Gwamnatin jihar Kebbi ta jajanta wa al’ummar Waje da ke karamar hukumar Danko Wasagu sakamakon harin ‘yan bindiga da ya yi sanadin mutuwar manoma 15 tare da jikkata wasu 3.

 

Mataimakin gwamnan jihar, Sanata Umar Abubakar Tafida, ya mika sakon ta’aziyyar gwamnati tare da bayar da tallafin Naira miliyan 24 ga iyalan wadanda suka mutu da wadanda suka jikkata.

 

Ya bayyana hakan a matsayin kokarin da gwamnatin jihar ke yi na tallafawa iyalan wadanda suka mutu da wadanda suka jikkata a wannan lokaci mai cike da kalubale.

 

Sanata Abubakar, ya bayar da tabbacin cewa gwamnatin jihar za ta dauki matakan da suka dace don magance matsalar rashin tsaro, tare da baiwa manoma damar gudanar da ayyukansu cikin aminci.

 

Shugaban karamar hukumar Danko Wasagu, Alhaji Hussaini Aliyu Bena, ya tabbatar da cewa an kashe manoma 15 tare da jikkata wasu 3 a harin da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai.

 

Hakimin Waje, Alhaji Bala Danbaba, a lokacin da ya yaba wa gwamnatin jihar bisa wannan ziyarar da kuma tallafin kudi, ya bayyana cewa, iyakar Danko Wasagu da jihohin Neja, Zamfara da kuma Sokoto na haifar da matsala, inda ya yi kira da a kara inganta tsaro domin toshe wadannan hanyoyin shiga.

 

Abdullahi Tukur

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: wadanda suka

এছাড়াও পড়ুন:

Fiye Da Falasdinawa 300 Ne Su Ka Yi Shahada Da Jikkata Daga Safiyar Yau Juma’a

HKI tana ci gaba da yi wa Falasdinawa kisan kiyashi a  Gaza wanda ya ci rayukan Falasdiniwa  kusan 300 da su ka hada kananan yara da mata.

Tashar talabijin din ‘almayadin’ ta ambaci cewa;Tun da asubahin yau ne dai sojojin mamayar su ka fara kai wadannan munanan hare-haren wanda ba komai ba ne, sai kisan kiyashi akan Falasdinawada suke fama da matsananciyar yunwa saboda rashin abinci.

Bugu da kari, mafi yawancin Falasdinawan da HKI take kai wa hare-haren suna rayuwa ne a cikin hemomi bayan da ta rushe musu gidajensu.

Ma’aikatar kiwon lafiya ta Falasdinu ta sanar a cewa; A cikin sa’oi 24 da su ka gabata, adadin wadanda su ka yi shahada sun kai 109, kuma tuni an fito da gawawwakinsu daga gine-gine da hemomin da su ka fada a kansu, yayin da wasu 216 su ka jikkata.

A jiya kadai, adadin Falasdinawan da su ka yi shahada sun haura 100. Baya ga wadanda su ka yi shahadar, da akwai kuma wani adadi na falasdinawa da ya kai 100 da sun bace.

Daga 7 ga watan Oktoba na 2023 zuwa yanzu, adadin Falasdinawan da su ka yi shahada sun kai dubu 53, da 119, sai kuma wadanda su ka jikkata da sun kai 120,114.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutane 7 Sun Mutu 11Sun Jikkata A Hadarin Mota A Niger.
  • Boko Haram ta kashe manoma 90 a Borno cikin wata 5
  • Hajji: Gwamnatin Katsina ta biya wa maniyyata 2000 kuɗin hadaya
  • ’Yan sanda sun ceto tsohuwa mai shekara 80 a hannun ’yan bindiga a Jigawa
  • Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara
  • Mutum 5 sun jikkata yayin da gidan mai ya ƙone ƙurmus a Ribas
  • Fiye Da Falasdinawa 300 Ne Su Ka Yi Shahada Da Jikkata Daga Safiyar Yau Juma’a
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga da ƙwato shanun sata 1000 a Taraba 
  • Gwamnatin Katsina za ta gina birnin dawakai na farko a Afirka