Kudirin ya kuma nemi kafa wata hanyar warware takaddama don magance rikice-rikicen da suka shafi jam’iyyun siyasa, mambobinsu, ‘yan takara masu zaman kansu, da kuma kawance. Bugu da kari, ta tanadi hukunci kan keta haddi da bayar da shawarar gyara ga dokar zabe ta 2022 don cire rajistar jam’iyyun siyasa daga hukumar INEC.

Bayan gabatar da shawarwari, an mika kudirin ga kwamitin majalisa mai kula da harkokin zabe da kwamitin jam’iyyun siyasa domin ci gaba da tattaunawa a kansa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Matsalar rashin tsaro ce ta sa na yi waqar “Arewa”-SKD Arewa

Matsalar rashin tsaro ce ta sa na yi waqar “Arewa”-SKD Arewa

Muhsin Umar Chiroma wanda aka fi sani suna SKD Arewa, xaya ne daga cikin matasan mawaqan zamani da ludayinsu ke kan dawo wajen tashe, musamman a shafukan sada zaumunta. A hirarsa da Aminiya, saurayin mawaqin ya bayyana abin da ya xauki hankalinsa har ya yi wata waqa da ya yi wa laqabi da suna ‘Arewa’.

Muhsin wanda ya fi qwarewa a fagen waqoqin ‘Gambara’, da aka fi sani da Hip Hop, bayyana wa Aminiya cewa, halin da Arewacin Nijeriya ya shiga na rashin tsaro shi ne jigon waqarsa.

A cikin waqar haziqin mawaqin, ya yi tsokaci a kan yadda shugabanni a Arewa suka yi biris da halin da talakawa suka tsinci kansu a ciki na barazanar ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane da sauran matsalolin tsaro. Inda yake qoqarin ganin ya jawo hankalin masu muli da ma talakawa don su farka daga barci.

Matashi mawaqin ya ce, “waqata mai taken ‘Arewa’, waqa ce da zan ce na yi ta ne saboda in tayar da shugabanni da kuma talakawan Arewacin Nijeriya daga barci. Domin kuwa ga gobara nan ta tunkaro mu daga kogi amma kuma da alamu babu wanda ya damu da ita.”

Da yake amsa tambayar ko me ya sa ya zavi yin amfani da waqa don wayar da kan jama’a kan muhimmancin haxin kai don tunkarar wannan matsala? Mawaqin zamanin sai ya ce, “ka san kowa da dutsen da ke hannunsa zai yi jifa. Don haka tunda yake ina da fasahar waqa, shi ya sa na ga wannan ita ce, kawai hanya xaya tilo da tafi sauqi wajena in isar da wannan muhimmin saqo.”

Matashin ya bayyana cewa, ya zuwa yanzu akwai fitattun mawaqan da suka yi waqoqi kan abin da ya shafi tavarvarewar tsaro a qasa. Amma duk da haka, ya dace manya fitattun mawaqa na zamani da duniya ta san su, su qara qaimi wajen wayar da kan matasa don su guji shiga ayyukan laifi da ke jefa qasa cikin rashin tabbas.

SKD Arewa, ya kuma shawarci matasan mawaqa da su rungumi karatu, domin a cewarsa, ilimi ne zai taimaka musu wajen inganta sana’o’insu kuma ya basu damar amfani da shafukan sada zumunta wajen tallata fasahohinsu.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cin hanci da rashawa sun yi ƙatutu a Najeriya — ICPC
  • Rikicin Iyakar Thailand da Cambodia Ya Tilasta wa Dubban Mutane Barin Muhallansu
  • Australia ta Fara Aiwhatar da Dokar Hana Yara Amfani da Shafukan Sada Zumunta
  • Iran Tana Daukar Bakwancin Taron BRICS Na Binciken Kimiya Da Kuma Ci Gaban Ilmi
  • ’Yan jaridar Daily Trust da Trust TV sun lashe kyautar binciken ƙwaƙwaf ta Wole Soyinka ta bana
  • Saudiya da Qatar Zasu Gina Layin Dogo Mai Sauri Tsakanin Kasashen Biyu
  • Matsalar rashin tsaro ce ta sa na yi waqar “Arewa”-SKD Arewa
  •  Kasashen Iran Da Turkiya Za Su Bunkasa Alakarsu A Fagen Ilimi Da Musayar Fasaha
  • IRGC: Makaman Iran Sun Fada Kan Matatan Man Haifa Har Sau Biyu A Yakin Kwanaki 12
  • Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima Ya Isa Abidjan Wajen Rantsar da Shugaba Ouattara