Aminiya:
2025-08-01@01:16:30 GMT

MC Tagwaye ya fice daga APC zuwa SDP

Published: 14th, March 2025 GMT

Fitaccen mai barkwancin nan wanda yake kwaiwayon maganganun tsohon Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari, Obinna Simon wanda aka fi sani da ‘MC Tagwaye’ wanda yake mai nishaɗantarwa, ɗan kasuwa, kuma ɗan siyasa ya sauya sheƙa daga Jam’iyyar APC zuwa SDP.

Ya sanar da hakan ne a cikin wani saƙon da ya wallafa a dandalin sada zumunta na zamani a ranar Juma’a, ya danganta sauya jam’iyyar ne bayan tuntuɓa da yin shawarwari.

Wata mata ta faɗa ruwa ta mutu a Legas Direba ya murƙushe yarinya ta mutu a artabu da jami’an tsaro a Edo

“Bayan tsawon watanni na tuntuɓar juna, ni Obinna Simon da aka fi sani da MC Tagwaye, na yanke shawarar ficewa daga Jam’iyyar APC na koma SDP.”

“Wannan gagarumin mataki ya samo asali ne daga zurfafa tunani na cewa Jam’iyyar APC ta kauce daga aƙidarta na asali kuma ta daina sadaukar da kai ga jin daɗi da ci gaban al’ummar Nijeriya. Rashin tsarin da jam’iyyar ta yi na ba da lada ga membobinta masu aminci, tsarin shugabancinta da manufofinta da ke ci gaba da haddasa wahalhalu ga masu ƙaramin ƙarfi, suna cikin dalilai na sauya sheƙar.

“Duk da haka, dimokuraɗiyyar cikin gida ta APC ta taɓarɓare sosai, inda wasu ’yan ƙalilai masu madafun iko ke tafiyar da alƙiblar jam’iyyar tare da yin watsi da muryar mafi mafiya rinjaye.

“Saɓanin haka, Jam’iyyar SDP ta fito a matsayin ginshiƙin fata nagari, tare da sadaukar da kai ga matasa, dimokuraɗiyyar cikin gida, tabbatar da gaskiya da riƙon amana. Burin jam’iyyar ne na sabuwar Nijeriya, inda jin daɗin jama’a da ci gaban dukkan ‘yan ƙasa ke da muhimmanci sosai.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: MC Tagwaye Muhammadu Buhari

এছাড়াও পড়ুন:

Remi Tinubu ta ba da tallafin Naira biliyan ɗaya ga waɗanda harin Benuwe ya shafa

Uwargidan Shugaban Nijeriya, Sanata Remi Tinubu ta bayar da tallafin naira biliyan daya ga wadanda harin nan ya rutsa da su a yankin Yelwata na Ƙaramar Hukumar Guma a Jihar Benuwe.

Sanata Tinubu wadda ta miƙa cakin kuɗin ga Gwamna Hyacinth Alia ta sanar da bayar da tallafin ne a jawabinta na jaje wanda ta kai Fadar Gwamnatin Benuwe da ke Makurdi.

Gwamnatin Zamfara ta amince da naɗin sabon Sarkin Katsinan Gusau Ambaliya ta yi ajalin mutum 30 a China

Uwargidan shugaban ƙasar ta buƙaci a yi amfani da wannan tallafin a matsayin gudunmawar farfaɗo da yankin da waɗanda suka tsallake rijiya da baya a yayin harin musamman yaran da yanzu ke buƙatar komawa makarantu.

Ana iya tuna cewa, tun a daren ranar 13 ga watan Yuni zuwa wayewar gari 14 ga watan ne aka kashe fiye da mutum 100 a ƙauyen Yelwata, lamarin da ya janyo Allah wadai daga sassa daban-daban a faɗin ƙasar.

Jihar Benuwe dai na daga cikin jihohin da ke fuskantar matsalar tsaro a Nijeriya, musamman rikicin manoma da makiyaya da kuma na ƙabilanci, wanda ke sanadiyyar salwantar rayuka da dama.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • INEC Ta Gudanar da Taron Masu Ruwa da Tsaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi na Babura/Garki
  • Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • 2027: Ba Mu Kafa Haɗakarmu Don Cika Burin Atiku Ba – ADC
  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah
  • Tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa har zuwa baɗi — IMF
  • Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana
  • Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya
  • Remi Tinubu ta ba da tallafin Naira biliyan ɗaya ga waɗanda harin Benuwe ya shafa