Iran ta yi watsi da zarge-zargen taron kasashen Larabawa game da tsibirai uku na Tekun Fasha

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya yi watsi da zarge-zargen da ke kunshe a cikin bayanin karshe na taron kasashen Larabawa a Bagadaza dangane da tsibiran Iran guda uku na Babban Tunb, Karamin Tunb da Abu Musa.

Isma’il Baqa’i ya tabbatar a jiya Litinin 19 ga watan Mayu cewa: Tsibiran nan uku na Babban Tunb, Karamin Tunb da Abu Musa wasu bangarori ne na kasar Iran, yana mai cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana ganin duk wani da’awar a wannan fanni ya sabawa ka’idojin yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya da dokokin kasa da kasa, da kuma keta mutuncin yankunan kasa da ka’idojin kasa da kasa a matsayin makwabciyar kasa. Yana ganin gabatar da irin wannan batu a cikin bayanin karshe na taron kasashen Larabawa ba abu ne da za a amince da shi ba.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya shawarci kungiyar kasashen hadin kan Larabawa da ta yi la’akari da tabbatattun hujjoji na tarihi da na kasa a lokacin da suke tsara matsayinsu, maimakon yin zarge-zargen da ba su da tushe, da kuma kokarin kara fahimtar juna da alaka a tsakanin kasashen yankin.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasashen Larabawa

এছাড়াও পড়ুন:

JMI Ta Bukaci Kungiyar Majalisun Dokoki Ta Duniya Su Kori HKI Daga Cikinta

Shugaban tawagar Iran a kungiyar hada kan majalisun dokokin kasashen duniya ya bukaci kungiyar ta yi tir da HKI saboda hare-haren da ta kai mata wanda ya keta dokokin kasa da kasa, ya kuma bukaci a koreta daga kungiyar.

Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto Manoorchehr Mottaki yana fadar haka a wata wasikar da ya aikewa shugaban kungiyar majalisun dokokin ta duniya wato IPU, shugaban Tulia Ackson, ya ce abin  fata shi ne kungiyar zata yi tir da HKI kan sabawa doka ta 2(4) na MDD.

Har’ila yau Mottaki ya bayyana cewa yana fatan Ackson zai sa a jingine samuwar HKI a kungiyar.

Ya ce majalisar majalisun ta tattauna dangane da hare-haren Amurka da HKI kan kasar Iran su kumka yi All..wadai da su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi
  • Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar
  • Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Irin Aniyar Da Gwamantinsa Ta Kudurta Wajen Kare Tsaron Kasa Da Al’ummarta
  • Rasha Ta Jaddada Aniyarta Ta Karfafa Hadin Gwiwa Da Jamhuriyar Musulunci Ta Iran
  • JMI Ta Bukaci Kungiyar Majalisun Dokoki Ta Duniya Su Kori HKI Daga Cikinta
  • Wakilan Kasashen Duniya Da Kungiyoyin Sun Je Ta’aziyya Mutanen Da Suka Yi Shahada A Yakin Iran Da H.K.Isra’ila
  • Magajin Garin Birnin Tehran Ya Karyata Da’awar ‘Yan Sahayoniyya
  • An Kashe ‘Yan Kungiyar Shabab 19  A Kasar Somaliya
  •   ‘Yan Guudun Hijirar Sudan Miliyan 4 Suna Fuskantar Yunwa A Kasashen Makwabta