HausaTv:
2025-06-15@13:03:20 GMT

ECOWAS ta kaddamar da rundunarta mai dakaru 5,000 don yakar ta’addanci

Published: 13th, March 2025 GMT

Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka ECOWAS ta kaddamar da wata rundinarta mai manufar yaki da ayyukan ta’addanci da miyagun laifuffuka a yankin.

Ministan tsaron Nijeriya, Mohammed Badaru Abubakar ne ya sanar da hakan a yayin taron Kolin ECOWAS na hafsoshin tsaro karo na 43 a babban birnin tarayyar Nijeriya Abuja a ranar Talata.

Badaru ya ce taron ya jaddada kudurinsu na magance matsalolin tsaro da ke addabar yankin.

 “Kaddamar da wannan runduna yana kara jaddada kudurinmu na tunkarar ta’addancin da ya shafi tsaron yankin,’’ in ji shi.

Taron ya samu halartar manyan hafsan hafsoshin tsaro na kasashen kungiyar ECOWAS, banda kasashen Mali da Burkina Faso da Nijar wadanda suka raba gari da kungiyar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yarima Mai Jiran Gadon Saudiyya Ya Jaddada Goyon Bayan Kasarsa Ga Iran
  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Shaida Gamsuwa Da Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
  • Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran
  • Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
  • Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran
  • An Kaddamar Da Bikin Gabatar Da Jerin Shirye-shiryen Telebijin Da Fina-finai Na CMG A Birnin Astana
  • Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara