Sharhin Bayan Labarai: Dandalin Tattaunawa Na Tehran
Published: 19th, May 2025 GMT
Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka, sharhin bayan labarummu zai yi magana dangane da taron tattaunawa ta Tehran wanda aka bude a ranar Lahadi 18 ga watan mayu a nan Tehran.
A ranar Lahadi 18 ga watan Mayu da muke ciki ne aka bude taron tattaunawa da ta Tehran ta farko a nan Iran, don tattauna batutuwan da suka shafi kasashen yankin yammacin Asiya.
An sami halattan baki daga kasashe 53 daga cikinsu akwai jami’an gwamnatoci wadanda suka hada da ministoci masana da shuwagabannin cibiyoyin bincike da bada shawarori na kasashen duniya da dama.
Daga cikin bakin akwai ministan harkokin wajen kasar Oman Badr bin Hamad Al Busaidi wanda ya fadawa tashar talabijin ta Presstv kan cewa yankin yammacin Asiya a halin yanzu yana fuskantar matsaloli wadanda suke bukatar a tattaunasu tsakanin kasashen yankin. Ya kuma kara da cewa kasar Omman a shirye take ta shiga tattaunawa don fahintar juna ko da da wanda take da sabani sosai da ita ne kuwa. Ministan ya bada misali da rikicin kasar Falasdinu, wanda ya zarce dukka matsaloli yankin yammacin Asiya, har ya zama matsala ta kasashen duniya.
Ya ce: Abinda Falasdinawa suke fuskanta a hannun HKI a halin yanzu ya zama babban matsala da damuwa ga kasashen duniya da dama.
Albusaiti ya bayyana cewa abinda yake faruwa a kasar Falasdinu, bai kamata ya auku ba, ko kuma ba zai faru ba, da anbi hanyar tattaunawa tun lokaci bai kure ba. Ya kammala da cewa “Tattaunawar Tehran” wata dama ce ga wadanda suka yi Imani da tattaunawa a matsayin hanya tilo ta warware matsaloli tsakanin kasashe.
Sai kuma ministan harkokin wajen kasar Tajakisatn wanda ya bayyana cewa kasashen duniya suna bukatar tattaunawa mai zurfi don warware matsaloli masu yawa da take fama da su.
Sirajuddin Muhriddin ya kara da cewa kasashen duniya suna bukatar tattaunawa mai zurfi da kuma gudanar da bincike masu yawa don warware dimbin matsalolin da ake fuskanta da suka shafi tsaro da tabbatar da zaman lafiya a duniya.
Ministan ya bayyana a cikin jawabinda ya gabatar kan cewa lalle kasashen duniya suna bukatar tattaunawa saboda ganin yadda al-amura suke sauyawa a cikinta da sauri.
Yace wuce gona da iri da tsatsauran ra’ayi wadanda suka kaiwa ga tashe-tashen hankula sun zama babban barazana ga dukkan mutanen a duniya. Ya yi kira ga kasashen duniya su gaggauta daukan bai-daya don magance da kuma kawo karshen kara fadadar wadannan matsaloli.
Ya bukaci a samar da shirin bai daya na samar da tsaro a wannan yankin don tabbatar da tsaro da zaman lafiya a cikinsa.
Ministan harkokin wajen kasar Tajakistan ya kammala da cewa, wasu tsare-tsaren da ake da su a halin yanzu a yankin ba zasu iya tabbatar da zaman lafiya da kuma warware matsaloli tsakanin kasashen yankin ba, don haka akwia bukatar tattaunawa mai zurfi a tsakaninsu don cimma wannan manufar.
Sai kuma sakataren majalisar tsaro ta kasar Armenia wanda ya bayyana cewa kasarsa tana kokarin tabbatar da tsawo da zaman lafiya a kasar, da kuma makobta.
