Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a jihar Zamfara ta yi kakkausar suka ga gwamna Dauda Lawal kan kalaman da ta bayyana a matsayin bata gari dangane da kokarin gwamnatinsa na magance ‘yan fashi da makami da kuma bayar da tallafi ga wadanda ‘yan fashin suka kashe.

 

Hakan ya biyo bayan wani faifan bidiyo ne da aka ga gwamnan yana magana da manema labarai kan yadda gwamnatinsa ke tafiyar da harkokin tsaro da kuma jin dadin wadanda matsalar tsaro ta shafa.

 

A wata sanarwa da sakataren yada labaran jam’iyyar APC, Yusuf Idris Gusau ya fitar, ya bayyana kalaman gwamnan a matsayin rashin gaskiya da yaudara.

 

Malam Idris Yusuf Gusau ya yi zargin cewa, gwamnatin ta gaza cika wasu muhimman alkawuran yakin neman zabe, musamman alkawarin kawo karshen ‘yan fashi da makami a cikin watanni biyun farko da fara aiki.

 

Sanarwar ta kara da cewa “Gwamna Lawal da alama yana shirin cika shekara biyu a kan karagar mulki ba tare da samun wani ci gaba mai ma’ana ba kan babban alkawarin da ya yi a yakin neman zabe, maimakon a samu ci gaba, matsalar tsaro ta ta’azzara a Zamfara.”

 

A cewar Yusuf Idris, kalaman gwamna Lawal na baya-bayan nan a babban asibitin Gusau sun nuna rashin tausayi da jin kai.

 

“Jam’iyyar ta kuma zargi gwamnan da yin watsi da wadanda harin ya rutsa da su. “Maimakon ya ziyarci al’ummomin da ‘yan bindiga suka lalata ko aika sahihan tawaga don jajantawa da bayar da goyon baya, Gwamna Lawal ya zabi tafiya daga wata jiha ko kasa zuwa wata, yana jin dadin abokansa da ‘yan uwa yayin da mutanensa ke shan wahala.”

 

Ya yi nuni da cewa, babban abin da ya jawo cece-kuce shi ne ikirarin da gwamnan ya yi na cewa wadanda suka samu raunukan harbin bindiga suna karbar magani kyauta a asibitin kwararru na Yariman Bakura da cibiyar kula da lafiya ta tarayya da ke Gusau.

 

“Wannan karya ce kawai,” in ji Idris. “A makonnin da suka gabata ni da kaina na ga wadanda lamarin ya rutsa da su an mayar da su asibitin Yariman Bakura saboda rashin kudi, abin takaici wasun su sun mutu sakamakon haka, ba tare da taimakon gwamnati ba.”

 

Jam’iyyar APC ta yi kira ga gwamnan da ya fito fili ya bayyana sunaye, al’ummomi, da bayanan kula da wadanda suka ci gajiyar da aka ce sun samu kulawa kyauta, ciki har da kudaden da aka kashe da kuma kudaden da suka dace ko kuma bayanan biyan su.

 

Kakakin jam’iyyar APC ya kuma bukaci Gwamnan da mahukuntan asibitocin biyu da su buga cikakkun bayanai na jinya kyauta da aka yi a karkashin gwamnatinsa.”

 

Jam’iyyar ta kuma bukaci ‘yan jaridan da suka gudanar da hirar da su tabbatar da ikirarin gwamnan tare da zurfafa bincike kan al’amuran da abin ya shafa a lunguna da sako na jihar, kamar karamar hukumar Tsafe, wadanda ba za su iya samun kayan aiki a Gusau ba.

 

REL/AMINU DALHATU.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

A lokacin da yake jawabi a wurin ƙaddamarwar, Gwamna Lawal ya bayyana cewa da hawansa mulki a watan Mayun 2023, ya ci karo da tsarin kiwon lafiya da ya tabarbare saboda rashin kulawa.

Ya ce, “Gwamnatinmu, ƙarƙashin ginshiƙan shirye-shiryen ceto, nan da nan ta fara tantance abubuwan da asibitoci ke buƙata, inda sakamakon ya zama abin tsoro kuma ya nuna akwai jan-aiki.

“Alal misali, a jihar da ke da mutane kusan miliyan 6 tare da tarin ƙalubale, na’urar duban ɗan tayi ɗaya ce kawai a cikin dukkan cibiyoyin da gwamnati ta mallaka, kuma shi ma duk faci ne a jikinsa da salataf ko’ina! Nan take na ayyana dokar ta-baci a bangaren kiwon lafiya don dawo da ababen more rayuwa, samar da kayan aiki a asibitocinmu tare da samar da kwarin gwiwa da horarwa ga ƙwararru a fannin kiwon lafiya.

“Don inganta ayyukan more rayuwa, mun kuma ba da kwangilar samar da kayayyaki, sakawa, gwadawa, da horar da ma’aikata kan yadda za su yi amfani da na’urorin na zamani.

“Kamar yadda aka saba a wannan gwamnati ta Jihar Zamfara, muna tabbatar da cewa duk kayan aikin da aka kawo da kuma sanya su sun kasance masu inganci kuma sun cika ƙa’idojin da ake da su.

“Bari in jaddada cewa wannan ƙaddamarwar wani bangare ne na sake fasalin jihar Zamfara bakiɗaya a fannin kiwon lafiya, za ku iya tuna cewa mun riga mun samar da manyan asibitocin da aka gyara a garuruwan Ƙaura, Maradun, Maru, da Nasarawa Burkullu.

“Har ila yau, ana shirin ƙaddamar da wasu muhimman asibitocin da suka haɗa da Asibitin Ƙwararru na Ahmad Sani Yariman Bakura, Gusau, Babban Asibitin Talata Mafara, Shinkafi, da Babban Asibitin Tsafe, da dai sauransu.

“Bugu da ƙari, bayan amincewar majalisar zartarwa ta jiha, Ma’aikatar Lafiya ta fara aikin samar da cikakken kayan aiki ga manyan asibitocin da ke Anka, kuma wannan ya haɗa da samar da kayan aiki na zamani tare da horar da ma’aikatan kiwon lafiya.

“Ya ku ’yan uwa maza da mata, waɗannan ayyukan suna nuna hangen nesan mu na gina tsarin kiwon lafiya na zamani, mai aiki da kuma ɗorewa wanda zai rage yawan tura marasa lafiya zuwa wasu asibitoci a wajen jihar tare da tabbatar da cewa ’yan jihar mu sun sami ingantaccen kulawa kusa da gida.

“Yayin da muke murnar wannan nasarar, ina so in jawo hankalin mahukuntan asibitin kan buƙatar yin taka-tsan-tsan wajen amfani da kuma kula da wannan wuri.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zulum ya roƙi Gwamnatin Tarayya ta kai wa Marte ɗauki
  • Mawaƙan APC sun zargi gwamnatin Jigawa da yin watsi da su
  • Mawaƙan APC sun zargi gwamnati da watsi da su a Jigawa
  • Gwamnan Kano Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Tsaro
  • Hajji: Gwamnan Gombe ya yi bankwana da maniyyata 966, ya bai wa kowa kyautar Riyal 200
  • Hajji: Gwamnan Gombe ya yi bankwana da maniyyata 966, ya ba su kyautar Riyal 200
  • Gwamna Abdulrazaq Ya Jajanta Wa Wadanda Hatsarin Jirgin Ruwan Gbajibo Ya Rutsa Da Su
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 15 Sun Raunata 3 A Jihar Kebbi
  • Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara