An ɗaure mutum 6 shekaru 120 kan satar yara a Kano
Published: 25th, June 2025 GMT
Wata Babbar Kotu a Jihar Kano, ta yanke wa wasu mutum shida hukuncin zaman gidan yari na tsawon shekaru 120, bisa samun su da laifin satar yara da kuma sayar da su.
Mutanen da aka yanke wa hukuncin sun haɗa da Mercy Paul, Ebere Ogbono, Emmanuel Igwe, Loise Duru, Monica Oracha, da Chinelo Ifedigwe.
PDP ta mayar wa da na hannun damar Wike kujerarsa ta sakatarenta PDP ta mayar wa da na hannun damar Wike kujerarsa ta sakatarentaAn same su da laifin ɓoye bayanai, taimakawa wajen aikata laifi, satar yara da kuma safarar su.
An sace yaran ne daga Kano, sannan aka sayar da su a garin Onitsha da ke Jihar Anambra.
Shugaban tawagar, Paul Onwe, tuni aka yanke masa hukuncin ɗaurin shekaru 104 a gidan yari a watan Yulin 2021, bayan ya amsa laifuka 38 da ake zarginsa da aikatawa.
Amma sauran mutanen shida sun musanta laifin, shi ya sa aka gurfanar da su a gaban kotu domin shari’a.
Alƙalin da ta jagoranci shari’ar, Mai Shari’a Zuwaira Yusuf, ta ce an same su da laifi kuma ta yanke musu hukunci daban-daban ba tare da zaɓin biyan tara ba.
Mercy Paul ta samu hukuncin ɗaurin shekaru 55 a gidan yari, Ebere Ogbono shekaru 41, Emmanuel Igwe shekaru tara, Loise Duru shekaru shida, Monica Oracha shekaru biyar, sai Chinelo Ifedigwe shekaru tara.
An kama su ne tun a shekarar 2019.
Bayan shekaru shida ana shari’a, an kammala shari’ar.
Wannan lamari ya jawo hankalin jama’a sosai tare da nuna irin hatsarin safarar yara da ke ƙara yawaita a Najeriya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Safara satar yara
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun kama mutum 4 kan kai wa Lakurawa babura a Kebbi
Rundunar ’Yan sandan Jihar Kebbi ta cafke wasu mutum huɗu a yankin Kamba da ke jihar, bisa zargin su da shigar da babura uku da suka saya daga Jamhuriyar Benin domin kai wa kungiyar ta’addanci ta Lakurawa.
Haka kuma an kama wani Mubarak Ladan bayan ya yi tayin cin hancin naira dubu dari shida (₦600,000) ga DPO na Kamba, SP Bello Mohammad Lawal, domin a saki waɗanda aka kama.
Kakakin rundunar ’yan sanda ta jihar, CSP Nafiu Abubakar, ya ce baburan da ake kira “Boko Haram” guda uku an saye su ne kan kudi naira miliyan 5 da dubu 400, kuma an tanadar da su ne domin kai wa kungiyar Lakurawa ta hannun wani Alhaji da ke a Kangiwa.
Sanarwar ta ƙara da cewa an cafke mutanen ne bayan samun sahihan bayanai, inda jami’an ’yan sanda tare da ’yan sa-kai ƙarƙashin jagorancin DPO na Kamba suka kai samame
Kwamishinan ’Yan sandan Jihar Kebbi, Bello M. Sani, ya umurci Mataimakin Kwamishina na Sashen Binciken Manyan Laifuka (SCID), Birnin Kebbi, da ya bi sahun sauran waɗanda suka tsere a lamarin