya don ganin an samu adalci.

Ta jaddada ya kamata a yi wa wanda ake zargi hukuncin ɗaurin rai da rai matuƙar an same sa da laifi, domin hakan zai zama izina ga masu irin wannan ɗabi’a.

Mahaifiyar yarinyar, Hauwa’u Usman, ta gode wa Kwamishiniyar bisa goyon bayan da ta bayar da kuma addu’a a gare ta.

Ta kuma buƙaci gwamnati ta hukunta mijinta da tsauraran hukunci.

Daga bisani Kwamishiniyar, ta nufi hedikwatar ‘yan sandan Jihar Gombe don ganawa da Kwamishinan ‘yan sanda Bello Yahaya.

Sai dai ba ta same shi ba saboda yana bakin aiki.

Duk da haka, ta bar saƙo masa na gudanar da bincike tare da gurfanar da wanda ake zargi a kotu.

Muhammad Magaji, wanda ake zargi da laifin, yana hannun ’yan sanda kuma suna kan bincike.

Rundunar ’yan sandan ta tabbatar da cewa za a gurfanar da shi a kotu da zarar ta kammala bincike.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwamishina ta nemi a hukunta wanda ake zargi da yi wa ’yar matarsa fyaɗe a Gombe
  • Kwamishiniya ta nemi a hukunta wanda ake zargi da yi wa ’yar matarsa fyaɗe a Gombe
  • Mawaƙan APC sun zargi gwamnatin Jigawa da yin watsi da su
  • APC Ta Zargi Gwamnan Zamfara Da Shirga Karya Tare Da Kiran Ya Nemi Afuwar Zamfarawa
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 15 Sun Raunata 3 A Jihar Kebbi
  • ’Yan sanda sun ceto tsohuwa mai shekara 80 a hannun ’yan bindiga a Jigawa
  • Zargin Kin Amincewar Kwankwaso Zuwa APC: Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Mai Taimaka Ma Ta
  • Shin PDP za ta iya ɗinke ɓarakarta nan da zaɓen 2027?
  • Tawagar NAHCON Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido Jihar Jigawa