Leadership News Hausa:
2025-07-01@10:15:05 GMT

Majalisa Za Ta Binciki INEC Kan Jinkirin Gudanar Da Zaben Cike Gurbi

Published: 28th, February 2025 GMT

Majalisa Za Ta Binciki INEC Kan Jinkirin Gudanar Da Zaben Cike Gurbi

Ya kara da cewa rashin gudunar da daga wurin INEC abu ne mai hadari, wanda ya saba wa dokokin tsarin mulki da dokoki wadanda suka tilas zaben cike gurbi a duk lokacin da aka samu bukatan hakan.

Rahotanni sun bayyana cewa a halin yanzu akwai kujeru bakwai a majalisar kasar nan da babu kowa, akwar biyar a majalisar wakilai, sannan akwai biyu a majalisar dattawa.

Kujerun da babu kowa a majalisar wakilai akwai a jihohin Edo da Oyo da Kaduna da Ogun da kuma Jigawa, yayin da kujerun majalisar dattawan na jihohin Edo da Anambra.

Biyu daga cikin wadannan kujeru sun zama babu kowa ne bayan zaben gwamnan a Jihar Edo, yayin da sauran biyar suka zama babu kowa saboda mutuwar ‘yan majalisa.

Gwamnan Jihar Edo, Monday Okpebolo da mataimakinsa, Denis Idahosa, sun kasance ‘yan majalisar tarayya da ke wakiltar Edo ta tsakiya a majalisar dattawa da kuma mazabar tarayya ta Obia a majalisar.

Sauran kujerun da ba su da kowa sun hada da na marigayi Sanata Ifeanyi Ubah (Anambra South), Isa Dogonyaro (Jigawa), Ekene Abubakar Adams (Kaduna), Olaide Akinremi (Oyo) da Adewunmi Oriyomi Onanuga (Ogun).

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: a majalisar

এছাড়াও পড়ুন:

Babu wanda zai manta da gudunmawar da Wike ya ba ni — Fubara

Gwamnan Jihar Ribas, Siminalayi Fubara, ya ce zai iya yin komai muddin hakan zai kawo zaman lafiya da ci gaba a jiharsa.

Fubara, ya faɗi haka ne a garin Fatakwal a ranar Asabar, yayin da yake magana da magoya bayansa.

An samu amincewar yi wa Dantata jana’iza a Madina Van Nistelrooy ya ajiye aikin horas da Leicester City

Ya tabbatar musu cewa ya sasanta da Tsohon Gwamnan jihar, wanda a yanzu Ministan Abuja ne, Nyesom Wike.

Ya ce ya san wasu daga cikin magoya bayansa ba za su ji daɗin sasancin da aka yi ba, amma ya roƙe su da su yi haƙuri.

Ya ce: “Wani lokaci sai an ɗauki matakai masu wahala domin a samu gyara.”

Ya ƙara da cewa: “Kowa ya san mun yi iya ƙoƙarinmu. Amma yanzu abin da muke buƙata shi ne zaman lafiya.”

Fubara ya ce ba wanda zai iya musanta irin taimakon da Wike ya masa.

“E, mun samu saɓani a wasu abubuwa, amma ba za a iya cewa Wike bai taka rawar gani ba.

“Duk wanda ke sona da gaskiya, ya daina magana, lokaci ne na zaman lafiya.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zan yi takara a Zaɓen 2027 — Peter Obi
  • Iran Ta Bukaci Gudanar Da Bincike Kan Dalilin Isra’ila Na Kai Harin Kan Gidan Yarin Tehran
  • An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata
  • APC ta sa ranar taron Majalisar Zartarwa bayan murabus ɗin Ganduje
  • Jami’an tsaro sun tarwatsa taron kwamitin amintattun PDP
  • Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
  • Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya
  • Babu wanda zai manta da gudunmawar da Wike ya ba ni — Fubara
  • Yadda na hannun daman ’Yar’Adua ya yi tuggun hana ni zama shugaban ƙasa — Jonathan 
  • Jakadan Iran A Majalisar Dinkin Duniya Ya Jaddada Cewa: Iran Tana Da Hakkin Tace Sinadarin Uranium A Kasarta