Aminiya:
2025-08-12@01:43:56 GMT

Sojoji sun yi wa ’yan bindiga luguden wuta a Neja

Published: 27th, June 2025 GMT

Sojojin Sama sun kai gagarumin farmaki sansanonin ’yan bindiga da ke Jihar Neja a ranakun Laraba da Alhamis.

Wannan farmaki na zuwa ne a matsayin ramuwar gayya bayan da ’yan bindiga suka kai hari kan wasu dakarun Najeriya a kwanan nan.

’Yan sanda sun kama ɓarayi 5, sun ƙwato kuɗi da makamai a Gombe Ribas: Duk wani rikici tsakanina da Fubara ya ƙare – Wike

A cikin wata sanarwa da rundunar sojin sama ta fitar a shafinta na sada zumunta, ta bayyana cewa an kai harin ne a ƙarƙashin wani shiri da ake kira FANSAN YAMMA, wanda nufinsa shi ne kawar da barazanar da ’yan ta’adda ke haddasawa.

Sanarwar, wadda ta samu sa hannun Daraktan Yaɗa Labaran rundunar, Air Commodore Ehimen Ejodame, ta ce an samu bayanan sirri cewa ’yan bindigar suna satar shanu da kuma gudanar da wasu munanan ayyuka a yankunan Kakihun da Kumbashi.

Bayan haka ne sojojin sama tare da haɗin gwiwar sauran jami’an tsaro suka gano inda suke, kuma suka kai musu farmaki.

Sanarwar ta ce, “An kai hare-haren ne nan take, inda aka kashe ’yan fashin da dama, aka lalata kayayyakin da suke amfani da su, sannan aka hana su sake haɗuwa.”

A cikin makon nan ne rahotanni suka nuna cewa ’yan bindiga sun kai hari kan sansanin sojoji a Jihar Neja, inda suka kashe aƙalla jami’an soja 17.

Rundunar sojin ƙasa ta tabbatar da harin a wata sanarwa, amma ba ta faɗi adadin sojojin da suka mutu ba.

Jihar Neja na ɗaya daga cikin jihohin da ke fama da matsanancin matsalar tsaro, inda ’yan bindiga ke kai hare-hare.

Suna ƙone ƙauyuka da hallaka mutane da dama, lamarin da ke hana zaman lafiya da kuma lalata harkokin tattalin arziƙi a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga hari yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

Ƴan bindiga sun kashe mutane biyar, ciki har da wani Ɗansanda, a sabon harin da suka kai garin Babanla a ƙaramar hukumar Ifelodun ta jihar Kwara. Lamarin ya faru ne a ranar Juma’a, kwanaki ƙalilan bayan kisan wasu matafiya uku da garkuwa da wasu biyu a yankin.

Mai magana da yawun rundunar ƴansandan jihar, Toun Ejire-Adeyemi, ta ce maharan sun kai ɗaruruwa akan babura ne suka farmaki garin, kuma suka kai hari ofishin Ƴansanda na yankin, sannan suka yi ɓarna a kasuwar garin. An kashe Kofural Adejumo Wasiu tare da wasu fararen hula huɗu.

NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas  Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu

Ta bayyana cewa haɗin gwuiwar Ƴansanda, da Sojoji, da Jami’an sa-kai da mafarauta ya fatattaki maharan tare da dawo da zaman lafiya, inda yanzu aka fara sumame don kamo su. A ranar Lahadi, kwamishinan Ƴansanda Adekimi Ojo da Daraktan DSS na jihar sun ziyarci Babanla don tantance halin tsaro, tare da ganawa da Sarkin garin, Oba Yusuf Aliyu Alabi Arojojoye II.

Kwamishinan ya bayar da umarnin ci gaba da sintiri da tattara bayanan sirri tare da tura ƙwararrun jami’an bin sawu, yayin da DSS ta yi alƙawarin bayar da goyon baya da bayanan sirri domin kama duk masu hannu a harin. An kuma roƙi jama’a su kwantar da hankula, su kasance masu lura, tare da bayar da sahihan bayanai ga jami’an tsaro.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda sama da 400 a Zamfara
  • ‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno
  • An kashe mutum 24 an sace 144 a mako guda a Zamfara — Rahoto
  • Sojoji sun kama wasu kan zargin kitsa juyin mulki a Mali
  • Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara
  • Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas
  • ’Yan bindiga sun kashe gomman mutane a ƙauyukan Sakkwato
  • Ana Zanga-Zanga A Isra’ila Kan Shirin Netanyahu Na Mamaye Gaza
  • Venezuela: An dakile yunkurin kai wasu munanan hare-hare a cikin kasar
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi