Leadership News Hausa:
2025-07-11@08:24:11 GMT

Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba

Published: 12th, March 2025 GMT

Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba

Hakika yadda kasar Amurka ta dakatar da tallafi a wannan karo ya nuna ra’ayin shugaba Donald Trump dangane da kasashen Afirka. Wanda za a iya fahimta bisa ganin yadda ya bayyana kasar Lesotho a matsayin “kasar da ba a san ta ba”, wacce ba ta cancanci tallafin da ake ba ta ba, a kwanakin baya, yayin da yake magana da ‘yan majalisun kasar Amurka.

Sai dai shugaban bai san sauye-sauyen da kasashen Afirka suka samu ba, wadanda tun tuni suka daina dogaro da kasashen yammacin duniya.

A daura da haka, ana iya ganin fahimtar matsayin kasashen Afirka mai dacewa, a cikin maganar da ministan wajen kasar Sin Wang Yi ya fada a kwanan baya, yayin da yake amsa tambayar da wakiliyar kafar yada labaru ta Najeriya NAN ta gabatar masa. Inda ya bayyana nahiyar Afrika a matsayin wuri mai muhimmanci a karni na 21, wanda samun kwanciyar hankali da ci gaban tattalin arzikinsa ya shafi makomar bai daya ta daukacin dan Adam. Sa’an nan, bayan da ya yi bayani kan kokarin da kasar Sin ta yi wajen haifar da takamaiman ci gaba a kasashen Afirka, jami’in na Sin ya ce, “Nahiyar Afirka na cikin wani sabon mataki na farkawa. Kamata ya yi a mara musu baya, don su iya dogaro da kai wajen tafiya a kan sabuwar turbarsu ta raya kasa.” (Bello Wang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gamayyar ‘Yan Adawa Sun Kaddamar ADC A Gombe  

An kaddamar da jam’iyyar African Democratic Party, ADC a Gombe mako guda bayan wasu jiga-jigan ‘yan adawa sun hada kai cikin jam’iyyar.

 

Shugaban jam’iyyar ADC a jihar Gombe kuma tsohon ministan sufuri Alh. Idris Abdullahi, ya ce makasudin shiga jam’iyyar shi ne ceto kasar nan daga kangin tattalin arziki da dora ta kan turbar ci gaba.

 

A cewarsa gamayyar jam’iyyun adawa sun zabi jam’iyyar ADC a matsayin jam’iyya daya tilo da za ta samar da hanyar kalubalantar jam’iyyar APC mai mulki a zaben 2027.

 

Sanata Idris Abdullahi ya jaddada kudirin kungiyar a Gombe na ci gaba da kasancewa da hadin kai domin cimma burin ta.

 

Shugaban jam’iyyar ADC na jihar Gombe Alh. Auwal Barde ya ce gamayyar ta nuna mafarin dabarun mayar da jam’iyyar a matsayin mai karfi a jihar da kuma yanayin siyasar kasar nan.

 

Ya ce jam’iyyar ta bude rajistar zama mambobinta domin karbar sabbin masu shiga tare da yin kira ga ‘yan siyasa da ba su gamsu da su daga wasu jam’iyyun siyasa da su shiga abin da ya bayyana a matsayin ingantacciyar hanyar siyasa.

 

Alh. Auwal Barde ya ba da tabbacin cewa jam’iyyar a shirye take kuma a shirye take ta ba da sabuwar alkiblar da ta shafi rikon amana, hada kai da kuma tafiyar da al’umma.

 

HUDU Shehu/Gombe

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Aragchi: Kofar Iran Ta Tattaunawa A Bude Take, Amma Amurka Sai Ta Biya Kudade Kan Kura-Kuranta
  • Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita
  • Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya
  • Aragchi Ya Tattauna Da Bin Salman Kan Karfafa Zumunci Tsakanin Kasashen Biyu
  • An gabatar da Ganduje a matsayin shugaban kwamitin hukumar FAAN
  • Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa
  • Gamayyar ‘Yan Adawa Sun Kaddamar ADC A Gombe  
  • Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki
  • Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka
  • Zan Yi Ƙoƙarin Dawo Da Martabar Kano Pillars A Idon Duniya — Ahmed Musa