Zargi: ’Yan sanda sun musanta sace tsohon Kwamishinan El-Rufai
Published: 15th, March 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, ta ƙaryata zargin da Tsohon Gwamna Nasir El-Rufai ya yi cewa jami’an tsaro sun sace tsohon Kwamishinansa, Jafaru Sani.
El-Rufai ya yi wannan iƙirari ne a shafinsa na sada zumunta cewa an ɗauke tsohon Kwamishinan kamar fursuna ba tare da bin ƙa’idojin doka ba.
Direba ya murƙushe yarinya ta mutu a artabu da jami’an tsaro a Edo Cutar sanƙarau ta kashe sama da mutum 50 a Sakkwato da KebbiYa yi zargin cewa wata “ƙungiyar masu garkuwa da mutane” da ke da alaƙa da Gwamna Uba Sani ce ke da alhakin ɗauke tsohon Kwamishinan.
Da yake mayar da martani, kakakin ’yan sandan jihar, DSP Mansir Hassan, ya bayyana zargin a matsayin ƙarya.
“Babu wata ƙungiyar masu garkuwa da mutane a cikin Rundunar ’Yan Sandan Najeriya.
“Mu hukuma ce da ke aiki bisa kundin tsarin mulki don tabbatar da doka da oda,” in ji shi.
Ya buƙaci ’yan siyasa su guji yaɗa labaran da ba su da tushe.
“Yi wa jami’an tsaro ƙarya na iya haifar da ruɗani da kuma rage martabarsu. Idan mutum yana da ƙorafi, ya bi hanyar shari’a maimakon yaɗa kalaman da za su tayar da fitina,” a cewarsa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Jafaru Sani Tsohon Kwamishina zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Jirgin fadar shugaban ƙasa ya ƙi sayuwa wata 5 bayan saka shi a kasuwa
Jirgin Fadar Shugaban Kasa da Gwamnatin Najeriya ta saka a kasuwa da nufin sayarwa ya kasa samun mai saye kusan watanni biyar bayan ɗora shi a dandalin sayar da jiragen sama na duniya.
A sakamakon haka, tuni ma kamfanin dillancin da ke kula da sayar da jirgin samfurin Boeing 737-700 Business Jet ya janye jerin sayar da shi daga shafinsa.
’Yan Najeriya suna da ƙwarin guiwa a kaina, ba zan ba su kunya ba — Ministan Tsaro ’Yan sanda sun kama mutum 28 kan zargin lalata mata da yara a YobeJaridar Punch ta rawaito cewa jirgin da a baya aka saka a shafin kamfanin, yanzu an cire shi daga kai.
A cikin wata amsa ga sakon imel, Laurie Barringer wanda shi ne Manajan Binciken Kasuwa na JetHQ, ya tabbatar da cewa kamfanin ya cire jirgin daga jerin sayarwa, inda ya ce a nemi karin bayani daga Gwamnatin Najeriya.
“Mun gode da sakonku. Ba mu da jerin Boeing yanzu a shafinmu. Sai dai ku tuntubi Gwamnatin Najeriya don samun bayani kan abin da ya faru da jirgin. Na gode da lokacinku — Laurie Barringer, Manajan Binciken Kasuwanci, JetHQ,” in ji sakon.
Hadimin Mai Ba da Shawara kan Tsaron Ƙasa, Ismail Garba, ya yi alƙawarin bayar da amsa amma bai yi hakan ba har bayan kwanaki da dama.
Mataimakin Manajan Binciken Kasuwa na JetHQ, Marinell Nuevo, ya tabbatar da cewa jirgin “yana nan a kasuwa” amma ya tura karin tambayoyi zuwa Barringer.
Daga baya Barringer ya bayyana cewa kamfanin ba zai bayyana wasu bayanai fiye da kasancewar jirgin a kasuwa ba, yana mai cewa irin wannan bayani na sirri ne.
“Ba ma bayar da irin wadannan bayanan ga kowa sai ga mamallakin jirgin kai tsaye. Ana ɗaukar wannan bayani a matsayin sirri. Ina fatan za ku fahimta. Abin kawai da za mu iya bayarwa shi ne cewa jirgin yana nan a kasuwa,” in ji Barringer.
Kafin a cire shi daga jerin sayarwa, bayanai sun nuna cewa an yi wa jirgin gyare-gyare a watan Yuli 2024, ciki har da gyaran kujerun ajin farko, sauya kafet na cikin jirgi da sauran kananan gyare-gyare.
A cewar aircraftcostcalculator.com, jirgin Boeing 737 BBJ da aka taɓa amfani da shi darajarsa a kasuwa ta kai kusan $56m, kwatankwacin Naira sama da Naira biliyan 82.
An sayi jirgin a shekarar 2005 a kan $43m a zamanin tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo, kuma ya kasance wani jerin jiragen Fadar Shugaban Ƙasa.
A watan Yuli 2025, gwamnatin Tinubu ta sanar da shirin sayar da jirgin a matsayin wani ɓangare na dabarar rage kashe kuɗi da daidaita yawan jiragen, a yayin da jama’a ke ƙara sa ido kan yadda gwamnati ke kashe kuɗade.