Aminiya:
2025-11-08@16:37:40 GMT

An ɗaure mutum 6 shekaru 120 kan satar yara a Kano

Published: 25th, June 2025 GMT

Wata Babbar Kotu a Jihar Kano, ta yanke wa wasu mutum shida hukuncin zaman gidan yari na tsawon shekaru 120, bisa samun su da laifin satar yara da kuma sayar da su.

Mutanen da aka yanke wa hukuncin sun haɗa da Mercy Paul, Ebere Ogbono, Emmanuel Igwe, Loise Duru, Monica Oracha, da Chinelo Ifedigwe.

PDP ta mayar wa da na hannun damar Wike kujerarsa ta sakatarenta PDP ta mayar wa da na hannun damar Wike kujerarsa ta sakatarenta

An same su da laifin ɓoye bayanai, taimakawa wajen aikata laifi, satar yara da kuma safarar su.

An sace yaran ne daga Kano, sannan aka sayar da su a garin Onitsha da ke Jihar Anambra.

Shugaban tawagar, Paul Onwe, tuni aka yanke masa hukuncin ɗaurin shekaru 104 a gidan yari a watan Yulin 2021, bayan ya amsa laifuka 38 da ake zarginsa da aikatawa.

Amma sauran mutanen shida sun musanta laifin, shi ya sa aka gurfanar da su a gaban kotu domin shari’a.

Alƙalin da ta jagoranci shari’ar, Mai Shari’a Zuwaira Yusuf, ta ce an same su da laifi kuma ta yanke musu hukunci daban-daban ba tare da zaɓin biyan tara ba.

Mercy Paul ta samu hukuncin ɗaurin shekaru 55 a gidan yari, Ebere Ogbono shekaru 41, Emmanuel Igwe shekaru tara, Loise Duru shekaru shida, Monica Oracha shekaru biyar, sai Chinelo Ifedigwe shekaru tara.

An kama su ne tun a shekarar 2019.

Bayan shekaru shida ana shari’a, an kammala shari’ar.

Wannan lamari ya jawo hankalin jama’a sosai tare da nuna irin hatsarin safarar yara da ke ƙara yawaita a Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Safara satar yara

এছাড়াও পড়ুন:

Matsalar Tsaro: Mun samu gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa, gwamnatinsa ta samu ci gaba sosai wajen magance matsalar rashin tsaro a faɗin ƙasar cikin shekaru biyu da suka gabata.

Shugaban ya kuma jaddada aniyar gwamnatinsa na daƙile ayyukan ta’addanci da kuma tabbatar da zaman lafiyar ƙasa.

Ɗan shekara 2 ya rasu bayan faɗawa rijiya a Kano An gano gawar wata mai shekara 96 a cikin masai

A wata sanarwa da Tinubu ya fitar a shafinsa na sada zumunta, a ranar Juma’a, ya ce ƙalubalen tsaro a Najeriya, da suka haɗa da ta’addanci da aikata laifuka, ana magance su da sabbin tsari da sauye-sauyen dabarun dawo da zaman lafiya a faɗin ƙasar.

“Haƙiƙa muna fuskantar ta’addanci – ƙalubalen da Najeriya ta fuskanta kusan shekaru ashirin, kuma ba za mu ja da baya ba, za mu yi nasara a kan ta’addanci kuma mu yi iƙirarin samun nasara a wannan yaƙin, ba za mu taɓa yin sulhu harkar tsaro ba.

“Najeriya ƙasa ɗaya ce mai haɗin kai, mun tashi tare, mun ci gaba tare, kuma mun ƙi yanke ƙauna domin tabbatar da ƙuduri.

“Aikin da ke gabanmu yana da yawa, amma duk da haka ƙudurinmu ya fi girma, za mu ci gaba da ɗorewa tare da inganta nasarorin da muka samu na sake fasalin ƙasa da kuma samar da ci gaba a Najeriya.

“Ba za mu yi ƙasa a gwiwa ba kuma ba za mu bar wani abu ba a cikin aikinmu na kawar da masu aikata laifuka a cikin al’ummarmu, muna kira ga abokan haɗin gwiwarmu da su tsaya tsayin daka tare da mu yayin da muke ƙara faɗaɗa yaƙin da muke yi da ta’addanci, mun samu gagarumin ci gaba a cikin shekaru biyu da suka gabata, kuma za mu kawar da wannan barazana.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta
  • Matsalar Tsaro: Mun samu gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
  • Ma’aikacin jinya ya kashe marasa lafiya 10 saboda aiki ya masa yawa
  • Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru
  • An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano
  • An rantsar da shugaban Kamaru Paul Biya karo na 8
  • Kwalara ta kashe mutum 10 a Ƙaramar Hukumar Adamawa
  • An kama mutum 2 kan sukar shugaban karamar hukuma a Kano
  • An amince da hukuncin yi wa malamai ɗaurin shekara 14 kan lalata da ɗalibai
  • Yara biyu sun mutu bayan faɗawa rijiya a Kano