Filato: Mahara sun cire hannun matashi a kan hanyar komawa gida daga jana’iza
Published: 4th, July 2025 GMT
Wasu ’yan bindiga sun kai hari kan masu dawowa daga binne gawa a kauyen Rim na jihar Filato, inda suka datse wa daya daga cikin matasan da ke wurin hannu daya.
Bayanai sun nuna cewa mutanen na kan hanyarsu ce ta dawowa daga bikin binne wani mutum ne a kauyen Bachit da ke da makwabtaka da su inda suka yi arba da maharan wadanda suka tare su suka bude musu wuta, sannan suka datse wa daya daga cikin mutanen hannu daya.
Wani Hadimin Gwamnan Filato, Caleb Mutfwang, mai suna Timothy Dantong, wanda yake cikin mutanen da suke dawowa daga binnewar da shi ma ya tsallake rijiya da baya, ya tabbatar wa majiyarmu da kai harin a ranar Alhamis.
Ya ce daga bisani an turo wata tankar yaki da jami’an tsaro wadanda suka isa yankin suka ceto su.
Timothy ya ce, “Jiya na je jana’iza a kauyena na Bachit. A kan hanyarmu ta dawowa sai muka tarar an kai hari kauyen Rim, inda aka shawarce mu da mu dakata, saboda dole sai mun wuce ta nan kafin mu koma gida. Haka muka zauna sai da muka shafe awa biya muna zaman jira.
“Wasu daga cikinmu da suka gaza jira suka tafi, inda aka bude musu wuta sannan aka cire wa daya daga cikinsu hannunsa gaba daya.
“Mu ma dole sai daga baya aka turo mana tankar yaki ta zo ta ceto mu daga zaman jiran tsammani, amma da tuni lamarin ya ritsa da ni. Ban son me wadannan maharan suke so daga gare mu ba, sun matsa wa mutanenmu,” in ji Timothy.
Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Filato, Alabo Alfred bai dauki kiran da aka mas aba don jin ta bakin rundunar kan harin, har zuwa lokacin hada wannan rahoton.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga mahara
এছাড়াও পড়ুন:
HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa
Rahotanni sun bayyana cewa Isra’ila ta kashe wasu falasdinawa guda 5 yankin gaza a ci gaba da keta yarjejeniyar dakatar da bude wuta da suka cimma tsakaninta da kungiyar Hamas a farkon watan oktoba,
A yau juma’a kafar yada labarai ta falasdinu ta bayyana cewa sojojin Isra’ila sun harbe wani bafalasdine a yankin jabaliya dake arewacin yankin Gaza, haka zalika wani bafalasdine mai suna Mahmud suleman al- wadiya sojojin isaraila sun kashe shi a gabashin shuja’iyya dake makwabtaka da gabashin gaza, gari mafi girma a gaza kuma an jikkata wani dan uwansa,
Har ila yau hamdi al-barim da mohamma salem qadi sun ji mummunan rauni sakamakon harin da sojojin Isra’ila suka kai musu a khan yunus dake yammacin gaza a yan kwanakin nan,
Tun daga lokacin da Isra’ila ta kaddamar da hare-hare a yankin Gaza zuwa yanzu a shekara ta 2023 sojojin Isra’ila na ci gaba da kai hare – hare a yankuna daban – daban inda akalla sun kashe mutane 1062 tare da jikkata wasu dubbai fiye da 20,000 kuma da suka hada da yara kana 1600 an cafkesu ana tsare da su .
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa October 31, 2025 Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta October 31, 2025 M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi October 31, 2025 Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda October 31, 2025 Araqchi: Gwajin Makaman Nukiliya Na Amurka Babbar Barazana Ce Ga Duniya October 31, 2025 Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan October 31, 2025 Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar October 31, 2025 Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa October 31, 2025 Iran ta yi fatali da kalamman IAEA Kan Shirin Nukiliyarta October 30, 2025 Trump Ya Umarci Ma’aikatar Yakin Amurka Ta koma gwajin makaman nukiliya October 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci