Aminiya:
2025-08-12@05:57:20 GMT

Bom ya kashe mutum hudu da raunata 21 a Yobe

Published: 28th, June 2025 GMT

A ranar Juma’ar nan ne wasu abubuwa da ake kyautata zaton bom ne ya kashe mutane huɗu tare da raunata wasu 21 a hanyar Katarko zuwa Goniri a Ƙaramar hukumar Gujba a Jihar Yobe.

Kamar yadda rahoton ke nunawa, waɗanda lamarin ya rutsa da su, galibi ’yan ƙabilar Gotala ne, suna kan hanyarsu ta zuwa babbar kasuwar Buni yadi ne a lokacin da motarsu ta taka wani abin fashewa da ake zargin bam ne.

Tirela ta afka cikin kasuwa ta kashe mutum da raunata 5 a Taraba Ƙudan zuma ya tarwatsa ɗaliban da ke jarrabawar NECO

A rahoton da ya fito daga babban asibitin ƙwararru na Damaturu ya nuna cewa an kai gawarwakin mutane huɗu da suka mutu a fashewar bam ɗin zuwa gida domin yi musu jana’iza yayin da sauran ke jinya a asibitin ƙwararru da kuma asibitin koyarwa na Jami’ar Yobe da ke Damaturu.

Al’ummar Gotala dai na can ne a bakin dajin Sambisa inda ’yan ta’addan da ake kyautata zaton ’yan Boko Haram ne suka shafe shekaru suna gudanar da ayyukansu.

Wata majiya da ba a tabbatar da ita ba ta shaida wa wakilinmu cewa, ‘yan banga da motocin soji ma sun bi ta kan wannan hanya jiya ba tare da wani abu ya faru ba.

Har zuwa lokacin cika wannan rahoto, rundunar sojin ba ta fitar da wata sanarwa ba.

‘Yan uwan waɗanda abin ya shafa da aka zanta da su a asibitoci sun yi kira ga gwamnatin Jihar Yobe da ta gaggauta sake gina hanyar da ta lalace domin daƙile ayyukan ’yan tada ƙayar baya da ke addabar al’umma.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram

এছাড়াও পড়ুন:

Fashewar gurneti ya kashe yara uku a Borno 

Fashewar gurneti ya salwantar da rayukan yara mata uku a garin Pulka da ke Ƙaramar Hukumar Gwoza a Jihar Borno.

A wani rahoto da ma’aikacin Sibiliyan JTF Buba Yaga ya fitar, ya ce ɗaya daga cikin ƙananna yaran suna wasa da gurnetin da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne, suka yi watsi da su a lokacin da gurnetin ya tashi da misalin ƙarfe 2:20 na ranar Alhamis.

An garzaya da yaran zuwa Babban Asibitin Gwoza, inda likitoci suka tabbatar da mutuwarsu.

Daga nan ne aka miqa gawarsu ga iyalansu domin yi musu jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

Yadda ma’aikatan gwamnati ke gina gidaje da kuɗin sata a Abuja Yadda ma’aikatan gwamnati ke gina gidaje da kuɗin sata a Abuja

Haɗaɗɗiyar tawagar ’yan sandan da suke tantance bama-bamai (EOD-CBRN), da dakarun Operation Hadin Kai, CJTF, da mafarautan yankin sun ziyarci wurin, inda suka gudanar da aikin share wasu na’urori.

Ba a samu ƙarin ko ɗaya ba, kuma an ayyana yankin a matsayin keɓantaccen wurin da za a kauce wa bi zuwa wani lokaci.

Hukumomin tsaron sun bukaci mazauna yankin da su gaggauta kai rahoton abubuwan da suke zargi ga jami’an tsaro domin hana afkuwar irin wannan bala’i.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za a gyara tarbiyar tubabbun ’yan daban Kano
  • Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe
  • ‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno
  • An kashe mutum 24 an sace 144 a mako guda a Zamfara — Rahoto
  • ‘Yan Sandan Nasarawa Sun Kama Mutum Shida Da Laifin Fashi Da Makami Da Garkuwa Da Mutane
  • Ana Neman Daukar Karin Matakin Kawar Da Shingayen Dake Hana ‘Ya’ya Mata Zuwa Makaranta A Zamfara
  • Ma’aikatan shari’a 97 sun samu ƙarin girma a Borno
  • ’Yan bindiga sun kashe gomman mutane a ƙauyukan Sakkwato
  • ASUU na shirin sake tsunduma yajin aiki
  • Fashewar gurneti ya kashe yara uku a Borno