Leadership News Hausa:
2025-11-23@04:33:24 GMT

Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba

Published: 12th, March 2025 GMT

Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba

Hakika yadda kasar Amurka ta dakatar da tallafi a wannan karo ya nuna ra’ayin shugaba Donald Trump dangane da kasashen Afirka. Wanda za a iya fahimta bisa ganin yadda ya bayyana kasar Lesotho a matsayin “kasar da ba a san ta ba”, wacce ba ta cancanci tallafin da ake ba ta ba, a kwanakin baya, yayin da yake magana da ‘yan majalisun kasar Amurka.

Sai dai shugaban bai san sauye-sauyen da kasashen Afirka suka samu ba, wadanda tun tuni suka daina dogaro da kasashen yammacin duniya.

A daura da haka, ana iya ganin fahimtar matsayin kasashen Afirka mai dacewa, a cikin maganar da ministan wajen kasar Sin Wang Yi ya fada a kwanan baya, yayin da yake amsa tambayar da wakiliyar kafar yada labaru ta Najeriya NAN ta gabatar masa. Inda ya bayyana nahiyar Afrika a matsayin wuri mai muhimmanci a karni na 21, wanda samun kwanciyar hankali da ci gaban tattalin arzikinsa ya shafi makomar bai daya ta daukacin dan Adam. Sa’an nan, bayan da ya yi bayani kan kokarin da kasar Sin ta yi wajen haifar da takamaiman ci gaba a kasashen Afirka, jami’in na Sin ya ce, “Nahiyar Afirka na cikin wani sabon mataki na farkawa. Kamata ya yi a mara musu baya, don su iya dogaro da kai wajen tafiya a kan sabuwar turbarsu ta raya kasa.” (Bello Wang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugabar Tanzania ta Naɗa ‘Yarta da Surikinta Ministoci a Ƙasar

Shugabar ƙasar Tanzania Samia Suluhu Hassan ta fitar da sunayen sababbin ministocin ƙasar, inda ta sanar da ƙirƙirar sabuwar ma’aikatar matasa, wanda hakan ya ƙara yawan ma’aikatun ƙasar daga 26 zuwa 27 a sabuwar gwamnatin.

Daga cikin ministocin akwai sababbin fuskoki, da tsofaffin ƴan siyasar ƙasar, ciki har da tsofaffin ministoci bakwai, sannan ba ta mayar da tsohon mataimakin firaministan ƙasar kuma ministan makamashi, Dotto Biteko da tsohon shugaban majalisar ƙasar, Tulia Ackson ba.

Sai dai hankali ya fi karkata ne kan naɗin ƴar shugabar ƙasar, Wanu Hafidh a matsayin mataimakiyar ministar ilimi, sannan ta naɗa surikinta, Mohamed Mchegerwa a matsayin ministan lafiya a cikin sababbin ministocin.

Wannan na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan shugabar ƙasar ta kafa kwamitin bincike domin gano musabbin zanga-zangar bayan zaɓe da aka yi a ƙasar.

Jam’iyyun hamayya da ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan’adam sun zargi jami’an tsaron ƙasar da kashe ɗaruruwan mutane, sannan suka ɓoye gawarwakinsu.

Sai dai har zuwa yanzu hukumomin ƙasar ba su fitar da alƙaluman waɗanda suka mutu ba.

Samia Suluhu Hassan dai ta lashe zaɓen ƙasar ne da kashi 98 na ƙuri’ar kasar.

 

bbc

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Sanar Da Nada Janar Jahanshashi A Matsayin Kwamandan Dakarun Rudunar Sojin Kasa
  •  Afirka Ta Kudu: Rashin Halartar Amurka Taron G-20 Ba Zai Yi Wani Tasiri Ba
  • Yan Wasan Kasar Iran Sun tashi Da Lambobin Yabo 81 A Wasannin Zumunci Tsakanin Kasashen Musulmi
  • Zaman Majalisar Amurka Kan Zargin Kisan Kiristoci A Najeriya
  • Shugabar Tanzania ta Naɗa ‘Yarta da Surikinta Ministoci a Ƙasar
  • Wayar wutar lantarki ta kashe mutum 4 a wajen cashiya a Legas
  • Achraf Hakimi Ya Zama Gwarzon Wasan Kwallon Kafar Afirka Na Shekara Ta 2025
  • Kasashen Iran Da Malesiya Sun Rattaba Hannu Kan Jarjejeniyar Fadada Dangantakar Addini
  • Kotu ta sanya ranar fara shari’ar shugabannin ƙungiyar Ansaru
  • AU ta yi Allah-wadai da tsoma bakin kasashen waje a harkokin tsaron Afirka