Aminiya:
2025-11-27@21:56:49 GMT

Tinubu ya rattaba hannu kan sababbin dokokin haraji

Published: 27th, June 2025 GMT

Daga ƙarshe dai Shugaban Kasa Bola Tinubu ya sa hannu kan sababbin dokokin haraji guda hudu da a baya suka jawo cece-kuce da zazzafar muhawara a faɗin Najeriya.

An dai sanya hannun ne a fadar shugaban kasa ta Aso Rock da ke Abuja ranar Alhamis, inda shugaban ya ce dokokin za su bunkasa harkokin hada-hadar kudade da tattara haraji a kasar.

NAJERIYA A YAU: Ko Wadanne Dalilai Ne Ke Hana Mata A Arewa Koyon Ilimin Kimiyya? Sheikh Dahiru Bauchi ya cika shekara 101 a duniya

A kwanan nan ne dai Majalisar Dokoki ta Ƙasa ta amince da kudurorin su zama doka bayan tafka zazzafar muhawara a zaurukan majalisun guda biyu.

Daga cikin waɗanda suka halarci bikin saka hannun akwai Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio da Kakakin Majalisar Wakilai, Tajuddeen Abbas da shugabannin masu rinjaye na majalisun biyu da kuma shugabannin kwamitocin kudi na majalisun.

A ranar Laraba ce dai mai magana da yawun shugaba Tinubu, Bayo Onanuga, ya sanar da cewa da zarar sun fara aiki, kudurorin za su bunkasa hanyoyin tattara kudaden shiga a kasar.

A cewarsa, ana sa ran dokokin za su kuma karan yawan kudaden harajin da Najeriya ke samu sannan sau bunkasa harkokin kasuwanci su kuma haɓaka harkokin zuba jari daga ’yan kasuwar gida da na ƙetare.

Sai dai Hukumar Tattara Haraji ta Kasa (FIRS) ta ce dokokin ba za su fara aiki ba sai a watan Janairun 2026.

A baya dai saɗarorin dokokin da suka fi yamutsa hazo su ne na batun rarraba harajin kuɗaɗen sayen kaya na VAT da yadda za a raba shi.

Sai dai majalisar dattawa da ta wakilai ta gyara saɗarorin kafin ta amince da su tare da samun amincewar akasarin ’yan majalisar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dokokin Haraji

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Nuna Farin Cikinsa Bisa Bayyanar Daliban Kebbi, Ya Bukaci a Ceto Sauran

Daga Bello Wakili 

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bayyana farin cikinsa bisa dawowar ’yan mata 24 da ’yan ta’adda suka sace a Maga, Jihar Kebbi.

’Yan ta’addan sun kai hari makarantar  ranar 17 ga wantan Nuwamban 2026, inda suka yi awon gaba da ’yan matan, jim kaɗan bayan wata rundunar soji ta bar harabar makarantar.

Lamarin Kebbi ya haifar da wasu sace-sace makamanta a Eruku da ke Jihar Kwara da kuma Papiri a Jihar Neja.

An sako dukkan mutune 38 da aka sace a Eruku ranar Lahadi, inda a wannan ranar ce shugaban kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) Jihar Neja ya ce an samu yara 50 daga cikin ɗaliban makarantar Katolika da suka ɓace a gidajen iyayensu.

Shugaba Tinubu ya yaba wa jami’an tsaro bisa ƙoƙarin da suka yi wajen ganin an kubutar da dukkan mutanen da ’yan ta’adda suka sace.

Ya umarci jami’an tsaro da su ƙara ɗaukar matakan gaggawa don ceto sauran ɗaliban da har yanzu ke hannun ‘yan bindiga.

“Ina farin cikin cewa an samu dukkan ’yan mata 24. Ya zama wajibi mu ƙara tura jami’an tsaro  yankunan da ke da rauni don hana sake faruwar irin wannan lamari. Gwamnatina za ta bayar da dukkan tallafin da ake buƙata don cimma haka,” in ji Shugaba Tinubu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
  • Gwamna Radda Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Ya Zama Doka
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasdinu Ta Sanar Cewa Akalla Yan Mata 33000 Ne Isra’ila Ta Kashe A Gaza
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan harkar tsaro
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan tsaro
  • Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu
  • Tinubu Ya Nuna Farin Cikinsa Bisa Bayyanar Daliban Kebbi, Ya Bukaci a Ceto Sauran
  • Yan Majalisar Kudu Sun Nemi Gafarar Tinubu Ga Nnamdi Kanu
  • ’Yan Majalisar Kudu sun roƙi Tinubu ya yi wa Nnamdi Kanu Afuwa