Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba
Published: 12th, March 2025 GMT
Hakika yadda kasar Amurka ta dakatar da tallafi a wannan karo ya nuna ra’ayin shugaba Donald Trump dangane da kasashen Afirka. Wanda za a iya fahimta bisa ganin yadda ya bayyana kasar Lesotho a matsayin “kasar da ba a san ta ba”, wacce ba ta cancanci tallafin da ake ba ta ba, a kwanakin baya, yayin da yake magana da ‘yan majalisun kasar Amurka.
A daura da haka, ana iya ganin fahimtar matsayin kasashen Afirka mai dacewa, a cikin maganar da ministan wajen kasar Sin Wang Yi ya fada a kwanan baya, yayin da yake amsa tambayar da wakiliyar kafar yada labaru ta Najeriya NAN ta gabatar masa. Inda ya bayyana nahiyar Afrika a matsayin wuri mai muhimmanci a karni na 21, wanda samun kwanciyar hankali da ci gaban tattalin arzikinsa ya shafi makomar bai daya ta daukacin dan Adam. Sa’an nan, bayan da ya yi bayani kan kokarin da kasar Sin ta yi wajen haifar da takamaiman ci gaba a kasashen Afirka, jami’in na Sin ya ce, “Nahiyar Afirka na cikin wani sabon mataki na farkawa. Kamata ya yi a mara musu baya, don su iya dogaro da kai wajen tafiya a kan sabuwar turbarsu ta raya kasa.” (Bello Wang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Osimhen ba zai halarci bikin karrama gwarzon ɗan ƙwallon Afirka na bana ba
Fitaccen ɗan wasan gaba na Najeriya da ke taka leda a ƙungiyar Galatasaray ta Turkiyya, Victor Osimhen, ba zai halarci bikin karrama gwarazan ‘yan wasan Afirka na 2025 ba.
Osimhen, wanda ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan Afirka a 2023, ya bayyana cewa ya koma Turkiyya ne domin duba lafiyarsa, bayan raunin da ya samu a wasan da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo ta doke Najeriya.
Tankin ruwa ya kashe mutum 4, wasu sun jikkata a Jigawa An yanke wa shugaban ISWAP hukuncin ɗaurin shekara 20 a gidan yariA yau Laraba ne Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Afirka (CAF) za ta sanar da sunayen gwarazan ‘yan wasan nahiyar na shekarar 2025, a yayin babban bikin da za a gudanar a Morocco.
Za a bayyana gwarazan a rukuni-rukuni daban-daban: maza da mata, masu horarwa, ƙungiyoyi, tawagar ƙasashe, da kuma matasan ‘yan wasa masu tasowa.
Za a fara bikin ne da misalin ƙarfe 7:00 na yamma agogon Morocco da Najeriya, a jami’ar Mohammed VI Polytechnic University (UM6P) da ke Rabat, babban birnin ƙasar.