Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-08-15@21:39:58 GMT

NAHCON Za Ta Fara Jigilar Alhazai Ranar 5 Ga Watan Mayun 2025

Published: 12th, March 2025 GMT

NAHCON Za Ta Fara Jigilar Alhazai Ranar 5 Ga Watan Mayun 2025

Hukumar Alhazai ta Kasa NAHCON ta fitar da sunayen kamfanonin jiragen sama da za su yi jigilar Alhazan bana.

Bayanin ya ƙunshi sunayen jiragen da kuma adadin mahajjatan da aka ware wa kowannensu.

Kamfanin Fly Nas zai yi jigilar Alhazai 22,893, kashi 32.12 bisa dari kenan na maniyyatan Najeriya a bana, yayin da Kamfanin Air peace ya sami Alhazai  9,145 , kashi 12.

83.

Sauran su ne Max Air Ltd da aka warewa Alhazai 23,343, kashin 32.75 kenan bisa dari, sai kamfanin Umza Air Ltd an ware  da ya sami 15,893 wato kashi 22.30 bisa 100, wanda ya kawo adadin maniyyata 71,274 da ake sa ran za su sauke farali a bana.

Hukumar ta NAHCON ta ce za a fara jigilar maniyyatan ne a ranar 5 ga Mayun 2025.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigilar Maniyyata

এছাড়াও পড়ুন:

ASCSN Ta Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Nada Muhammad Dagaceri Shugaban Ma’aikata

Kungiyar Manyan Ma’aikatan Gwamnati ta Najeriya ta yaba wa Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa bisa nada Alhaji Muhammad K. Dagaceri a matsayin shugaban ma’aikata na jiha.

Shugaban  ƙungiyar na kasa, kuma mataimakin shugaban ƙungiyar kwadago ta ƙasa TUC, Kwamared Shehu Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya kai ziyara ga shugaban ma’aikata, Alhaji Muhammad Dagaceri, a ofishinsa.

Ya tabbatar wa shugaban ma’aikatan da cikakken goyon baya da haɗin kan ƙungiyar wajen cimma manufofin da aka tsara a matsayinsa na shugaban ma’aikatan jiharta Jigawa.

“Kungiyarna sa ran yin haɗin gwiwa da zai ƙara inganta aikin ma’aikata da kuma bayar da gudunmawa wajen ci gaban jihar.” In ji shugaban ƙungiyar.

A jawabinsa, Alhaji Muhammad Dagaceri ya bayyana godiyarsa bisa wannan ziyara, tare da jaddada kudirin wannan gwamnati na samar da kyakkyawar alaka tsakanin ta da dukkan ƙungiyoyin masana’antu a fadin jihar.

Usman Muhammad Zaria

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ba mu da tabbas na ci gaba da rijistar kaɗa ƙuri’a a Borno – INEC
  • Duniyarmu A Yau: Ranar 40 Ta Imam Hussain (a) A Bana
  • Duniyarmu A Yau: Ranar 40 na Imam Hussain (a) Na Bana
  • Farashin Kayayyaki A Nijeriya Sun Sauka Zuwa Kashi 21.88%
  • ASCSN Ta Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Nada Muhammad Dagaceri Shugaban Ma’aikata
  • Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana
  • Za’a Fara tattaunawar Kasa Dangane Da Talauci da Kuma Rashin Adalci A Rabin Arziki A kasar
  • Kungiyar SSANU Ta Ba Gwamnatin Taraba Wa’adin Sati Biyu Akan Kudaden Albashin Da Ba A Biya Ba.
  • Tinubu Ya Nada Hukumar Gudanarwa Ta NCC Da Sauran su
  • Ranar Hausa ta duniya: Za a yi gagarumin biki a fadar Sarkin Daura