Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba
Published: 12th, March 2025 GMT
Hakika yadda kasar Amurka ta dakatar da tallafi a wannan karo ya nuna ra’ayin shugaba Donald Trump dangane da kasashen Afirka. Wanda za a iya fahimta bisa ganin yadda ya bayyana kasar Lesotho a matsayin “kasar da ba a san ta ba”, wacce ba ta cancanci tallafin da ake ba ta ba, a kwanakin baya, yayin da yake magana da ‘yan majalisun kasar Amurka.
A daura da haka, ana iya ganin fahimtar matsayin kasashen Afirka mai dacewa, a cikin maganar da ministan wajen kasar Sin Wang Yi ya fada a kwanan baya, yayin da yake amsa tambayar da wakiliyar kafar yada labaru ta Najeriya NAN ta gabatar masa. Inda ya bayyana nahiyar Afrika a matsayin wuri mai muhimmanci a karni na 21, wanda samun kwanciyar hankali da ci gaban tattalin arzikinsa ya shafi makomar bai daya ta daukacin dan Adam. Sa’an nan, bayan da ya yi bayani kan kokarin da kasar Sin ta yi wajen haifar da takamaiman ci gaba a kasashen Afirka, jami’in na Sin ya ce, “Nahiyar Afirka na cikin wani sabon mataki na farkawa. Kamata ya yi a mara musu baya, don su iya dogaro da kai wajen tafiya a kan sabuwar turbarsu ta raya kasa.” (Bello Wang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Manchester United ta shiga zawarcin Sergio Ramos
Ƙungiyyar Ƙwallon Ƙafa ta Manchester United ta fara zawarcin tsohon ɗan wasan Real Madrid Sergio Ramos, mai shekara 39,wanda ya bar Ƙungiyar Monterrey ta Mexico.
Ramos wanda a shekarun baya, United ta yi ƙoƙarin ɗaukarsa, yanzu haka yana da damar komawa ƙungiyyar a matsayin kyauta.
Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a Yobe Kisan Zariya: Na bar Buhari da Allah — Sheikh El-ZakzakyUnited dai yanzu haka tana fuskantar matsaloli daga ’yan wasan baya, inda Harry Maguire ke fama da rauni, yayin da sauran ’yan wasan ke tafka kura-kurai.
Manchester dai yanzu haka ta amincewa mai horarwa ta Roben Amorim ya sayi ɗan wasan baya da tsakiya a watan Januairu.
Kawo yanzu dai ƙungiyyar na mataki na 6 da maki 25 cikin wasannin 15 da ta buga a gasar Firimiyya.
A ranar Litinin ƙungiyyar zata karɓi bakuncin Bournemouth a wasan mako na 16 a filin wasanta na Old Trafford.