Jami’in Sin: Ba Za A Lamunci Ayyukan ‘Yan Aware Na “Ballewar Taiwan” Ta Ko Wace Hanya Ba
Published: 15th, March 2025 GMT
Wani jami’in yada labarai na babban yankin kasar Sin ya bayyana a jiya Alhamis cewa, ba za a amince da duk wani mahaluki ko wata runduna da za ta raba yankin Taiwan da kasar Sin ba, kuma babu yadda za a yi a lamunce da ayyukan “ballewar Taiwan” ta ko wace hanya.
Jami’in yada labarun, da ke aiki a ofishin kula da harkokin Taiwan na majalisar gudanarwar kasar Sin, Chen Binhua ya kara da cewa, matukar dakarun ‘yan awaren suka kuskura suka bari tura ta kai bango, za a dauki kwararan matakan mayar da martani a kansu.
Chen ya bayyana hakan ne a lokacin da yake yin tir da kalaman jagoran ‘yan awaren Taiwan na baya-bayan nan, Lai Ching-te, wanda ya yi ikirarin cewa bangarori biyu na mashigin Taiwan ba su nuna biyayya ga junansu.
Da yake mayar da martani kan haka, Chen ya jaddada cewa, Taiwan wani yanki ne na kasar Sin da ba za a iya rabuwa da shi ba. Kana bai taba zama kasa ba kuma ba zai zama ba a gaba. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Nakiya ta hallaka yara 4 a Borno
Wata nakiya da ta fashe a garin Banki, da ke Ƙaramar Hukumar Bama, a Jihar Borno, ta yi sanadin mutuwar yara huɗu tare da jikkata wani yaro guda ɗaya.
Rundunar ’yan sandan jihar, ta tabbatar da aukuwar lamarin a ranar Juma’a.
Kwastam ta kama jirgin ruwan Brazil ɗauke da hodar iblis a Legas Ranar Sabuwar Shekara za mu rufe duk na’urar POS mara rajista —GwamnatiLamarin ya faru da misalin ƙarfe 12:40 na rana a bayan tashar motar Banki da ke yankin Wajari.
Wani mazaunin garin, Babagana Mohammed, ya kai rahoton fashewar nakiyar da misalin ƙarfe 1 na rana, wanda hakan ya sa aka tura jami’an tsaro zuwa yankin.
DPO na Banki tare da ƙwararrun sashen cire bam, sun killace wajen domin kare jama’a da kuma fara bincike.
An gano cewa wani yaro mai shekaru 12, Mustapha Tijja, ya samu munanan rauni, kuma an kai shi asibitin FHI 360 da ke Banki, inda ake kula da shi.
Rahotanni sun nuna cewa yaron da ya tsira da ransa, yana tare da abokansa huɗu a bayan tashar motar.
Sun samu wani abun fashewa da ake zargin ajiye shi aka yi a wajen, wanda ya fashe yayin da suke wasa da shi.
Yaran da suka rasu sun haɗa da Awana Mustapha mai shekaru 15, Malum Modu mai shekaru 14, Lawan Ibrahim mai shekaru 12 da Modu Abacha mai shekaru 12
Rundunar ’yan sandan jihar, ta ce al’amura sun daidaita a yankin, yayin da a gefe guda ta ke ci gaba da bincike.
Kwamishinan ’yan sandan Jihar, CP Naziru Abdulmajid, ya bayyana alhininsa kan faruwar lamarin, tare da bayyana cewa rundunar tana gudanar da bincike.
Ya gargaɗi jama’a cewa: “A guji taɓa ko wasa da duk wani abu da ba a saba gani ba. Duk abun da ake zargi, a gaggauta sanar da jami’an tsaro.”
Rundunar ta bayyana lambobin kiran gaggawa da jama’a za su yi amfani da su don kai rahoto: 0806 807 5581 da 0802 347 3293.
Kakakin rundunar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya ce rundunar za ta ci gaba da aiki tuƙuru wajen tabbatar da tsaro da hana irin waɗannan abubuwan faruwa a gaba.