Armen Grigoryan ya bayyana cewa shirin gwamnatin kasar na (Drossroad For Peace) wanda aka kaddamar da shi a cikin watan Octoban shekara ta 2023 yana dauke da manufar bude hanyoyin bunkasa tattalin arzikin yankin wanda ya dade yana tseye baya motsawa, ya zama ya samar da cudayya da juna a yankin saboda ci gaban kowa. Ya ce munyi Imani kan cewa wannan shirin yana da muhimmanci wajen bunkasa tattalin arziki wanda kuma zai kai ga samar da zaman lafiya mai dorewa a yankin.
Sannan tsohon firai ministan kasar Iraqi Adil Abdulmahdi, a jawabinda ya gabatar a dandalin tattaunawa na Tehran wato “Tehran Dialoque Furum”, ya ce kasashen larabawa da sauran kasashen duniya duk, sun kasa warware rikicin Falasdinawa da HKI. Ya kuma kara da cewa kissan kiyashin da ke faruwa a Gaza, wata babbar matsala ce wacce ta girgiza dukkan mai lamiri a cikin zuciyarsa.
Abdul Mahdi ya cewa hatta kotun kasa da kasa ta ICC ta kasa dakatar da kisan kiyashin da HKI take aikawa a Gaza wanda ya nuna irin lalacewra da al-amura suka yi a duniya a yau.
Tsohon firai ministan ya kara da cewa abinda yake faruwa a Gaza, Holocus ne a fili wanda al-amarin bai tsaya nan ba, birane a yankin yamma da kogin Jordan da Lebanon duk suna fauskantar wannan matsalar daga HKI.
Daga karse yayi kira ga kasashen duniya su tashi su nuna cewa sun damu da binda ke faruwa a Gaza, mai yuwa mu kawo karshen wannan kissan kare dangin.
Abdul Mahdi ya rufe da cewa tarihi zata riki wasu da dama da shirun da suka yi a ta’asar da HKI take aikawata a Gaza.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: ministan harkokin wajen kasar kasashen duniya su bukatar tattaunawa da zaman lafiya ya bayyana cewa kara da cewa tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
Gwamnatin mamayar Isra’ila ta yanke hukuncin kisa kan masu fama da cutar kansa da kuma waɗanda suke fama da matsalar koda na mutuwa a Gaza domin hana fitar da su wata kasa don neman magani
Cibiyar Kare Hakkin Dan Adam ta Gaza ta bayyana matukar damuwarta game da tabarbarewar lafiyar marasa lafiya da ke fama da cutar kansa da kuma cutar koda a Zirin Gaza. Wadannan cututtuka sun kara ta’azzara ne sakamakon hare-haren sojojin mamayar Isra’ila kan Gaza da kuma ci gaba da killace yankin bayan tsagaita bude wuta, gami da hana shigar dq magunguna da kayayyakin ayyukan likitanci masu muhimmanci cikin yankin. Cibiyar ta kuma yi nuni da tsauraran matakan fitar da marasa lafiya zuwa ƙasashen waje don neman magani.
A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Lahadi, Cibiyar ta tabbatar da cewa, wannan yanayin ba shi da wata shakka cewa Isra’ila na aiwatar da manufar kisan gilla a kan dubban marasa lafiya ta hanyar hana su ‘yancinsu na rayuwa da magani da gangan, da kuma canza wahalarsu zuwa wani nau’in hukunci na gama gari.
Cibiyar ta ambaci majiyoyin lafiya da ke tabbatar da cewa, akwai marasa lafiya 12,500 da ke fama da cutar kansa a Zirin Gaza, ciki har da ƙananan yara. Ta lura cewa mata sun kai kusan kashi 52% na dukkan masu cutar kansa a Gaza.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher November 2, 2025 IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya November 2, 2025 Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci November 2, 2025 Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza November 2, 2025 Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran November 2, 2025 Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari November 2, 2025 Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon November 2, 2025 Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya November 2, 2025 Shugaban AmurkaTrump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya November 2, 2025 Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar November 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci