Ƙarancin Abinci: UNICEF ta tallafa wa yara 600,000 a Borno da Yobe
Published: 27th, June 2025 GMT
Asusun kula da Ƙananan yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF) ya bayar da rahoton samun gagarumin ci gaba a ƙoƙarin da take yi na ceto rayukan ƙananan yara.
Da kuma samar da damammakin ci gaba a jihohin Borno da Yobe duk da ƙalubalen da ke tattare da tashe-tashen hankula da talauci, UNICEF ta samu gagarumar nasara a jihohin.
Shugaban ofishin UNICEF na Maiduguri, Joseph Senesie ne ya bayyana hakan a jawabin da ya yi a lokacin wani taron tattaunawa da manema labarai kan ɗa’ar aikin jarida da rahoton kare haƙƙin yara a Damaturu, babban birnin Jihar Yobe.
A cewarsa, a shekarar 2024 UNICEF ta tallafawa jinyar yara kimanin dubu 600 da ke fama da matsanancin halin rashin abinci mai gina jiki, tare da yi wa yara miliyan 1.2 allurar rigakafin cutar kwalara, tare da kai wa mutane miliyan 1.6 allurar rigakafin cutar kwalara.
Bugu da kari, an tallafa wa sama da yara rabin miliyan masu watanni 0-59 da rajistar haihuwa, kuma yara 500,000 sun samu ilimin boko a jihohin Borno da Yobe.
“Duk da haka, duk da waɗannan yunƙurin, ƙalubalen ya ci gaba ne kawai yadda yara 3 cikin yara 10 a Borno, Yobe, da Adamawa aka yi musu rajistar haihuwarsu. Duk da haka, kusan yara miliyan 2 ba sa zuwa makaranta a Arewa maso Gabas, wanda ke nuna buƙatar halin gaggawa na jin ƙai da ci gaba”.
Lamarin da ya ce ya ƙara dagulewa da matsalar ilimi, inda kashi 72 cikin 100 na ɗaliban da suka kammala firamare a yankin ba su iya karatu da rubutu ba, wadda wannan yana nuna babbar gazawa wajen ba da ilimi a matakin farko, kuma yana nuna buƙatar shiga lamarin cikin gaggawa.
UNICEF ta ci gaba da jajircewa wajen yin aiki tare da gwamnatoci da abokan hulɗa domin magance waɗannan ƙalubale.
Haka nan hukumar ta sadaukar da dala miliyan 270 don bayar da agajin jin ƙai da kawar da fatara a Najeriya, inda ta mayar da hankali kan ilimi da lafiya da kuma kariya ga yara masu rauni.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Super Falcons za su ƙaurace wa wasannin Nijeriya saboda riƙe musu alawus
’Yan wasan tawagar ƙwallon ƙafar Nijeriya ta Mata, Super Falcons, sun yi barazanar ƙaurace wa wasannin sada zumunta da Najeriya za ta buga a watan Disamba mai kamawa.
’Yan wasan sun ce za su ƙaurace wa wasannin ne idan har Hukumar Kwallon Kafa ta Najeriya (NFF) ta ci gaba da jinkirta biyan kuɗaɗen alawus-alawus da suke biyo tun na Gasar Olympics da aka yi a birnin Paris a 2024.
Andrea Thompson ta zama mace mafi ƙarfi a duniya Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaroWasu majiyoyi daga ƙungiyar sun tabbatar cewa ’yan wasan na ci gaba da jiran a biya su haƙƙoƙinsu na wasannin da suka buga, ciki har da alawus na nasarar da suka samu a gasar Olympics, duk da cewa Najeriya ta fice tun a matakin rukuni bayan shan kashi a hannun Brazil da Spain da Japan.
Wani jami’in tawagar, wanda ya nemi a ɓoye sunansa, ya ce ’yan wasan gaba ɗaya sun amince cewa ba za su halarci kowanne wasa ba muddin ba a biya su haƙƙoƙinsu ba.
Ana sa ran Najeriya za ta buga jerin wasannin sada zumunta daga ranar 2 zuwa 10 ga watan Disamba, a wani ɓangare na shirye-shiryen Super Falcons domin tunkarar gasar cin Kofin Afrika ta Mata na 2026.
A halin yanzu, NFF ba ta fitar da jerin sunayen ’yan wasan da za su wakilci Najeriya a wasannin ba.