Aminiya:
2025-07-03@21:57:56 GMT

Lukurawa Sun Kashe Mutane 15 a Sakkwato

Published: 3rd, July 2025 GMT

Wasu ‘yan bindigar da ake zargi Lukurawa ne a wani sabon hari sun kashe mutane sama da 15 a Qaramar Hukumar Tangaza ta jihar Sakkwato, ranar Litinin da ta gabata.

Babban Jami’i a Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Qasa(Red Cross) reshen Sakkwato Alhaji Abubakar Ainu ya tabbatar wa Aminiya harin wanda ya yi matuqar tayar da hankalin mutanen yankin ganin an xauki dogon lokaci kafin kawo irin wannan hari mai muni.

Ainu ya ce, “jami’anmu na sa kai sun ziyarci qauyen Kwalajiya na mazabar Magoho a garin Tangaza domin jajantawa da kuma halartar sallah janaza ta muanen da ‘yan bindigar suka kashe sama da 15.  Waxanda suka jikkata an kai su Asibitin Kashi na Wamakko da Asibitin Koyarwa ta Xanfodiyo da na Qwararru a birnin jiha domin karvar magani.”

Ya ce yankin na cikin wuraren da ke fama da matsalar tsaro ta varayin shanu da masu tayar da qayar baya.

“Wannan lamari baya da daxi ko kaxan, dubi yadda aka mayar da wasu mata zawarawa aka mayar da wasu yara marayu domin biyan wata buqata wadda addini bai yarda da ita ba, ina kira ga hukuma ta sake salon yaqar ‘yan bindiga da take yi,” in ji Ainu.

Wani mazauni qauyen Kwalajiya ya ce ‘yan bindigar Lukurawa sun zo a qauyen a daren Lahadi har zuwa Asuba ta ranar Litinin in da suka kashe wasu mutane a harin da suka kai, a lokacin da suka yi ta harbi kan mai uwa da wabi.

“Bayan sun kashe mana mutane sun tafi da dabbobi masu yawa, duk da mutanenmu sun yi qoqari amma yawan mutane da makaman da suke xauke da su ya sa suka fi qarfinmu. Har zuwa yanzu ba mu san adadin waxanda aka kai asibiti ba domin suna da yawa, sai dai waxanda suka rasu 15 muka yi wa Sallah.

“Muna kira ga jami’an tsaro su mayar da hankali wurin korar mana waxannan ‘yan bindigar don mu samu zaman lafiya a jiha baki xaya.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan bindigar

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan Najeriya sun fara begen Buhari saboda azabar Tinubu – Amaechi

Tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi, ya ce wahalhalu sun yi yawa a Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, wanda har ya sa mutane suka fara fatan dawowar tsohon Shugaba Muhammadu Buhari.

Yayin da yake magana a birnin Abuja, Amaechi ya ce Najeriya ta taɓarɓare matuƙa, inda ya ce sauyin gwamnati ne kawai zai magance matsaloli.

Gwamnatin Yobe ta rufe kasuwanni 3 saboda matsalar tsaro Ɗan wasan Liverpool, Diogo Jota, ya mutu a hatsarin mota

“Farashi kayayyaki ya tashi sosai. Mutane ba za su iya siyan abinci ba. Babu kuɗi. Komai ya lalace,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa rayuwa ta yi tsanani har mutane sun fara tunawa da zamanin Buhari da muradin dawowarsa kan mulki.

“Yanzu mutane na so Buhari ya dawo. A Najeriya, kowace sabuwar gwamnati tana ƙara muni fiye da ta baya. Wannan shi ne dalilin da ya sa mutane ke ci gaba da tunanin gwamnatin da ta gabata,” in ji shi.

Amaechi ya bayyana cewa ya fice daga jam’iyyar APC a daren ranar Talata, inda yanzu ya koma jam’iyyar haɗaka ta ADC.

Ya ce tuni ya daina shiga harkokin jam’iyyar APC tun da daɗewa.

“Na fice daga APC jiya da daddare. Ban halarci taro ko guda ɗaha ba. Na taɓa gargaɗinsu, kuma na rubuta musu kada su sake gayyatata. Ba za ka zauna cikin ƙungiyar da yawancinsu suke satar dukiya ba, kai kuma ka yi shiru,” in ji shi.

Da aka tambaye shi me ya sa yake sukar gwamnatin da ya taɓa yi wa aiki, Amaechi ya ce matsalar Najeriya ba kawai shugabanci ba ne, sai an gyara tsarin gaba ɗaya.

Ya ce akwai bukatar fara shiri, ba kawai kafa jam’iyya ba, wanda zai haɗa ‘yan Najeriya su ƙwato ƙasarsu da hannunsu.

Amaechi ya kuma ce bai taɓa ganin Tinubu a matsayin mutum wanda ya cancanci ya mulki Najeriya ba.

“Na taɓa cewa Tinubu ba shi da ɗabi’u shugabanci. Har yanzu ra’ayina kenan,” in ji shi.

Ya soki yadda gwamnati ke tafiyar da tattalin arziƙi, musamman faɗuwar darajar Naira.

“Lokacin Buhari, dala tana kusa da Naira 460 ko Naira 500. Yanzu ta kai Naira 1580. Wannan ya fi kashi 100,” in ji shi.

Da aka tambaye shi ko wannan matsala ta Naira wata dabara ce ta gwamnati, Amaechi musanta hakan.

Ya ce, “Ko dabara ce ko akasin haka, duk wata gwamnati da ba ta damu da rayuwar mutane ba, ba za a ce dabara ce mai kyau ba.”

Tsohon Ministan Shari’a, Abubakar Malami, shi ma ya fice daga jam’iyyar APC, inda ya bu sahun Amaechi wajen komawa jam’iyyar ADC.

Ficewarsu da wasu manyan jiga-jigan siyasa na nuni da juyin juya hali kafin babban zaɓen 2027, yayin da jam’iyyar ADC ke neman zama sabuwar babbar jam’iyyar adawa a ƙasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lakurawa sun kashe mutane 15 a Sakkwato
  • ’Yan Najeriya sun fara begen Buhari saboda azabar Tinubu – Amaechi
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara
  • ’Yansanda Sun Ceto Ɗan Ghana, Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 3
  • Lakurawa sun kashe mutum 15 a harin ramuwar gayya a Sakkwato
  • An Kashe Kusan Mutane 1500 Kan Sabanin Mazhaba A Kasar Siriya A Wata Guda
  • Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram 10 a Borno
  • Togo: An Kashe Mutane 7 A Zanga-zangar Kin Jinin Gwamnati
  • An Kashe ‘Yan Kungiyar Shabab 19  A Kasar Somaliya