Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-12-15@01:57:11 GMT

NAHCON Za Ta Fara Jigilar Alhazai Ranar 5 Ga Watan Mayun 2025

Published: 12th, March 2025 GMT

NAHCON Za Ta Fara Jigilar Alhazai Ranar 5 Ga Watan Mayun 2025

Hukumar Alhazai ta Kasa NAHCON ta fitar da sunayen kamfanonin jiragen sama da za su yi jigilar Alhazan bana.

Bayanin ya ƙunshi sunayen jiragen da kuma adadin mahajjatan da aka ware wa kowannensu.

Kamfanin Fly Nas zai yi jigilar Alhazai 22,893, kashi 32.12 bisa dari kenan na maniyyatan Najeriya a bana, yayin da Kamfanin Air peace ya sami Alhazai  9,145 , kashi 12.

83.

Sauran su ne Max Air Ltd da aka warewa Alhazai 23,343, kashin 32.75 kenan bisa dari, sai kamfanin Umza Air Ltd an ware  da ya sami 15,893 wato kashi 22.30 bisa 100, wanda ya kawo adadin maniyyata 71,274 da ake sa ran za su sauke farali a bana.

Hukumar ta NAHCON ta ce za a fara jigilar maniyyatan ne a ranar 5 ga Mayun 2025.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigilar Maniyyata

এছাড়াও পড়ুন:

An Fara Gyaran Tashar Talabijin Ta Jigawa Don Kara Mata Nisan Zango

Gidan Talbijin na Jihar Jigawa wato JTV, ya fara gudanar da gyare-gyaren doguwar eriyar yada shirye-shiryen tashar dake garin Andaza.

Da yake yiwa shugaban gidan Talabijin na JTV Alhaji Abba Tukur karin bayani kan fara aikin, jagoran tawagar injiniyoyin, Injiniya Obi Onya, ya ce za su gudanar da aikin ta hanyar gano sassan doguwar eriyar da suke da matsala.

Injiniya Onya ya bayyana cewar, haka kuma za su gudanar da irin wannan aikin a kananan tashoshin yada shirye-shiryen tashar dake garuruwa 3 na kananan hukumomi a Jihar.

Yana mai cewar, garuruwan su ne Gumel da Hadejia da kuma Kazaure.

Shugaban gidan talabijin din  wanda ya sami wakilcin Manajan Sashin injiniya na JTV, Malam Sha’aban Abubakar Tahir, ya yi bayani kan muhimmancin yi wa doguwar eriyar gyara, wanda ya ce zai karawa tashar nisan zango.

 

Usman Muhammad Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Na Ɗauki Harkar Fim Tamkar Aikin Gwamnati — Maryam Usman
  • An Fara Gyaran Tashar Talabijin Ta Jigawa Don Kara Mata Nisan Zango
  • Bankin Ajiya na Jihar Jigawa Ya Karamar Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu
  • Yadda za ku cike neman aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON
  • Yadda za ku nemi aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON
  • Hukumar Alhazai ta Jigawa ta Kiyasta Naira Biliyan 3 Don Ayyukan Hajjin 2026
  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • NLC Ta Shirya Zanga-Zangar Rashin Tsaro A Faɗin Ƙasa Ranar 17 Ga Disamba
  • Za A Yi Manyan Zabuka A Kasar Habasha A Watan Yuni Na 2026
  • Kamfanonin Sin Sun Kera Tare Da Sayar Da Motoci Sama Da Miliyan 31 Tsakanin Janairu Zuwa Nuwamban Bana