Aminiya:
2025-06-27@09:55:53 GMT

Tinubu ya rattaba hannu kan sababbin dokokin haraji

Published: 27th, June 2025 GMT

Daga ƙarshe dai Shugaban Kasa Bola Tinubu ya sa hannu kan sababbin dokokin haraji guda hudu da a baya suka jawo cece-kuce da zazzafar muhawara a faɗin Najeriya.

An dai sanya hannun ne a fadar shugaban kasa ta Aso Rock da ke Abuja ranar Alhamis, inda shugaban ya ce dokokin za su bunkasa harkokin hada-hadar kudade da tattara haraji a kasar.

NAJERIYA A YAU: Ko Wadanne Dalilai Ne Ke Hana Mata A Arewa Koyon Ilimin Kimiyya? Sheikh Dahiru Bauchi ya cika shekara 101 a duniya

A kwanan nan ne dai Majalisar Dokoki ta Ƙasa ta amince da kudurorin su zama doka bayan tafka zazzafar muhawara a zaurukan majalisun guda biyu.

Daga cikin waɗanda suka halarci bikin saka hannun akwai Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio da Kakakin Majalisar Wakilai, Tajuddeen Abbas da shugabannin masu rinjaye na majalisun biyu da kuma shugabannin kwamitocin kudi na majalisun.

A ranar Laraba ce dai mai magana da yawun shugaba Tinubu, Bayo Onanuga, ya sanar da cewa da zarar sun fara aiki, kudurorin za su bunkasa hanyoyin tattara kudaden shiga a kasar.

A cewarsa, ana sa ran dokokin za su kuma karan yawan kudaden harajin da Najeriya ke samu sannan sau bunkasa harkokin kasuwanci su kuma haɓaka harkokin zuba jari daga ’yan kasuwar gida da na ƙetare.

Sai dai Hukumar Tattara Haraji ta Kasa (FIRS) ta ce dokokin ba za su fara aiki ba sai a watan Janairun 2026.

A baya dai saɗarorin dokokin da suka fi yamutsa hazo su ne na batun rarraba harajin kuɗaɗen sayen kaya na VAT da yadda za a raba shi.

Sai dai majalisar dattawa da ta wakilai ta gyara saɗarorin kafin ta amince da su tare da samun amincewar akasarin ’yan majalisar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dokokin Haraji

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

Majalisar ministocin harkokin waje ta kungiyar kasashen musulmi (OIC), ta gudanar da taronta na 51 daga ranar 21 zuwa 22 ga watan nan. Taron ya tabbatar da kokarin Sin na kare al’ummar musulmi tare da yaba wa ci gaban da aka samu na dangantaka tsakanin Sin da kasashen musulmi da kuma sa ran kara zurfafa hadin gwiwa tsakanin kungiyar OIC da kasar Sin.

Da yake tsokaci kan hakan, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Guo Jian kun, ya ce a ’yan shekarun nan, Sin da kasashen musulmi da ma kungiyar OIC, sun ci gaba da zurfafa aminci a tsakaninsu da fadada hadin gwiwarsu a bangarori daban-daban da karfafa musaya tsakanin al’ummominsu tare da samun kyawawan sakamako.

Ya ce Sin za ta ci gaba da hada hannu da kasashen da kungiyar OIC wajen raya dangantakar dake tsakaninsu. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki
  • Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji
  • ’Yan sanda sun kama mutum 5 kan kisan Kanawa 2 a Benuwe
  • Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 
  • DAGA LARABA: Ko Najeriya Na Da Kudin Renon Sabbin Jihohi?
  • Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu
  • Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6
  • Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Muharram
  • Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC