Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba
Published: 12th, March 2025 GMT
Hakika yadda kasar Amurka ta dakatar da tallafi a wannan karo ya nuna ra’ayin shugaba Donald Trump dangane da kasashen Afirka. Wanda za a iya fahimta bisa ganin yadda ya bayyana kasar Lesotho a matsayin “kasar da ba a san ta ba”, wacce ba ta cancanci tallafin da ake ba ta ba, a kwanakin baya, yayin da yake magana da ‘yan majalisun kasar Amurka.
A daura da haka, ana iya ganin fahimtar matsayin kasashen Afirka mai dacewa, a cikin maganar da ministan wajen kasar Sin Wang Yi ya fada a kwanan baya, yayin da yake amsa tambayar da wakiliyar kafar yada labaru ta Najeriya NAN ta gabatar masa. Inda ya bayyana nahiyar Afrika a matsayin wuri mai muhimmanci a karni na 21, wanda samun kwanciyar hankali da ci gaban tattalin arzikinsa ya shafi makomar bai daya ta daukacin dan Adam. Sa’an nan, bayan da ya yi bayani kan kokarin da kasar Sin ta yi wajen haifar da takamaiman ci gaba a kasashen Afirka, jami’in na Sin ya ce, “Nahiyar Afirka na cikin wani sabon mataki na farkawa. Kamata ya yi a mara musu baya, don su iya dogaro da kai wajen tafiya a kan sabuwar turbarsu ta raya kasa.” (Bello Wang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Sanatan Enugu ya mutu a Birtaniya
Majalisar Dattawa ta shiga cikin jimami a ranar Laraba bayan mutuwar Sanata Okey Ezea, mai wakiltar mazabar Enugu ta Arewa.
Bayanai sun nuna marigayin ya rasu ne a kasar Burtaniya inda yake jinya.
‘Yadda aka harbe mijina a gabana lokacin sace daliban Kebbi’ Mai taɓin hankali ya kashe soja a LegasEzea, wanda aka zaɓe a ƙarƙashin jam’iyyar LP, shi ne kaɗai Sanatan da ya ci zabe daga Enugu karkashin jam’iyyar a Majalisar Dattawa ta 10.
Rasuwarsa ta sa ya zama sanata na biyu daga yankin Kudu maso Gabas da ya rasu cikin shekaru biyu, bayan mutuwar Sanata Ifeanyi Ubah daga Jihar Anambra, wanda shi ma ya rasu a Landan a watan Yuli 2024 yana da shekara 52.
Da labarin rasuwarsa ya isa Majalisar, abokan aikinsa sun yi ta’aziyya, suna bayyana shi a matsayin ɗan majalisa mai tawali’u, mai jajircewa, da kuma sadaukarwa, wanda rashin sa ya bar gibi a zauren majalisar.
Sanata Orji Uzor Kalu, wanda ke wakiltar Abia ta Arewa, ya ce ya yi matukar kaduwa da samun labarin, inda ya bayyana marigayin a matsayin ɗan’uwana kuma abokinsa.
Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan daga Kogi ta Tsakiya, ita ma ta yi jimami, tana bayyana Ezea a matsayin aboki mai hikima da natsuwa, wanda shawarwarinsa da addu’oinsa suka taimaka mata a lokutan da ta shiga ƙalubale.
Ana sa ran Majalisar Dattawa za ta yi magana a hukumance kan rasuwarsa a zaman majalisa, tare da yin shiru na minti ɗaya don girmamawa, kamar yadda al’ada ta tanada.