Sanarwar ta ƙara da cewa, a yayin taron an sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna tsakanin gwamnatin jihar Zamfara da Hukumar Samar da Wutar Lantarki ta Yankunan Karkara, sannan aka tattauna da masu ruwa da tsaki, tambayoyi da amsoshi, ra’ayoyi, da kuma alƙawura.

 

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya ce ya gaji matalauciyar gwamnatin a bangaten lantarki.

 

Ya ci gaba da cewa, “An katse ƙananan hukumomi da yawa daga babban lantarkin ƙasa. An sace wayoyin lantarki da dama, wasu kuma sun lalace, wasu muhimman ababen more rayuwa sun durƙushe a cikin shekaru saboda watsi da su, sannan masana’antu da kasuwancinmu sun gurgunta saboda rashin ingantaccen wutar lantarki.

 

“Duk da haka, mun zaɓi kada mu shiga wasan zargi, a maimakon haka, mun mayar da martani ga ƙalubalen da muka gamu da su tare da hangen nesa mai muhimmanci, ƙuduri aiwatar da aiki da kuma yanke hukuncin cikin gaggawa.

 

“Tun daga wannan lokacin ne gwamnatinmu ta fara aikin sake rubuta wannan labari ta hanyar sanya hanyoyin samar da wutar lantarki a cikin dabarun ci gabanmu, mun ƙaddamar da ɗaya daga cikin shirye-shiryen samar da taransfoma na ƙasar nan, inda muka tura taransifoma sama da guda 150 a cikin birane da ƙauyuka.

 

“A tare da haɗin gwiwar Kamfanin Samar da Wutar Lantarki ta Kaduna mun maido da wutar lantarki a ƙananan hukumomi shida, kuma mun sake haxe wasu guda bakwai, waɗanda wasu daga cikinsu ba su da wutar lantarki sama da shekaru goma, wannan ƙoƙari na cikin wani shiri na zaburar da masana’antu, da kuma buɗe kasuwanni masu zaman kansu.

 

Gwamna Lawal ya ce, Zamfara tana ba da damammaki masu kyau don saka hannun jari a bangaren lantarki. “An albarkace mu da hasken rana mai tsananin ƙarfi a duk shekara, wanda ya sa mu zama wuri na farko da gonakin hasken rana za su samu habaka cikin sauri.

 

“Idan aka duba za a babban damar da madatsar ruwa ta Bakalori ke da shi, kadara ce ta samar da wutar lantarki da ba a yi amfani da ita ba, tare da yanki sama da hekta 30,000 na ban ruwa. Wannan haɗin gwiwa na hasken rana yana ba da damar ƙaddamar da hanyoyin samar da lantarki wanda zai iya ci gaba da ƙarfafa birane da karkara.

 

“Bangaren nomanmu wani muhimmin batu ne, a kullum jihar Zamfara tana cikin jerin manyan jihohin da ke girbin gero, dawa, waken soya, da gyaɗa a Nijeriya, muna sake fasalin wannan fanni ta hanyar ingantattun kayan aiki, injininan noma na zamani, da gyaran ban ruwa.

 

“Babban misalin sabunta kayan aikin mu shi ne filin jirgin sama na Gusau da filin jirageb ɗaukar kaya da ke kusa da shi, wanda aka tsara shi a matsayin ƙofa ga fasinjoji, kasuwanci da saka hannun jari.

 

“Don cimma burinmu na noma, muna nufin wannan ginin ya zama filin jirgin sama na farko a Nujeriya wanda zai samu wutar lantarki aƙalla kashi 50 cikin 100, kuma zai bai wa RESCO damar jagorantar sufurin jiragen sama mai ɗorewa.”

 

Tun da farko, Manajan Daraktan REA, Abba Abubakar Aliyu, ya tabbatar wa Gwamna Lawal ƙudirin hukumar na samar da kayayyakin wutar lantarki a jihar Zamfara.

 

“A karon farko a tarihin Nijeriya an yi taswirar ƙasar baki ɗaya, kuma hakan ya nuna adadin mutanen da ba su da wutar lantarki da kuma wurin da suke da shi, yanayin al’ummarsu da kuma buƙatar wutar lantarki, hakan ya taimaka wa RESCO da kuɗi, kuma gwamnatin jihar ta samu dabarar da za a bi don ganin cewa waɗannan mutanen sun samu wutar lantarki.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: samar da wutar lantarki wutar lantarki a Gwamna Lawal

এছাড়াও পড়ুন:

Baltasar: Mutumin da ya fitar da bidiyon lalatarsa da mata sama da 400 ya gurfana a kotu

Baltasar Engonga Ebang, mutumin nan dan kasar Equatorial Guinea da a bara ya saki bidiyon lalatarsa da mata sama da 400 na fuskantar shari’a a kotu kan badakalar kudade.

Baltasar, wanda tsohon Shugaban Hukumar Yaki da Rashawa ta kasar Equatorial Guinea ne dai an gurfanar da shi a gaban kotu ne bisa zargin karkatar da kudade a karkashin Ma’aikatar Kudin kasar.

Masu shigar da kara na neman a yanke masa hukuncin daurin shekara 18 a kurkuru sannan a umarce shi ya dawo da wasu kudaden masu yawa.

’Yan Najeriya sun fara begen Buhari saboda azabar TIinubu – Amaechi Ɗan wasan Liverpool, Diogo Jota, ya mutu a hatsarin mota

Ana dai zarginsa ne da almundahana, azurta kai da kuma rub-da-ciki a kan dukiyar al’umma lokacin da yake rike da mukamin hukumar.

Lauyoyi masu shigar da kara na zargin Baltasar da yin babakere a kan kudi har sama da CFA biliyan daya, kwatankwacin sama da Naira biliyan biyu da rabi.

Bugu da kari, lauyoyin na kuma son a yanke masa hukuncin shekara takwas kan laifin almundahana, shekara hudu da wata biyar kan laifin azurta kai, sai kuma shekara shida kan laifin cin amanar ofishinsa.

Lauyoyin sun kuma bukaci kotun ta ci Baltasar tarar CFA miliyan 910 sannan a haramta masa rike kowanne irin ofishin gwamanti na tsawon lokacin da zai shafe a dauren.

To sai dai lauyoyin wanda ake karar sun yi fatali da dukkan laifukan da ake zargin wanda suke karewa da aikatawa da ma sauran wadanda ake zargin, inda suka ce bas u da tushe.

A watan Disambar bara ne dai bidiyoyin Baltasar na lalata da mata sama da 400 suka cika shafukan sada zumunta. Daga cikin matan da aka gan shi yana lalata da su har da matan ministotin kasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwamandan Sojojin Iran Ya Ziyarci Gidan Babban Jami’in Sojin Kasar Da Ya Yii Shahada Lokacin Yakin Baya-Bayan Nan
  • Baltasar: Mutumin da ya fitar da bidiyon lalatarsa da mata sama da 400 ya gurfana a kotu
  • Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma
  • Iraki Ta Kai Karar HKI Kan Amfani Da Sararin Samaniyar Kasar Don Kaiwa Iran Hare hare
  • Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang
  • Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar
  • Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba
  • Uwargidar Gwamnan Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Noma Ga Mata Manoma
  • Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara