Aminiya:
2025-06-30@23:16:31 GMT

Zargi: ’Yan sanda sun musanta sace tsohon Kwamishinan El-Rufai

Published: 15th, March 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, ta ƙaryata zargin da Tsohon Gwamna Nasir El-Rufai ya yi cewa jami’an tsaro sun sace tsohon Kwamishinansa, Jafaru Sani.

El-Rufai ya yi wannan iƙirari ne a shafinsa na sada zumunta cewa an ɗauke tsohon Kwamishinan kamar fursuna ba tare da bin ƙa’idojin doka ba.

Direba ya murƙushe yarinya ta mutu a artabu da jami’an tsaro a Edo Cutar sanƙarau ta kashe sama da mutum 50 a Sakkwato da Kebbi

Ya yi zargin cewa wata “ƙungiyar masu garkuwa da mutane” da ke da alaƙa da Gwamna Uba Sani ce ke da alhakin ɗauke tsohon Kwamishinan.

Da yake mayar da martani, kakakin ’yan sandan jihar, DSP Mansir Hassan, ya bayyana zargin a matsayin ƙarya.

“Babu wata ƙungiyar masu garkuwa da mutane a cikin Rundunar ’Yan Sandan Najeriya.

“Mu hukuma ce da ke aiki bisa kundin tsarin mulki don tabbatar da doka da oda,” in ji shi.

Ya buƙaci ’yan siyasa su guji yaɗa labaran da ba su da tushe.

“Yi wa jami’an tsaro ƙarya na iya haifar da ruɗani da kuma rage martabarsu. Idan mutum yana da ƙorafi, ya bi hanyar shari’a maimakon yaɗa kalaman da za su tayar da fitina,” a cewarsa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Jafaru Sani Tsohon Kwamishina zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe ubangidan Turji, Kacalla Ɗanbokolo a Zamfara
  • Magidanci ya kashe matarsa da adda a Yobe
  • Jami’an tsaro sun tarwatsa taron kwamitin amintattun PDP
  •   Ka’a’ni: Nasarar Da Mu Ka Samu Za Ta Ci Gaba Da Dorewa
  • Fararen hulan Isra’ila sun kai wa sojojin ƙasarsu hari
  • Aminu Ɗantata: Na roƙi Allah kada Ya ba ni abin da mutane ba za su amfana ba
  • Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
  • Iran Ta Shigar Da Korafi A Hukumar Kare Hakkin Bil’adama Ta MDD
  •  Sojojin Isra’ila: Da Gangan Muke Kashe Faladinawa A Wurin Karbar Taimakon Abinci
  • Za a tono gawar tsohon Gwamna Alao-Akala domin gwajin jinin ’ya’yansa