Aminiya:
2025-06-27@18:38:14 GMT

Sojoji sun yi wa ’yan bindiga luguden wuta a Neja

Published: 27th, June 2025 GMT

Sojojin Sama sun kai gagarumin farmaki sansanonin ’yan bindiga da ke Jihar Neja a ranakun Laraba da Alhamis.

Wannan farmaki na zuwa ne a matsayin ramuwar gayya bayan da ’yan bindiga suka kai hari kan wasu dakarun Najeriya a kwanan nan.

’Yan sanda sun kama ɓarayi 5, sun ƙwato kuɗi da makamai a Gombe Ribas: Duk wani rikici tsakanina da Fubara ya ƙare – Wike

A cikin wata sanarwa da rundunar sojin sama ta fitar a shafinta na sada zumunta, ta bayyana cewa an kai harin ne a ƙarƙashin wani shiri da ake kira FANSAN YAMMA, wanda nufinsa shi ne kawar da barazanar da ’yan ta’adda ke haddasawa.

Sanarwar, wadda ta samu sa hannun Daraktan Yaɗa Labaran rundunar, Air Commodore Ehimen Ejodame, ta ce an samu bayanan sirri cewa ’yan bindigar suna satar shanu da kuma gudanar da wasu munanan ayyuka a yankunan Kakihun da Kumbashi.

Bayan haka ne sojojin sama tare da haɗin gwiwar sauran jami’an tsaro suka gano inda suke, kuma suka kai musu farmaki.

Sanarwar ta ce, “An kai hare-haren ne nan take, inda aka kashe ’yan fashin da dama, aka lalata kayayyakin da suke amfani da su, sannan aka hana su sake haɗuwa.”

A cikin makon nan ne rahotanni suka nuna cewa ’yan bindiga sun kai hari kan sansanin sojoji a Jihar Neja, inda suka kashe aƙalla jami’an soja 17.

Rundunar sojin ƙasa ta tabbatar da harin a wata sanarwa, amma ba ta faɗi adadin sojojin da suka mutu ba.

Jihar Neja na ɗaya daga cikin jihohin da ke fama da matsanancin matsalar tsaro, inda ’yan bindiga ke kai hare-hare.

Suna ƙone ƙauyuka da hallaka mutane da dama, lamarin da ke hana zaman lafiya da kuma lalata harkokin tattalin arziƙi a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga hari yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

Rahotanni sun bayyana cewa, wasu ‘yan bindiga dauke da makamai karkashin jagorancin wani fitaccen kasurgumin dan bindiga mai suna Babaro sun kwace iko da jagorancin karamar hukumar Kankara a jihar Katsina. Wani mai sharhi kan harkokin tsaro,  Bakatsine ne ya bayyana hakan a wani sharhi da aka wallafa a shafinsa na X, yana mai cewa, maharan sun kashe mazauna yankin da dama, tare da hana ayyukan noma, da kuma haddasa durkushewar ayyukan kasuwanci na yau da kullum a yankin. “Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan bindiga karkashin jagorancin babaro sun kwace iko da jagorancin karamar hukumar Kankara, jihar Katsina. An hana noma daga Marabar Kankara zuwa ‘Yantumaki, an kashe mutane da dama, an yi garkuwa da wasu, kiwon lafiya ya durkushe. Mazauna garin suna rokon Gwamna @dikko_radda da gwamnatin tarayya (FG) su kawo musu dauki cikin gaggawa.” in ji sanarwar LEADERSHIP ta ruwaito cewa, karamar hukumar Kankara na ci gaba da kasancewa ramin kura, inda hare-haren yankin ya jawo fargaba a fadin kasar, musamman ma sace yara dalibai sama da 300 a watan Disambar 2020. Har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto, gwamnatin jihar Katsina ko hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance dangane da wannan rahoton ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja
  • Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP
  • Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga
  • Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina
  • Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja
  • Za mu ci gaba da tattaunawa da Iran kan yarjejeniyar nukiliya — Trump
  • Isra’ila da Iran sun ci gaba da musayar wuta duk da sanarwar tsagaita wuta
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara
  • Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba