Aminiya:
2025-06-26@12:21:51 GMT

Gwamnatin Gombe za ta sayi takin N8.8bn don tallafa wa manoma

Published: 26th, June 2025 GMT

A ƙoƙarinta na bunƙasa noma da samar da isasshen abinci, Gwamnatin Jihar Gombe ta amince ta sayi tan 10,000 na taki, wanda ya yi daidai da buhu 200,000 domin shirin noman daminar bana.

Kwamishinan Harkokin Noma na Jihar, Dokta Barnabas Musa Malle, ya ce za a kashe Naira biliyan 8.8 wajen sayen takin.

1447: Yau ce ranar sabuwar shekarar Musulunci – Sarkin Musulmi 2027: Zan karɓi kowane irin muƙami da Tinubu zai ba ni — Sanata Barau

Ya ce hakan na nuna yadda gwamnatin jihar ke ƙoƙarin tallafa wa manoma da kuma ƙara samar da abinci a jihar.

Dokta Malle ya ce, “Gwamnati ta fito da sabbin hanyoyin aiki sama da yadda aka yi a baya, kuma za a raba wa manoma takin domin su fara amfani da shi kafin damina ta sauka.”

Ya kuma bayyana cewa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya zai ƙaddamar da wannan shiri a ranar Alhamis, 26 ga watan Yuni, 2025.

An shirya sayar da takin a farashi mai rahusa domin manoma su iya saya.

Wannan shiri yana daga cikin matakan gwamnatin na tabbatar da ci gaba a harkar noma da kuma shawo kan matsalar ƙarancin abinci a nan gaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnati Kwamishina

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe

Rundunar ‘yansandan jihar Benuwe ta tabbatar da garkuwa da dukkan fasinjojin wata motar bas ta kamfanin Benue Links a hanyar Eke, Ugbokolo a karamar hukumar Okpokwu ta jihar a yammacin Lahadi. Wani ganau da ya zanta da LEADERSHIP ta wayar tarho, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 7 na yammacin ranar Lahadi, inda wasu ‘yan bindigar suka tare wata motar bas din da ta taho daga Abeokuta, babban birnin jihar Ogun, suka yi awon gaba da fasinjojin da ke cikinta bayan sun kwace kayayyakinsu, sannan suka tafi da su cikin daji. 2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar Benuwe, Edet Udeme ya bayyana cewa, lamarin ya rutsa ne da wata motar bas kirar Toyota mai lamba 14B-143BN, wadda aka same ta a gefen titi a Ugbokolo, cikin karamar hukumar Okokwu. A cewar Udeme, da samun rahoton lamarin, tawagar ‘yansanda tare da hadin gwiwar sojoji da kuma ‘yan sa kai na al’ummar jihar Benuwe, suka yi gaggawar zuwa wurin. “A lokacin da rundunar ta tsunduma dajin, ta ceto daya daga cikin fasinjojin, mai suna Paul Terns, wanda ya yi nasarar tserewa daga hannun masu garkuwar”. Udeme ta kara da cewa, an tura karin wasu sojoji a yankin domin kara kaimi wajen neman sauran fasinjojin da kuma tabbatar da dawowarsu cikin koshin lafiya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun kama mutum 5 kan kisan Kanawa 2 a Benuwe
  • Gwamnatin Neja ta rufe Jami’ar IBB bayan ɓarkewar rikici
  • NAJERIYA A YAU: Yadda ‘Yan Najeriya Za Su Kula Da Lafiyar Jikin Su
  • Gwamnatin Kano ta ba da hutun sabuwar shekarar musulunci
  • Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato
  • Gwamnatin Gombe za ta biya ’yan fansho Naira biliyan 6.6 kuɗin ritaya
  • Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa
  • Gwamnatin Nijeriya ta yi wa Amurka martani kan barazanar tsaro a Abuja
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe