APC Ta Zargi Gwamnan Zamfara Da Shirga Karya Tare Da Kiran Ya Nemi Afuwar Zamfarawa
Published: 19th, May 2025 GMT
Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a jihar Zamfara ta yi kakkausar suka ga gwamna Dauda Lawal kan kalaman da ta bayyana a matsayin bata gari dangane da kokarin gwamnatinsa na magance ‘yan fashi da makami da kuma bayar da tallafi ga wadanda ‘yan fashin suka kashe.
Hakan ya biyo bayan wani faifan bidiyo ne da aka ga gwamnan yana magana da manema labarai kan yadda gwamnatinsa ke tafiyar da harkokin tsaro da kuma jin dadin wadanda matsalar tsaro ta shafa.
A wata sanarwa da sakataren yada labaran jam’iyyar APC, Yusuf Idris Gusau ya fitar, ya bayyana kalaman gwamnan a matsayin rashin gaskiya da yaudara.
Malam Idris Yusuf Gusau ya yi zargin cewa, gwamnatin ta gaza cika wasu muhimman alkawuran yakin neman zabe, musamman alkawarin kawo karshen ‘yan fashi da makami a cikin watanni biyun farko da fara aiki.
Sanarwar ta kara da cewa “Gwamna Lawal da alama yana shirin cika shekara biyu a kan karagar mulki ba tare da samun wani ci gaba mai ma’ana ba kan babban alkawarin da ya yi a yakin neman zabe, maimakon a samu ci gaba, matsalar tsaro ta ta’azzara a Zamfara.”
A cewar Yusuf Idris, kalaman gwamna Lawal na baya-bayan nan a babban asibitin Gusau sun nuna rashin tausayi da jin kai.
“Jam’iyyar ta kuma zargi gwamnan da yin watsi da wadanda harin ya rutsa da su. “Maimakon ya ziyarci al’ummomin da ‘yan bindiga suka lalata ko aika sahihan tawaga don jajantawa da bayar da goyon baya, Gwamna Lawal ya zabi tafiya daga wata jiha ko kasa zuwa wata, yana jin dadin abokansa da ‘yan uwa yayin da mutanensa ke shan wahala.”
Ya yi nuni da cewa, babban abin da ya jawo cece-kuce shi ne ikirarin da gwamnan ya yi na cewa wadanda suka samu raunukan harbin bindiga suna karbar magani kyauta a asibitin kwararru na Yariman Bakura da cibiyar kula da lafiya ta tarayya da ke Gusau.
“Wannan karya ce kawai,” in ji Idris. “A makonnin da suka gabata ni da kaina na ga wadanda lamarin ya rutsa da su an mayar da su asibitin Yariman Bakura saboda rashin kudi, abin takaici wasun su sun mutu sakamakon haka, ba tare da taimakon gwamnati ba.”
Jam’iyyar APC ta yi kira ga gwamnan da ya fito fili ya bayyana sunaye, al’ummomi, da bayanan kula da wadanda suka ci gajiyar da aka ce sun samu kulawa kyauta, ciki har da kudaden da aka kashe da kuma kudaden da suka dace ko kuma bayanan biyan su.
Kakakin jam’iyyar APC ya kuma bukaci Gwamnan da mahukuntan asibitocin biyu da su buga cikakkun bayanai na jinya kyauta da aka yi a karkashin gwamnatinsa.”
Jam’iyyar ta kuma bukaci ‘yan jaridan da suka gudanar da hirar da su tabbatar da ikirarin gwamnan tare da zurfafa bincike kan al’amuran da abin ya shafa a lunguna da sako na jihar, kamar karamar hukumar Tsafe, wadanda ba za su iya samun kayan aiki a Gusau ba.
REL/AMINU DALHATU.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Dinkin Duniya Ta Fitar Da Rahoton Wadanda Suke Taimakawa ‘Yan Sahayoniyya Wajen Murkushe Falasdinawa
Rahoton Majalisar Dinkin Duniya mai ban tsoro ya bayyana cewa: Manyan kamfanoni suna da hannu wajen aiwatar da kisan kare dangi a Gaza
Wani rahoto da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar ya bayyana sunayen wasu manyan kamfanoni na duniya sama da 60 da ke da hannu a tallafawa wajen gine-ginen matsugunan yahudawa ‘yan kaka gida a yankunan gabar yammacin kogin Jordan da kuma hare-haren wuce gona da iri kan Zirin Gaza.
Rahoton wanda wakiliyar Majalisar Dinkin Duniya na musamman kan halin da ake ciki na kare hakkin bil adama a yankunan Falasdinawa da aka mamaye, Francesca Albanese, ta wallafa ya samo asali ne daga bayanai sama da 200 daga kasashe, kungiyoyin kare hakkin bil adama, masana ilimi da kamfanoni. Ta yi kira ga kamfanonin da su daina kasuwanci da haramtacciyar kasar Isra’ila, ta kuma yi tambayar cewa saboda rike harkokin gudanarwar kudade da kuma doka da oda don fa’idarsu da suke samu daga hare-haren da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke kai wa yankunan Falasdinawa.
Daga cikin kamfanonin da aka ambata a cikin rahoton, mafiya shahararsu akwai kamfanonin Amurka: Google, Microsoft, IBM, Caterpillar, a heavy equipment manufacturer, Lockheed Martin, a military manufacturer, da Hyundai na kasar Koriya ta Kudu. Rahoton ya zarge su da hannu a ayyukan danniya, kera makamai, da lalata dukiyoyi a yankunan Falasdinu.
Rahoton yana wakiltar fadada jerin sunayen da aka baiwa Majalisar Dinkin Duniya a shekara ta 2023 wanda ya mayar da hankali kawai kan kamfanonin da ke da alaka gwamnatin mamaya, yayin da sabon rahoton ya kunshi bangarori masu fadi da ke da alaka da cin zarafi a Gaza. Albanese ta gabatar da wannan zargi a cikin wani cikakken bayani game da rikicin Falasdinu: “Yayin da ake kashe rayuka a Gaza kuma ake ci gaba da kara kashe-kashen a gabar yammacin kogin Jordan, wannan rahoto ya nuna cewa kisan kiyashin da ake kira ya ci gaba ne kawai saboda yana da riba ga bangarori da yawa.”