Aminiya:
2025-12-12@06:26:56 GMT

Zargi: ’Yan sanda sun musanta sace tsohon Kwamishinan El-Rufai

Published: 15th, March 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, ta ƙaryata zargin da Tsohon Gwamna Nasir El-Rufai ya yi cewa jami’an tsaro sun sace tsohon Kwamishinansa, Jafaru Sani.

El-Rufai ya yi wannan iƙirari ne a shafinsa na sada zumunta cewa an ɗauke tsohon Kwamishinan kamar fursuna ba tare da bin ƙa’idojin doka ba.

Direba ya murƙushe yarinya ta mutu a artabu da jami’an tsaro a Edo Cutar sanƙarau ta kashe sama da mutum 50 a Sakkwato da Kebbi

Ya yi zargin cewa wata “ƙungiyar masu garkuwa da mutane” da ke da alaƙa da Gwamna Uba Sani ce ke da alhakin ɗauke tsohon Kwamishinan.

Da yake mayar da martani, kakakin ’yan sandan jihar, DSP Mansir Hassan, ya bayyana zargin a matsayin ƙarya.

“Babu wata ƙungiyar masu garkuwa da mutane a cikin Rundunar ’Yan Sandan Najeriya.

“Mu hukuma ce da ke aiki bisa kundin tsarin mulki don tabbatar da doka da oda,” in ji shi.

Ya buƙaci ’yan siyasa su guji yaɗa labaran da ba su da tushe.

“Yi wa jami’an tsaro ƙarya na iya haifar da ruɗani da kuma rage martabarsu. Idan mutum yana da ƙorafi, ya bi hanyar shari’a maimakon yaɗa kalaman da za su tayar da fitina,” a cewarsa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Jafaru Sani Tsohon Kwamishina zargi

এছাড়াও পড়ুন:

‘Sojojin Najeriya da na Ivory Coast 200 sun shiga domin tsaftace Jamhuriyar Benin’

Ministan Harkokin Waje na Jamhuriyar Benin, Olushegun Adjadi Bakari, ya ce kimanin sojoji 200 daga Najeriya da Ivory Coast yanzu haka na cikin kasar shi a matsayin wani ɓangare na aikin tsaro don tallafa wa gwamnati.

Ƙaramar ƙasa ta Yammacin Afirka ta girgiza da yunƙurin juyin mulkin da bai yi nasara ba a ranar Lahadi, wanda ya sa Najeriya, Faransa da Ivory Coast suka tashi tsaye wajen goyon bayan gwamnatin farar hula.

Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa Ɗaliban Jami’ar Unijos 8 sun mutu a hatsarin mota

“A halin yanzu akwai kusan sojoji 200 da suka zo don ba da taimako ga rundunar tsaron Benin a cikin aikin sharewa da tsaftacewa,” in ji Olushegun Adjadi Bakari ga ’yan jarida a taron manema labarai da aka yi a Abuja ranar Alhamis.

Wata majiyar tsaro daga Ivory Coast ta ce Abidjan ta turo sojoji 50 a matsayin ɓangare na wannan aiki, inda ƙungiyar ECOWAS ta bayyana cewa za a haɗa da sojoji daga Ghana da Saliyo.

Najeriya ta ce sojojinta sun isa Benin tun ranar Lahadi. ECOWAS ba ta bayyana adadin sojojin da ake sa ran za su shiga ba.

Bakari ya ce lokacin da rundunar Benin ta nemi taimako, shirin juyin mulkin “ya riga ya yi wargaje.”

Ya ce sojojin Benin masu biyayya sun fatattaki harin farko, amma lamarin na buƙatar kulawa sosai don kauce wa asarar rayukan fararen hula.

“Mun nemi goyon bayan ’yan’uwa ba saboda rundunarmu ba za ta iya ba, amma saboda Shugaban Ƙasa bai so a yi asarar rayuka masu yawa ba.”

Ya ƙara da cewa kai hari kai tsaye zuwa sansanin masu juyin mulkin na iya haifar da zubar da jini mai yawa. “Shi ya sa Shugaba Patrice Talon ya nemi goyon bayan Jamhuriyar Tarayyar Najeriya.

“Rundunar Benin ta yi nasarar fatattakar wannan yunƙurin juyin mulki, amma haɗarin asarar rayuka da dama ya sa aka buƙaci martani na haɗin gwiwa.”

Ana ci gaba da tattaunawa kan ko sojojin tsaro na yankin za su ci gaba da zama na ɗan lokaci, amma Bakari ya ce duk wani mataki “za a ɗauka ne tare da haɗin gwiwar rundunar tsaro ta Benin, wadda ta nuna jarumta.”

Yadda Najeriya ta taimaka wa Benin — Tuggar

A taron ministocin ECOWAS da aka yi a Abuja, Ministan Harkokin Waje na Najeriya, Yusuf Maitama Tuggar, ya ce saurin matakan diflomasiyya, na soja da na leƙen asiri tsakanin Najeriya da Benin ne ya taimaka wajen dakile juyin mulkin.

Tuggar ya ce lamarin ya nuna yadda za a iya kare dimokuraɗiyya idan ƙasashe makwabta suna sadarwa yadda ya kamata.

Ya ce, “Haɗin kai don tabbatar da cewa dimokuraɗiyya ta ci gaba da kasancewa a Benin ya yi nasara, kuma wannan misali ne na abin da ya kamata a yi duk lokacin da dimokuraɗiyya ke fuskantar barazana a yankinmu.”

A halin yanzu, kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito cewa Pascal Tigri, wanda ake zargi da jagorantar juyin mulkin da bai yi nasara va, tare da abokan aikinsa suna buya a Togo.

A ranar Laraba, jami’an gwamnatin Benin suka shaida wa Reuters cewa shugaban juyin mulkin yana gudun hijira a Lome 2, unguwa a babban birnin Togo inda gidan shugaban ƙasar, Faure Gnassingbe yake.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Rawar Gani A Kafa Gidauniyar Fuskantar Matsalar Tsaro
  • ‘Sojojin Najeriya da na Ivory Coast 200 sun shiga domin tsaftace Jamhuriyar Benin’
  • An kai hari gidan jami’in ɗan sanda a Yobe
  • EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige
  • Ba ni da shirin ficewa daga PDP — Gwamnan Bauchi
  • Rikicin Iyakar Thailand da Cambodia Ya Tilasta wa Dubban Mutane Barin Muhallansu
  • An kama wani mutum a Abuja yana ƙoƙarin kai harsasai ga ’yan bindiga a Zamfara
  • Dalibin jami’a ya rasu a hatsarin motar murnar kammala jarabawa
  • Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Benin – Soyinka
  • Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Jamhuriyar Benin – Soyinka