Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-03-15@23:25:37 GMT

NAHCON Za Ta Fara Jigilar Alhazai Ranar 5 Ga Watan Mayun 2025

Published: 12th, March 2025 GMT

NAHCON Za Ta Fara Jigilar Alhazai Ranar 5 Ga Watan Mayun 2025

Hukumar Alhazai ta Kasa NAHCON ta fitar da sunayen kamfanonin jiragen sama da za su yi jigilar Alhazan bana.

Bayanin ya ƙunshi sunayen jiragen da kuma adadin mahajjatan da aka ware wa kowannensu.

Kamfanin Fly Nas zai yi jigilar Alhazai 22,893, kashi 32.12 bisa dari kenan na maniyyatan Najeriya a bana, yayin da Kamfanin Air peace ya sami Alhazai  9,145 , kashi 12.

83.

Sauran su ne Max Air Ltd da aka warewa Alhazai 23,343, kashin 32.75 kenan bisa dari, sai kamfanin Umza Air Ltd an ware  da ya sami 15,893 wato kashi 22.30 bisa 100, wanda ya kawo adadin maniyyata 71,274 da ake sa ran za su sauke farali a bana.

Hukumar ta NAHCON ta ce za a fara jigilar maniyyatan ne a ranar 5 ga Mayun 2025.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigilar Maniyyata

এছাড়াও পড়ুন:

Rundunar Sojin Najeriya Za Ta Fara Atisayen Koyon Harbi A ‘Yar Gaba Da Ke Dutse

Rundunar sojin Najeriya ta ce za ta fara atisayen tantance gwanintar harbi na shekarar 2025 daga ranar Litinin 17 zuwa 19 ga watan Maris a Barikin Yar Gaba da ke Dutse, Jihar Jigawa.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar Sojin Najeriya ta 26 Armoured Brigade, Laftanar Uzoma Egwu-Ukpai, ya sanyawa hannu aka kuma bai wa gidan rediyon Najeriya a Dutse.

Sanarwar ta bayyana cewa, atisayen tantance gwanintar harbi ana yi ne domin auna ƙwarewar jami’an soji wajen sarrafa makamai da ingancin harbinsu.

Laftanar Uzoma Ukpai ya shawarci al’umma da kada su firgita yayin atisayen idan suka ga sojoji suna kai-komo ko suka ji karar harbi, musamman mutanen da ke zaune a yankin Yargaba.

Haka kuma, Mataimakin Daraktan ya umarci manoma da mafarauta da ke kusa da wurin atisayen da su guji yankunansu na noma da farauta a lokacin atisayen.

 

Usman Muhammad Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masarautar Hadejia Ta Raba Zakka Ta Kimanin Naira Miliyan 63 Ga Mabukata
  • Rundunar Sojin Najeriya Za Ta Fara Atisayen Koyon Harbi A ‘Yar Gaba Da Ke Dutse
  • Jami’ar Gwamnatin Tarayya Kachia Ta Shirya Tsaf Domin Fara Aiki
  • Araghchi : Iran a shirye take ta shiga tattaunawa da Turawa bisa mutunta juna
  • An Cire Maguire Cikin Tawagar Ingila Da Za Ta Buga Wasan Neman Gurbi
  • Hajjin Bana: NAHCON Za Ta Fara Jigilar Maniyyata A Ranar 6 Ga Mayu
  • Ranar Mata Ta Duniya: Kalubalen Da Mata Ke Fuskanta A Siyasar Nijeriya
  • Senegal ta yi Allah-wadai da tsare ‘yan kasarta a Mauritania
  • Gwamnati: Farashin Kayan Abinci Na Raguwa, Tattalin Arziki Na Ingantuwa
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Kaduna Na Cigaba Da Ba Da Rarar Kudi Ga Alhazan 2023