Tawagogin tattauna batutuwan cinikayya da tattalin arziki na Sin da Amurka, sun kara tabbatar da bayanan tsarin aiwatar da muhimmiyar matsayar da shugabannin kasashen biyu suka cimma yayin tattaunawar da suka yi ta wayar tarho a ranar 5 ga watan nan na Yuni, da karfafa sakamakon da aka cimma a tattaunawar cinikayya da tattalin arziki da aka yi a Geneva.

Kakakin ma’aikatar kula da cinikayya na Sin ne ya bayyana haka yau, inda ya ce an tabbatar da bayanan ne bayan bangarorin biyu sun ci gaba da tuntubar juna bayan tattaunawa mai ruwa da tsaki da suka yi a birnin London a ranekun 9 da 10 ga wata.

Ya ce Sin za ta bi tsarin doka wajen sake nazari da amincewa da izinin neman fitar da wasu kayayyaki da aka takaita fitarwa, ita kuma Amurka za ta cire jerin takunkuman da ta kakabawa kasar Sin.

A cewar kakakin, Sin na fatan Amurka za ta yi amfani da tsarin tuntubar juna kan tattalin arziki da cinikayya dake tsakaninsu, ta ci gaba da karfafa fahimtar juna da rage sabanin dake akwai da karfafa hadin gwiwa don ganin dangantakar Sin da Amurka kan tattalin arziki da cinikayya ya dore cikin aminci. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: tattalin arziki

এছাড়াও পড়ুন:

Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya
  • Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri
  • Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP
  • Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya
  • Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai, makarantun Islamiyya
  • Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai da makarantun Islamiyya
  • An tallafawa iyalan ‘yan sanda da Naira miliyan N13.4m a Borno
  • An tallafawa iyalan jami’an ‘yan sanda da Naira miliyan N13.4m a Borno
  • Mutane 4 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata Yayin Da Wata Mota Ta Taka Bam A Borno