A yau Alhamis ne mataimakin shugaban kasar Sin Han Zheng, ya halarci bikin bude dandalin tattaunawa kan zaman lafiya na duniya karo na 13, a jami’ar Tsinghua inda kuma ya gabatar da jawabi.

A cikin jawabin nasa, Han Zheng ya bayyana cewa, a halin yanzu an samu babban sauyi a duniya, tare da fuskantar batutuwan kasa da kasa da yankuna da dama, don haka ana fuskantar kalubale a sha’anin kiyaye zaman lafiya da samun ci gaban duniya.

Ya ce, tunanin raya al’umma mai kyakkyawar makoma ga dukkan bil’adama, da kiran samun bunkasar duniya, da kiran kiyaye tsaron duniya, da kuma kiran kiyaye al’adun duniya da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar, sun samar da ra’ayoyin Sin kan daidaita manyan batutuwan duniya dake shafar zaman lafiya, da bunkasa rayuwar bil’adama baki daya.

Han Zheng, ya gabatar da shawarwari hudu, inda da farko ya ce kamata ya yi a koyi fasahohi daga abubuwan da suka gabata, da tabbatar da odar kasa da kasa bayan yakin duniya na 2. Na biyu kuma a ci gaba da yin hadin gwiwa wajen sarrafa harkokin duniya baki daya. Na uku a kiyaye bude kofa ga kasashen waje, don sa kaimi ga samun wadata da ci gaba a duniya. Kana na hudu a goyi bayan juna don cimma nasarar zamanantarwa tare. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa

A zahiri, zamanin da kasashen yammacin duniya ke ba da umarni ga kasashe masu tasowa ya riga ya wuce. An taba bin tsare-tsaren da kasashen yamma suka tanada, amma ba a samu nasarar da aka sa ran samu ba, wannan sakamako ya sa kasashe masu tasowa daina amincewa da huldar kasa da kasa da kasashen yamma suka tsara. Sai dai, ko wace irin sabuwar dangantakar sassan kasa da kasa muke bukata a zamanin yau?

 

A matsayinta na daya daga cikin kasashe masu tasowa, kasar Sin ta sha yin kira da a kafa sabon nau’in huldar kasa da kasa bisa tushen mutunta juna, da adalci, da hadin gwiwa don tabbatar da moriyar juna. Wannan tunani shi ma ya bayyana sarai a cikin babbar shawarar inganta jagorancin duniya da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar a watan jiya.

 

Yayin da ake kawo karshen tsohon zamanin da kasashen yammacin duniya ke taka rawa a matsayin masu ba da umarni a duniya, kasashe masu tasowa, ciki har da kasashen Afirka da kasar Sin, za su kara kawo ci gaba mai inganci, da adalci, da daidaito ga duniya, yayin da suke kokarin aiwatar da wasu sabbin tunani, gami da raya su a kai a kai. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Ra'ayi Riga Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka October 7, 2025 Ra'ayi Riga Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang September 30, 2025 Ra'ayi Riga Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka September 29, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta
  • Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya
  • Araghchi : Trump bai cancanci mai samar da zaman lafiya ba yayin da yake haifar da yake-yake
  • Mahalarta Taron ‘Sherm-Sheikh” Sun Rattaba Hannu Akan Yarjejeniyar Zaman Lafiya
  • Iran Ta Gabatar Da Shawarar Kulla Yarjejeniyar Tausayawa A Tsakanin Matan Duniya
  • Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya
  • Iran Ba Zata Halarci Zaman Taron Sharm El-Sheikh Ba Saboda Wasu Dalilai Da Ta Byyana
  • Trump, da Al’Sisi za su jagoranci taron zaman lafiya kan Gaza a Masar ranar Litinin  
  • Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka
  • Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa