MC Tagwaye ya fice daga APC zuwa SDP
Published: 14th, March 2025 GMT
Fitaccen mai barkwancin nan wanda yake kwaiwayon maganganun tsohon Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari, Obinna Simon wanda aka fi sani da ‘MC Tagwaye’ wanda yake mai nishaɗantarwa, ɗan kasuwa, kuma ɗan siyasa ya sauya sheƙa daga Jam’iyyar APC zuwa SDP.
Ya sanar da hakan ne a cikin wani saƙon da ya wallafa a dandalin sada zumunta na zamani a ranar Juma’a, ya danganta sauya jam’iyyar ne bayan tuntuɓa da yin shawarwari.
“Bayan tsawon watanni na tuntuɓar juna, ni Obinna Simon da aka fi sani da MC Tagwaye, na yanke shawarar ficewa daga Jam’iyyar APC na koma SDP.”
“Wannan gagarumin mataki ya samo asali ne daga zurfafa tunani na cewa Jam’iyyar APC ta kauce daga aƙidarta na asali kuma ta daina sadaukar da kai ga jin daɗi da ci gaban al’ummar Nijeriya. Rashin tsarin da jam’iyyar ta yi na ba da lada ga membobinta masu aminci, tsarin shugabancinta da manufofinta da ke ci gaba da haddasa wahalhalu ga masu ƙaramin ƙarfi, suna cikin dalilai na sauya sheƙar.
“Duk da haka, dimokuraɗiyyar cikin gida ta APC ta taɓarɓare sosai, inda wasu ’yan ƙalilai masu madafun iko ke tafiyar da alƙiblar jam’iyyar tare da yin watsi da muryar mafi mafiya rinjaye.
“Saɓanin haka, Jam’iyyar SDP ta fito a matsayin ginshiƙin fata nagari, tare da sadaukar da kai ga matasa, dimokuraɗiyyar cikin gida, tabbatar da gaskiya da riƙon amana. Burin jam’iyyar ne na sabuwar Nijeriya, inda jin daɗin jama’a da ci gaban dukkan ‘yan ƙasa ke da muhimmanci sosai.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: MC Tagwaye Muhammadu Buhari
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
Dakarun Operation Haɗin Kai sun kama mut biyar da ake zargin suna taimaka wa ’yan ta’adda da kayan aiki.
Daga cikinsu har da wani ɗan ƙasar China da ya ce shi mai harkar ma’adinai ne.
Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin TarayyaAn kama su ne a lokacin kai wani samame da aka gudanar daga 5 zuwa 7 ga watan Yuni a ƙananan hukumomin Kukawa da Ngala na Jihar Borno, da kuma Geidam a Jihar Yobe.
A lokacin wannan aiki, dakarun sun ƙwato wasu kayayyaki da suka haɗa da mota, babur, wayoyin salula, fasfo na ƙasar China, da kuma kuɗi Naira 10,000.
Shugaban sashen yaɗa labaran tsaro, Manjo Janar Edward Markus Kangye, ya bayyana hakan a wata ganawa da manema labarai a Abuja.
Ya ce sojojin sun kuma kai farmaki wasu yankuna bisa bayanan sirri da suka samu, ciki har da Gwoza da Abadam a Borno da kuma Nangere a Yobe, daga 6 zuwa 9 ga watan Yuni.
Ya ƙara da cewa daga 6 zuwa 11 ga watan Yuni, wasu maza da mata da yara da dama sun miƙa wuya ga dakarun Najeriya.
Kangye ya bayyana cewa rundunar ta kuma kai wasu hare-hare tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro a Ngala, Marte, Gwoza a Jjihar Borno da Bade da Gujba a Jihar Yobe daga 6 zuwa 10 ga watan Yuni.
A wannan lokaci, sun lalata sansanonin ’yan ta’adda, sun ƙwato makamai da alburusai.
Manjo Janar Kangye ya ce sojojin Najeriya za su ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin ’yan ƙasa tare da tabbatar da doka da oda.
“Mun ƙudiri aniyar kare martabar Najeriya da tabbatar da zaman lafiya a kowane yanki na ƙasar nan. Wannan aiki namu na ci gaba da yin tasiri,” in ji shi.
Ya buƙaci haɗin kan jama’a wajen taimaka wa sojoji su ci gaba da yaƙi da ’yan ta’adda.
Ya ce idan jama’a da hukumomi suka haɗa kai, Najeriya za ta samu zama lafiya da wadata.
“Zamu ci gaba da sanar da al’umma duk wani ci gaba da muka samu wajen yaƙar ta’addanci,” in ji Kangye.