Jami’in Sin: Ba Za A Lamunci Ayyukan ‘Yan Aware Na “Ballewar Taiwan” Ta Ko Wace Hanya Ba
Published: 15th, March 2025 GMT
Wani jami’in yada labarai na babban yankin kasar Sin ya bayyana a jiya Alhamis cewa, ba za a amince da duk wani mahaluki ko wata runduna da za ta raba yankin Taiwan da kasar Sin ba, kuma babu yadda za a yi a lamunce da ayyukan “ballewar Taiwan” ta ko wace hanya.
Jami’in yada labarun, da ke aiki a ofishin kula da harkokin Taiwan na majalisar gudanarwar kasar Sin, Chen Binhua ya kara da cewa, matukar dakarun ‘yan awaren suka kuskura suka bari tura ta kai bango, za a dauki kwararan matakan mayar da martani a kansu.
Chen ya bayyana hakan ne a lokacin da yake yin tir da kalaman jagoran ‘yan awaren Taiwan na baya-bayan nan, Lai Ching-te, wanda ya yi ikirarin cewa bangarori biyu na mashigin Taiwan ba su nuna biyayya ga junansu.
Da yake mayar da martani kan haka, Chen ya jaddada cewa, Taiwan wani yanki ne na kasar Sin da ba za a iya rabuwa da shi ba. Kana bai taba zama kasa ba kuma ba zai zama ba a gaba. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
An kashe mai ciki da ɗanta a Kano
Al’ummar unguwar Sheka Sabuwar Gandu da ke Ƙaramar Hukumar Birni a Jihar Kano, sun shiga fargaba, bayan wasu da ba a san ko su waye ba, suka kashe wata mai ciki da ɗanta ɗan wata18 a duniya.
An tabbatar da faruwar lamarin da misalin ƙarfe 8 na dare, lokacin da mijin matar ya dawo gida daga aiki ya tarar ƙofar gidan a kulle.
Hafsan sojin ƙasa ya buƙaci sabbin dakaru su zama masu kishin ƙasa An kashe mutum 11 da jikkata wasu 29 a bikin Yahudawa a OstireliyaA cewar maƙwabtan matar, bayan mijin ya tambayi jama’a a unguwar, sai ya shiga gidan, inda ya tarar da gawar matarsa da ta ɗanta.
Daga nan ne al’ummar unguwar suka sanar da hukumomin tsaro.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin, shugaban jama’a aunguwar, Ahmad Sani, ya ce jama’a sun shiga firgici da tashin hankali matuƙa.
Ya koka da rashin tsaro a yankin, inda ya bayyana cewa duk da gina ofishin ’yan sanda a unguwar, har yanzu ba a turo jami’an tsaro da za su kula da shi ba.
“Dukkanin al’ummar unguwar sun shiga ruɗani. Ba a taɓa samun irin wannan abu ba. Muna cikin damuwa saboda babu jami’an tsaro a nan,” in ji shi.
Ya roƙi Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Kano, Ibrahim Adamu Bakori, da ya ɗauki matakin gaggawa wajen inganta tsaro a yankin domin hana sake faruwar hakan.
Da aka tuntuɓi kakakin rundunar ’yan sandan jihar, CSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce ba zai ce komai ba domin rundunar na gudanar da bincike.
A halin yanzu, mazauna yankin sun buƙaci hukumomin tsaro su gaggauta kamo waɗanda suka aikata laifin.