HausaTv:
2025-05-19@20:27:09 GMT

Sharhin Bayan Labarai: Dandalin Tattaunawa Na Tehran

Published: 19th, May 2025 GMT

Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka, sharhin bayan labarummu zai yi magana dangane da taron tattaunawa ta Tehran wanda aka bude a ranar Lahadi 18 ga watan mayu a nan Tehran.

A ranar Lahadi 18 ga watan Mayu da muke ciki ne aka bude taron tattaunawa da ta Tehran ta farko a nan Iran, don tattauna batutuwan da suka shafi kasashen yankin yammacin Asiya.

Inda shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiyan da kuma ministan harkokin wajen kasar Iran suka gabatar da jawaban farko a taron.

An sami halattan baki daga kasashe 53 daga cikinsu akwai jami’an gwamnatoci wadanda suka hada da ministoci  masana da shuwagabannin cibiyoyin bincike da bada shawarori na kasashen duniya da dama.

Daga cikin bakin akwai ministan harkokin wajen kasar Oman Badr bin Hamad Al Busaidi wanda ya fadawa tashar talabijin ta Presstv kan cewa yankin yammacin Asiya a halin yanzu yana fuskantar matsaloli wadanda suke bukatar a tattaunasu tsakanin kasashen yankin. Ya kuma kara da cewa kasar Omman a shirye take ta shiga tattaunawa don fahintar juna ko da da wanda take da sabani sosai da ita ne kuwa. Ministan ya bada misali da rikicin kasar Falasdinu, wanda ya zarce dukka matsaloli yankin yammacin Asiya, har ya zama matsala ta kasashen duniya.

Ya ce: Abinda Falasdinawa suke fuskanta a hannun HKI a halin yanzu ya zama babban matsala da damuwa ga kasashen duniya da dama.

Albusaiti ya bayyana cewa abinda yake faruwa a kasar Falasdinu, bai kamata ya auku ba, ko kuma ba zai faru ba, da anbi hanyar tattaunawa tun lokaci bai kure ba. Ya kammala da cewa “Tattaunawar Tehran” wata dama ce ga wadanda suka yi Imani da tattaunawa a matsayin hanya tilo ta warware matsaloli tsakanin kasashe.

Sai kuma ministan harkokin wajen kasar Tajakisatn wanda ya bayyana cewa kasashen duniya suna bukatar tattaunawa mai zurfi don warware matsaloli masu yawa da take fama da su.

Sirajuddin Muhriddin ya kara da cewa kasashen duniya suna bukatar tattaunawa mai zurfi da kuma gudanar da bincike masu yawa don warware dimbin matsalolin da ake fuskanta da suka shafi tsaro da tabbatar da zaman lafiya a duniya.

Ministan ya bayyana a cikin jawabinda ya gabatar kan cewa lalle kasashen duniya suna bukatar tattaunawa saboda ganin yadda al-amura suke sauyawa a cikinta da sauri.

Yace wuce gona da iri da tsatsauran ra’ayi wadanda suka kaiwa ga tashe-tashen hankula sun zama babban barazana ga dukkan mutanen a duniya. Ya yi kira ga kasashen duniya su gaggauta daukan bai-daya don magance da kuma kawo karshen kara fadadar wadannan matsaloli.

Ya bukaci a samar da shirin bai daya na samar da tsaro a wannan yankin don tabbatar da tsaro da zaman lafiya a cikinsa.

Ministan harkokin wajen kasar Tajakistan ya kammala da cewa, wasu tsare-tsaren da ake da su a halin yanzu a yankin ba zasu iya tabbatar da zaman lafiya da kuma warware matsaloli tsakanin kasashen yankin ba, don haka akwia bukatar tattaunawa mai zurfi a tsakaninsu don cimma wannan manufar.

Sai kuma sakataren majalisar tsaro ta kasar Armenia wanda ya bayyana cewa kasarsa tana kokarin tabbatar da tsawo da zaman lafiya a kasar, da kuma makobta.

Armen Grigoryan ya bayyana cewa shirin gwamnatin kasar na (Drossroad For Peace) wanda aka kaddamar da shi a cikin watan Octoban shekara ta 2023 yana dauke da manufar bude hanyoyin bunkasa tattalin arzikin yankin wanda ya dade yana tseye baya motsawa, ya zama ya samar da cudayya da juna a yankin saboda ci gaban kowa. Ya ce munyi Imani kan cewa wannan shirin yana da muhimmanci wajen bunkasa tattalin arziki wanda kuma zai kai ga samar da zaman lafiya mai dorewa a yankin.

