Dangote Da NNPCL Sun Koma Teburin Tattaunawa Kan Cinikin Danyen Mai A Kan Naira
Published: 14th, March 2025 GMT
Takardar da aka yi nazari a karshen watan Janairu ta nuna cewa a watan Fabrairun 2025, an ware shirin samar da mai na kan naira zuwa jirgin dakon mai hudu ne kawai, rukuni hudu zalla, kuma a watan Maris, dakon man biyu ne kawai aka yi da ya kai ganga 950,000 (ganga miliyan 1.9 ga watan). Wannan yana wakiltar rabon ganga 61,290 a kowace rana kasa da makasudin 385,000 bpd a karkashin tsarin.
Karancin samun danyen mai ya tursasa wa matatar man Dangote garzaya wa kasashen waje domin neman danyen man. A baya-bayan nan kamfanin ya samu gangar danyen mai miliyan 12 daga Amurka.
Duk da dai har yanzu matatar Mai ta Dangote ba ta fito a hukumance ta yi bayani kan karewar yarjejeniyar cinikayyar danyen mai din ba, amma wata majiya daga matatar ya tabbatar da cewa zancen ya kare, sai dai majiyar ba ta ba da cikakken karin haske ba.
Sai dai, kakakin kamfanin NNPC, Olufemi Shoneye yayin da ke fashin karin haske kan batun karewar hada-hadar cinikin, inda ya ce, “Bar na fayyace wannan lamarin, daman an kulla yarjejeniya ce na watanni shida, ya danganci wadatar danyen mai, kuma zai kare ne a karshen watan Maris na 2025.
“Tattaunawa na ci gaba da gudanar kan yadda za a kulla sabuwar yarjejeniya.
“A karkashin wannan yarjejeniyar, NNPC ya samar da danyen mai sama da ganga miliyan 48 ga matatar Mai ta Dangote tun watan Oktoban 2024.
“A takaice, NNPC ya samar da danyen mai ganga miliyan 84 ga matatar tun lokacin da ta fara aiki a shekarar 2023.
“NNPC ya himma wajen samar da danyen mai ga matatun mai na cikin gida a bisa tsarin yarjejeniya da sharuddan da aka cimma,” ya shaida
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista
Ya ce Jihar Kurus Ribas ita ce ta farko a yankin kudu da ta shiga a dama da ita a harkar noman alkama, lamarin da ke nuni da gayar nasara wajen samar da abinci a kowani sassa na kasar nan.
Kyari ya kara da cewa shirin rabar da takin zamani ya taimaka wajen bunkasa samar da shinkafa zuwa tan 58,000, lamarin da ya bai wa gwamnatin tarayya sanya tallafi a bangaren rabar da shinkafa ga jihohin da ambaliyar ruwa ta shafa.
Ministan ya ce akwai bukatar kare masu amfani da kuma kayan da ake nomawa, “kaso 80 cikin 100 na abincinmu manoman cikin gida ne suka samar da su.”
A daidai gabar da ake hasashen adadin ‘yan Nijeriya zai kai miliyan 400 a nan da shekarar 2050, Kyari ya ce gwamnati ta dukufa wajen kyautata harkar noma da kuma samar wa matasa ayyukan yi a matsayin mataki mai dogon zango na samar da wadatar abincin.
Ya ce gwamnati na kuma kokarin gyara kadarorin da kasar ke da su kamar su taraktoci, da sauran muhimman kayan aiki domin kara bunkasa samar da abinci.
Ya kuma ce Nijeriya ta yi hadin gwiwa da kasar Belarus don samar da ayyukan hadaka da nufin kara yawan kayan da ake fitarwa.
Ministan ya yi gargadin cewa a guji amfani da injinan noma da gwamnati ta samar ba ta hanyoyin da suka dace ba, inda ya bukaci manoma da su yi amfani da irin wadannan kayan aikin yadda ya kamata.
Ministan ya ce warare uku na ajiyar kaya wato silo ne kawai suke aiki a halin yanzu, inda ya sha alwashin cewa za a maida hankali wajen gyara sauran.
Kyari ya ce “Ma’aikatar noma da dawata kasa da abinci za ta hada kai da masu ruwa da tsaki don tabbatar da an yi amfani da wadannan muhimman wuraren ajiyar kaya.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp