MC Tagwaye ya fice daga APC zuwa SDP
Published: 14th, March 2025 GMT
Fitaccen mai barkwancin nan wanda yake kwaiwayon maganganun tsohon Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari, Obinna Simon wanda aka fi sani da ‘MC Tagwaye’ wanda yake mai nishaɗantarwa, ɗan kasuwa, kuma ɗan siyasa ya sauya sheƙa daga Jam’iyyar APC zuwa SDP.
Ya sanar da hakan ne a cikin wani saƙon da ya wallafa a dandalin sada zumunta na zamani a ranar Juma’a, ya danganta sauya jam’iyyar ne bayan tuntuɓa da yin shawarwari.
“Bayan tsawon watanni na tuntuɓar juna, ni Obinna Simon da aka fi sani da MC Tagwaye, na yanke shawarar ficewa daga Jam’iyyar APC na koma SDP.”
“Wannan gagarumin mataki ya samo asali ne daga zurfafa tunani na cewa Jam’iyyar APC ta kauce daga aƙidarta na asali kuma ta daina sadaukar da kai ga jin daɗi da ci gaban al’ummar Nijeriya. Rashin tsarin da jam’iyyar ta yi na ba da lada ga membobinta masu aminci, tsarin shugabancinta da manufofinta da ke ci gaba da haddasa wahalhalu ga masu ƙaramin ƙarfi, suna cikin dalilai na sauya sheƙar.
“Duk da haka, dimokuraɗiyyar cikin gida ta APC ta taɓarɓare sosai, inda wasu ’yan ƙalilai masu madafun iko ke tafiyar da alƙiblar jam’iyyar tare da yin watsi da muryar mafi mafiya rinjaye.
“Saɓanin haka, Jam’iyyar SDP ta fito a matsayin ginshiƙin fata nagari, tare da sadaukar da kai ga matasa, dimokuraɗiyyar cikin gida, tabbatar da gaskiya da riƙon amana. Burin jam’iyyar ne na sabuwar Nijeriya, inda jin daɗin jama’a da ci gaban dukkan ‘yan ƙasa ke da muhimmanci sosai.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: MC Tagwaye Muhammadu Buhari
এছাড়াও পড়ুন:
Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu
Tsoffin ma’aikatan Hukumar Shirya Jarabawar (NECO), da suka yi ritaya na neman a biya su haƙƙoƙinsu da suke bin bashi.
Shugaban ƙungiyar tsofffin ma’aikatan, Dokta Abdullahi Rotimi Williams ne ya bayyana hakan a bikin ƙaddamar da hedikwatar kungiyar a Minna, babban birnin Neja.
Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta NijeriyaShugaban ya kuma koka kan yadda gwamnatin Nijeriya ta maida ritaya abin fargaba a wurin ma’aikata saboda tarin ƙalubalen da ke biyo bayan hakan, musamman maƙalewar haƙƙoƙinsu.
“Da yawa tsoron ritaya ake yi yanzu. Don haka wannan ƙungiyar za ta taimaka wajen rage waɗannan matsalolin.
“Babban ƙalubalen da muke fuskanta shi ne na lafiya. Don haka ina roƙon shugaban hukumar da ya tabbatar cewa daga yanzu an kammala shirye-shiryen da suka kamata kafin ma’aikacin NECO ya yi ritaya.”
Ya kuma ce duk da jagororin hukumar na yanzu sun biya wasu daga cikin haƙƙoƙin nasu, ba a kai ga biyan alawus ɗin ƙarin girma ba, da na tafiye-tafiye ba.