Sannan tsohon firai ministan kasar Iraqi Adil Abdulmahdi, a jawabinda ya gabatar a dandalin tattaunawa na Tehran wato “Tehran Dialoque Furum”,  ya ce kasashen larabawa da sauran kasashen duniya duk, sun kasa warware rikicin Falasdinawa da HKI. Ya kuma kara da cewa kissan kiyashin da ke faruwa a Gaza, wata babbar matsala ce wacce ta girgiza dukkan mai lamiri a cikin zuciyarsa.

Abdul Mahdi ya cewa hatta kotun kasa da kasa ta ICC ta kasa dakatar da kisan kiyashin da HKI take aikawa a Gaza wanda ya nuna irin lalacewra da al-amura suka yi a duniya a yau.

Tsohon firai ministan ya kara da cewa abinda yake faruwa a Gaza, Holocus ne a fili wanda al-amarin bai tsaya nan ba, birane a yankin yamma da kogin Jordan da Lebanon duk suna fauskantar wannan matsalar daga HKI.

Daga karse yayi kira ga kasashen duniya su tashi su nuna cewa sun damu da binda ke faruwa a Gaza, mai yuwa mu kawo karshen wannan kissan kare dangin.

Abdul Mahdi ya rufe da cewa tarihi zata riki wasu da dama da shirun da suka yi a ta’asar da HKI take aikawata a Gaza.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: ministan harkokin wajen kasar kasashen duniya su bukatar tattaunawa da zaman lafiya ya bayyana cewa kara da cewa tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

ISWAP ta kashe manoma sama da 50 a Borno

Aƙalla manoma 50 ne suka rasu, sakamakon wani mummunan hari da ‘yan ta’addan ISWAP suka kai garin Malam Karanti da ke Ƙaramar Hukumar Kukawa, a jihar Borno.

Majiyoyi sun ce mayaƙan sun afka wa manoma yayin da suke noma da kamun kifi, duk da cewar suna biyan haraji kafin yin noma.

Tinubu ya isa Rome don rantsar da sabon Fafaroma Tsafta a gidan aure: Abubuwan da kowace mace ya kamata ta sani

“Sun mallaki takardun izini daga kwamandan ISWAP da ke kula da yankin Malam Karanti har zuwa Dawashi. Sun jima suna samun kariya daga Amir Akilu, wanda shi ne kwamandan yankin,” in ji wani mazaunin yankin.

Sai dai harin ya faru ne a lokacin da kwamandan bai kasance a yankin ba, inda wasu daga cikin mayaƙan suka zargi manoman da leƙen asiri, inda suka ce suna taimaka wa abokan gabansu.

Wannan ne dalilin da ya sa suka kai harin.

Wani wanda ya tsallake rijiya da baya a harin ya ce: “Mun fara girbin wake ne lokacin da suka zo. Sun kewaye mu, suka ce duk wanda ya yi yunƙurin tserewa za su harbe shi.

“Wasu daga cikinmu sun yanke shawarar guduwa duk da hakan. Sun kashe sama da mutum 50, da yawa daga cikinsu an yanka su.

“Sannan sun kama wasu daga cikinmu. Yau ma sun je Dawashi sun kashe mutane, amma ba a san adadin waɗanda suka kashe ba tukuna.”

Gwamnati da hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa dangane da wannan mummunan hari ba.

Wannan hari ya zo cikin watanni biyar kacal bayan wani makamancin sa da aka kai ƙauyen Dumba, inda manoma aƙalla 40 suka rasa rayukansu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yankin Taiwan Ba Shi Da Iko Ko Hujjar Halartar Taron WHA
  • Taron Tehran ya bukaci tattaunawa cikin gaggawa kan kalubalen yankin  
  • Tehran ta yi kakkausar suka kan tsare Iraniyawa a Birtaniya
  • MDD: Yunwa Ta Kara Tsanani A Duniya Daga Shekarar 2024
  • Kafofin Yada Labarai Na Amurka Sun Bayyana Kuzari Da Ci Gaban Da Fina-finan Kasar Sin Ke Samu A Bikin Cannes 
  • ISWAP ta kashe manoma sama da 50 a Borno
  • Jagora: Jawaban Trump A Ziyar Da Ya Kai Wasu Kasashen Larabawa Na Yankin Tekun Farisa Abin Kunya Ne Gare Shi Ga Kuma Amurkawa
  • Iran: Aiwatarda Yarjeniyar Zaman Lafiya Tsakanin Armenia Da Arzerbaijan Zai Tabbatar Da Zaman Lafiya A Tsakanin Kasashen Biyu
  • Hamas Ta Ce An Fara Tattaunawa Tare Da HKI Kan Tsakana Wuta A Doha A Yau Asabar