NAHCON Za Ta Fara Jigilar Alhazai Ranar 5 Ga Watan Mayun 2025
Published: 12th, March 2025 GMT
Hukumar Alhazai ta Kasa NAHCON ta fitar da sunayen kamfanonin jiragen sama da za su yi jigilar Alhazan bana.
Bayanin ya ƙunshi sunayen jiragen da kuma adadin mahajjatan da aka ware wa kowannensu.
Kamfanin Fly Nas zai yi jigilar Alhazai 22,893, kashi 32.12 bisa dari kenan na maniyyatan Najeriya a bana, yayin da Kamfanin Air peace ya sami Alhazai 9,145 , kashi 12.
Sauran su ne Max Air Ltd da aka warewa Alhazai 23,343, kashin 32.75 kenan bisa dari, sai kamfanin Umza Air Ltd an ware da ya sami 15,893 wato kashi 22.30 bisa 100, wanda ya kawo adadin maniyyata 71,274 da ake sa ran za su sauke farali a bana.
Hukumar ta NAHCON ta ce za a fara jigilar maniyyatan ne a ranar 5 ga Mayun 2025.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigilar Maniyyata
এছাড়াও পড়ুন:
Venezuela: Ba Mu Tsoron Kaudin Amurka Na Wuce Gona Da Iri
Ministan harkokin cikin gidan kasar Venezuela ya bayyana cewa al’ummar Venezuela ba ta tsoron barazanar da Amurka take yi ma ta, domin juyin juya halin kasar zai ci gaba, kuma azamar al’umma ce za ta yi nasara a gaban masu wuce gona da iri.
Ministan harkokin cikin gidan kasar ta Venezuela Diosdado Cabello Rondón wanda kuma shi ne sakataren jam’iyyar gurguzu ta kasar, ya ce a halin yanzu juyin juya halin kasar yana fuskatar gwagwarmaya ce wacce ba ta makami domin fuskantar matsin lamba na kowace rana daga Amurka.
Ministan harkokin cikin gidan kasar ta Venezuela wanda ya halarci bikin rantsar da sabbin shugabannin al’umma a jihar Monagas ya yi Ishara da yadda Amurka ta girke jiragen yaki a ruwa kasa da Venezuela, da kuma jiragen yaki na sama, ba don komai ba,sai kokarin tilastawa al’ummar Venezuela su mika ma ta wuya ta hanyar tsoratarwa.
Haka nan kuma ya jaddada cewa, abinda Amurkan take yi ba zai harfar ma ta Da, mai ido ba; domin ba su da masaniya akan cewa al’ummar kasar ba su tsoron wani abu ba.
Haka nan kuma ministan harkokin cikin gidan kasar ta Venezuela ya ce, babu wani abu da al’ummar kasar suke tsoro.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Zama Zakaran Duniya A Wasan “Taekwondo” Na Masu Shekaru Kasa Da 21 December 7, 2025 Afirka Ta Kudu: An Kashe Mutane 11 A Wani Bude Wuta Na Kan Mai Uwa Da Wabi December 7, 2025 Dubban Mutane Suna Guduwa Daga Gabashin DRC Saboda Barkewar Sabon Fada December 7, 2025 Mutane Biyar Ne Suka Mutu A Wata Musayar Wuta Tsakanin Sojojin Afghanistan Da Pakistan December 6, 2025 Iran Da Masar Sun yi Kira Da Kawo Karshen Keta Hurumin Gaza da Labanon da Isra’ila ke yi December 6, 2025 Qatar Tayi Gargardi Game Da Gakiyar Yarjejeniyar Gaza Matukar Isra’ila Bata Janye Ba December 6, 2025 Gwamnatin Najeriya Za ta Karbi Sabon Bashin Dala Miliyan 500 A Bankin Raya Kasashen Afrika December 6, 2025 Kungiyoyin Kare Hakkin Bil Adama Sun Yi Gargadi Game Da Yunkurin Isra’ila Na Kashe Barghusi December 6, 2025 Gasar FIFA: Iran Ta Fada Cikin Group Mai Sauki A Gasar Kwallon Kafa Ta FIFA 2026 December 6, 2025 Kasashen Musulmi 8 Sun Ki Amincewa Da Korar Falasdinawa Daga Gaza December 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci