Zargi: ’Yan sanda sun musanta sace tsohon Kwamishinan El-Rufai
Published: 15th, March 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, ta ƙaryata zargin da Tsohon Gwamna Nasir El-Rufai ya yi cewa jami’an tsaro sun sace tsohon Kwamishinansa, Jafaru Sani.
El-Rufai ya yi wannan iƙirari ne a shafinsa na sada zumunta cewa an ɗauke tsohon Kwamishinan kamar fursuna ba tare da bin ƙa’idojin doka ba.
Direba ya murƙushe yarinya ta mutu a artabu da jami’an tsaro a Edo Cutar sanƙarau ta kashe sama da mutum 50 a Sakkwato da KebbiYa yi zargin cewa wata “ƙungiyar masu garkuwa da mutane” da ke da alaƙa da Gwamna Uba Sani ce ke da alhakin ɗauke tsohon Kwamishinan.
Da yake mayar da martani, kakakin ’yan sandan jihar, DSP Mansir Hassan, ya bayyana zargin a matsayin ƙarya.
“Babu wata ƙungiyar masu garkuwa da mutane a cikin Rundunar ’Yan Sandan Najeriya.
“Mu hukuma ce da ke aiki bisa kundin tsarin mulki don tabbatar da doka da oda,” in ji shi.
Ya buƙaci ’yan siyasa su guji yaɗa labaran da ba su da tushe.
“Yi wa jami’an tsaro ƙarya na iya haifar da ruɗani da kuma rage martabarsu. Idan mutum yana da ƙorafi, ya bi hanyar shari’a maimakon yaɗa kalaman da za su tayar da fitina,” a cewarsa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Jafaru Sani Tsohon Kwamishina zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Hukuncin Kisa Kan Maryam Sanda
Alkalin ya kuma bayyana cewa ba daidai ba ne bangaren zartarwa ya yi rangwame ga hukuncin kisa yayin da har yanzu ana da karar daukaka kara a gaban kotu. Don haka, kotun ta kori daukaka karar Maryam Sanda gaba ɗaya tare da tabbatar da hukuncin kisa da kotunan ƙasa suka yanke mata.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA