Aminiya:
2025-06-25@20:25:16 GMT

An ɗaure mutum 6 shekaru 120 kan satar yara a Kano

Published: 25th, June 2025 GMT

Wata Babbar Kotu a Jihar Kano, ta yanke wa wasu mutum shida hukuncin zaman gidan yari na tsawon shekaru 120, bisa samun su da laifin satar yara da kuma sayar da su.

Mutanen da aka yanke wa hukuncin sun haɗa da Mercy Paul, Ebere Ogbono, Emmanuel Igwe, Loise Duru, Monica Oracha, da Chinelo Ifedigwe.

PDP ta mayar wa da na hannun damar Wike kujerarsa ta sakatarenta PDP ta mayar wa da na hannun damar Wike kujerarsa ta sakatarenta

An same su da laifin ɓoye bayanai, taimakawa wajen aikata laifi, satar yara da kuma safarar su.

An sace yaran ne daga Kano, sannan aka sayar da su a garin Onitsha da ke Jihar Anambra.

Shugaban tawagar, Paul Onwe, tuni aka yanke masa hukuncin ɗaurin shekaru 104 a gidan yari a watan Yulin 2021, bayan ya amsa laifuka 38 da ake zarginsa da aikatawa.

Amma sauran mutanen shida sun musanta laifin, shi ya sa aka gurfanar da su a gaban kotu domin shari’a.

Alƙalin da ta jagoranci shari’ar, Mai Shari’a Zuwaira Yusuf, ta ce an same su da laifi kuma ta yanke musu hukunci daban-daban ba tare da zaɓin biyan tara ba.

Mercy Paul ta samu hukuncin ɗaurin shekaru 55 a gidan yari, Ebere Ogbono shekaru 41, Emmanuel Igwe shekaru tara, Loise Duru shekaru shida, Monica Oracha shekaru biyar, sai Chinelo Ifedigwe shekaru tara.

An kama su ne tun a shekarar 2019.

Bayan shekaru shida ana shari’a, an kammala shari’ar.

Wannan lamari ya jawo hankalin jama’a sosai tare da nuna irin hatsarin safarar yara da ke ƙara yawaita a Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Safara satar yara

এছাড়াও পড়ুন:

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

Haɗin gwiwar NAFDAC da sashen bincike da aiwatar da dokokinta ne ya kai ga kama waɗanda ake zargi tare da rufe shagunan da suka shafa, da ɗaukar samfurin mayukan domin gwaji a ɗakin bincike.

Haka kuma, an rufe wasu kamfanonin da ke kwaikwayon kayayyakin da aka yi wa rijista ko suke karya ƙa’idodin NAFDAC, har sai an kammala bincike.

Ibrahim ya roƙi jama’a da su kasance masu lura da duk wani abu da ya saɓa wa doka kuma su riƙa sanar da hukumar nan take.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano
  • Iran ta kama ’yan leƙen asirin Isra’ila 6
  • Iyalan Kanawa da aka kashe a Uromi sun zargin gwamnati da yin watsi da su
  • An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato – Uba Sani
  • Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana
  • EFCC Ta Kama Tsohon Babban Jami’in NNPC Kan Zargin Satar Dala Biliyan 7.2
  • Mutum 2 sun mutu a ƙoƙarin ciro waya daga masai a Kano
  • Mutum 2 sun mutum a ƙoƙarin ciro wata daga masai a Kano
  • Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan