Sojoji sun yi wa ’yan bindiga luguden wuta a Neja
Published: 27th, June 2025 GMT
Sojojin Sama sun kai gagarumin farmaki sansanonin ’yan bindiga da ke Jihar Neja a ranakun Laraba da Alhamis.
Wannan farmaki na zuwa ne a matsayin ramuwar gayya bayan da ’yan bindiga suka kai hari kan wasu dakarun Najeriya a kwanan nan.
’Yan sanda sun kama ɓarayi 5, sun ƙwato kuɗi da makamai a Gombe Ribas: Duk wani rikici tsakanina da Fubara ya ƙare – WikeA cikin wata sanarwa da rundunar sojin sama ta fitar a shafinta na sada zumunta, ta bayyana cewa an kai harin ne a ƙarƙashin wani shiri da ake kira FANSAN YAMMA, wanda nufinsa shi ne kawar da barazanar da ’yan ta’adda ke haddasawa.
Sanarwar, wadda ta samu sa hannun Daraktan Yaɗa Labaran rundunar, Air Commodore Ehimen Ejodame, ta ce an samu bayanan sirri cewa ’yan bindigar suna satar shanu da kuma gudanar da wasu munanan ayyuka a yankunan Kakihun da Kumbashi.
Bayan haka ne sojojin sama tare da haɗin gwiwar sauran jami’an tsaro suka gano inda suke, kuma suka kai musu farmaki.
Sanarwar ta ce, “An kai hare-haren ne nan take, inda aka kashe ’yan fashin da dama, aka lalata kayayyakin da suke amfani da su, sannan aka hana su sake haɗuwa.”
A cikin makon nan ne rahotanni suka nuna cewa ’yan bindiga sun kai hari kan sansanin sojoji a Jihar Neja, inda suka kashe aƙalla jami’an soja 17.
Rundunar sojin ƙasa ta tabbatar da harin a wata sanarwa, amma ba ta faɗi adadin sojojin da suka mutu ba.
Jihar Neja na ɗaya daga cikin jihohin da ke fama da matsanancin matsalar tsaro, inda ’yan bindiga ke kai hare-hare.
Suna ƙone ƙauyuka da hallaka mutane da dama, lamarin da ke hana zaman lafiya da kuma lalata harkokin tattalin arziƙi a yankin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga hari yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno
Rahotanni sun tabbatar da rasuwar wasu sojoji huɗu, bayan ’yan ta’adda sun kai hari yankin Ngamdu na Jihar Borno.
Jihar Borno ta daɗe tana fama da hare-haren ta’addanci, musamman daga ƙungiyar Boko Haram.
Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 5 a Borno An yi jana’izar sojojin da ’yan bindiga suka kashe a KebbiKo da yake wasu mazauna yankin sun ce sojoji 10 ne suka mutu, sai dai mai magana da yawun rundunar Operation Haɗin Kai, Laftanar Kanar Sani Uba, bai tabbatar da hakan ba cikin sanarwar ya fitar a ranar Juma’a.
Amma rahotanni sun bayyana cewa sojoji huɗu ne suka mutu, yayin da wasu biyar suka jikkata a yayin harin.
A cewar Kanar Sani, ’yan ta’addan sun yi amfani da roka, jirage marasa matuƙa, da bama-bamai wajen kai harin.
Sai dai sojojin sun mayar da martani, inda suka kashe da dama daga cikin ’yan ta’addan.
Ya ƙara da cewa wasu motocin yaƙi na sojojin sun lalace, amma duk da haka dakarun sun yi tsayin daka wajen yaƙar maharan.
Bayan harin, ’yan ta’addan sun yi ƙoƙarin hana bin hanyar Ngamdu zuwa Damaturu, wanda hakan ya tilasta rufe hanyar na ɗan lokaci.
Daga baya,sojoji sun cire bama-bamai guda uku, sannan suka sake buɗe hanyar ga matafiya.
Laftanar Kanar Uba, ya ce an ƙara wa dakarun kayan yaƙi da harsasai domin ci gaba da fafatawa.
Rahotanni sun nuna cewa gawarwakin ’yan ta’adda kusan 15 aka samu a kusa da ƙauyen Bula Wura.
Rundunar Sojin Najeriya ta yaba wa jarumtar dakarun, tare da tabbatar wa jama’a cewa zaman lafiya ya samu a yankin.