Iran Ta Yi Watsi Da Da’awar Kungiyar Hadin Kan Kasashen Larabawa Kan Tsibiran Kasarta
Published: 19th, May 2025 GMT
Iran ta yi watsi da zarge-zargen taron kasashen Larabawa game da tsibirai uku na Tekun Fasha
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya yi watsi da zarge-zargen da ke kunshe a cikin bayanin karshe na taron kasashen Larabawa a Bagadaza dangane da tsibiran Iran guda uku na Babban Tunb, Karamin Tunb da Abu Musa.
Isma’il Baqa’i ya tabbatar a jiya Litinin 19 ga watan Mayu cewa: Tsibiran nan uku na Babban Tunb, Karamin Tunb da Abu Musa wasu bangarori ne na kasar Iran, yana mai cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana ganin duk wani da’awar a wannan fanni ya sabawa ka’idojin yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya da dokokin kasa da kasa, da kuma keta mutuncin yankunan kasa da ka’idojin kasa da kasa a matsayin makwabciyar kasa. Yana ganin gabatar da irin wannan batu a cikin bayanin karshe na taron kasashen Larabawa ba abu ne da za a amince da shi ba.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya shawarci kungiyar kasashen hadin kan Larabawa da ta yi la’akari da tabbatattun hujjoji na tarihi da na kasa a lokacin da suke tsara matsayinsu, maimakon yin zarge-zargen da ba su da tushe, da kuma kokarin kara fahimtar juna da alaka a tsakanin kasashen yankin.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasashen Larabawa
এছাড়াও পড়ুন:
JMI Ta Bukaci Kungiyar Majalisun Dokoki Ta Duniya Su Kori HKI Daga Cikinta
Shugaban tawagar Iran a kungiyar hada kan majalisun dokokin kasashen duniya ya bukaci kungiyar ta yi tir da HKI saboda hare-haren da ta kai mata wanda ya keta dokokin kasa da kasa, ya kuma bukaci a koreta daga kungiyar.
Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto Manoorchehr Mottaki yana fadar haka a wata wasikar da ya aikewa shugaban kungiyar majalisun dokokin ta duniya wato IPU, shugaban Tulia Ackson, ya ce abin fata shi ne kungiyar zata yi tir da HKI kan sabawa doka ta 2(4) na MDD.
Har’ila yau Mottaki ya bayyana cewa yana fatan Ackson zai sa a jingine samuwar HKI a kungiyar.
Ya ce majalisar majalisun ta tattauna dangane da hare-haren Amurka da HKI kan kasar Iran su kumka yi All..wadai da su.