Taron Tehran ya bukaci tattaunawa cikin gaggawa kan kalubalen yankin
Published: 19th, May 2025 GMT
Manyan jami’ai daga kasashe da dama da ke halartar taron tattaunawa na Tehran sun yi kira da a tattauna domin tunkarar manyan al’amura a yankin.
Manyan jami’ai daga kasashe 53 da suka hada da ministoci da masana da ne ke halartar taron na kwanaki biyu.
Ministan harkokin wajen Oman Badr bin Hamad Al Busaidi ya ce a halin yanzu yankin yammacin Asiya na fuskantar kalubale da dama da ke bukatar tattaunawa cikin gaggawa.
A yayin jawabin nasa, Ministan harkokin wajen Oman ya bayyana matukar damuwarsa kan tashe-tashen hankula da kisan kiyashin da al’ummar Falasdinu ke fuskanta, yana mai bayyana wannan lamari a matsayin wani abin takaici a duniya.
A nasa bangaren, ministan harkokin wajen kasar Tajikistan ya jaddada bukatar yin tattaunawa mai ma’ana don tinkarar manyan matsalolin da duniya ke fuskanta.
Armeniya ta bakin sakatarenta na komitin sulhu Armen Grigoryan ta tabbatar da aniyar tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.
Shi kuwa tsohon firaministan kasar Iraki Adel Abdul-Mahdi ya bayyana matukar damuwarsa game da matsalar jin kai da kuma ci gaba da kisan kiyashi a zirin Gaza.
Ya yi Allah wadai da gazawar kasashen Larabawa da kungiyoyin kasa da kasa, wadanda a cewarsa, sun kasa dakile irin ta’asar da Isra’ila ke yi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Babban Sakataren Majalisar Tsaron Kasar Iran Ya Bayyana Cewa; Ba Zasu Amince Da Shiga Tsakanin Iran Da Iraki Ba
Babban sakataren majalisar kolin tsaron kasar Iran ya jaddada cewa: Ba zasu yarda wasu kasashe su shiga tsakanin Iran da Iraki ba
Yayin da yake magana game da rattaba hannu kan yarjejeniyar tsaro tsakanin Iran da Iraki, babban sakataren majalisar koli na tsaron kasar Iran Ali Larijani ya yi nuni da cewa: Bai kamata a bar kasashe uku su tsoma baki cikin fahimtar juna da tsaron da ke tsakanin kasashen biyu ba, ko kuma su yi amfani da yankin wata kasa a kan wata kasa.
Ali Larijani, sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran ya tattauna da shirin “Tehran-Tel Aviv” da aka watsa a gidan radiyo da talabijin na kasar Iran kan ziyararsa ta farko a wannan matsayi a kasashen Iraki da Lebanon, da kuma game da halin da yankin yake ciki, yana mai cewa: Babu shakka batutuwan yankin suna daga cikin muhimman batutuwan da suka shafi moriyar kasa da tsaron kasar Iran, kuma a hakikanin gaskiya al’amurran da suka shafi tsaron yankin sun ginu ne bisa dabarun da suka dace na tsarin Jamhuriyar Musulunci.
Larijani ya kara da cewa: Akwai wasu muhimman layuka ko hangen nesa guda biyu dangane da batun tsaron kasa, yana mai cewa: Wata ka’ida ta ce Amurka da Isra’ila suna bayyanawa a fili a yau cewa suna son zaman lafiya da karfin tsiya, wanda ke nufin ko dai a mika musu wuya ko kuma su kaddamar da yaki. Sakamakon wannan ra’ayi na neman dagula lamura a yankin da ake gani a aikace a kasar Siriya.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Bayyana Cewa: Tana Sanya Ido Kan Abin Da Ke Faruwa A Kudancin Caucasus Cikin Lura August 17, 2025 Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Jaddada Shirinsu Na Tunkarar Duk Wata Barazana August 17, 2025 Jaridar Wall Street Journal Ta Ce: Har Yanzu Isra’ila Na Ci Gaba Da Neman Wajen Da Zata Tura Falasdinawa Gudun Hijira August 17, 2025 Gwamnatin DR Kongo Ta Nuna Rashin Amincewarta Da Zabin Kenya Kan Wajen Da Zata Bude Karamin Ofishin Jakadancinta A Kasarta August 17, 2025 Amurka Ta Dakatar Da Bawa Falasdinawa A Gaza Visar Shiga kasar August 17, 2025 Isra’ila Ta Jefa Boma-Bomai Kan Tashar Samar Da Wutan Lantarki A Yemen August 17, 2025 Donal Trump Yana Goyon bayan Shawarar Putin Na Musayar Kasa Don Zaman Lafiya Da Ukraine August 17, 2025 Dubban Mutane Sun Yiwa Barikin Sojojin Sama A Burtaniya Kofar Rago Saboda Gaza August 17, 2025 Iran Ta Bada Agajin Gaggawa Ga Pakistan Bayan Ambaliyar Ruwa August 17, 2025 Shugaban Iran na Shirin fara wata muhimmiyar ziyara a Armenia da Belarus August 17, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci