Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva
Published: 28th, June 2025 GMT
Tawagogin tattauna batutuwan cinikayya da tattalin arziki na Sin da Amurka, sun kara tabbatar da bayanan tsarin aiwatar da muhimmiyar matsayar da shugabannin kasashen biyu suka cimma yayin tattaunawar da suka yi ta wayar tarho a ranar 5 ga watan nan na Yuni, da karfafa sakamakon da aka cimma a tattaunawar cinikayya da tattalin arziki da aka yi a Geneva.
Kakakin ma’aikatar kula da cinikayya na Sin ne ya bayyana haka yau, inda ya ce an tabbatar da bayanan ne bayan bangarorin biyu sun ci gaba da tuntubar juna bayan tattaunawa mai ruwa da tsaki da suka yi a birnin London a ranekun 9 da 10 ga wata.
Ya ce Sin za ta bi tsarin doka wajen sake nazari da amincewa da izinin neman fitar da wasu kayayyaki da aka takaita fitarwa, ita kuma Amurka za ta cire jerin takunkuman da ta kakabawa kasar Sin.
A cewar kakakin, Sin na fatan Amurka za ta yi amfani da tsarin tuntubar juna kan tattalin arziki da cinikayya dake tsakaninsu, ta ci gaba da karfafa fahimtar juna da rage sabanin dake akwai da karfafa hadin gwiwa don ganin dangantakar Sin da Amurka kan tattalin arziki da cinikayya ya dore cikin aminci. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: tattalin arziki
এছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikatan shari’a 97 sun samu ƙarin girma a Borno
Hukumar Shari’a ta Jihar Borno ta ƙara wa ma’aikatanta 97 girma bayan wani taro na kwanaki huɗu da ta gudanar a Maiduguri.
Muƙaddashin sakataren hukumar, Saleh Khala Jidda ne, ya bayyana hakan a wata sanarwa cewa ma’aikatan sun samu ƙarin girma ne saboda ƙwazonsu.
EFCC ta kama ’yan damfara a ɗakin karatun Obasanjo ’Yan bindiga sun kashe gomman mutane a ƙauyukan SakkwatoWaɗanda abin ya shafa sun hada da Majistare 10 daga matakin Majistare mataki na ɗaya zuwa Babban Majistare mataki na biyu.
Sai Majistare daga matakin farko zuwa Babban Majistare na biyu.
Sauran sun haɗa manyan Magatakarda daga mataki na ɗaya zuwa na biyu.
Sai dai a gefe guda, hukumar ta ɗauki mataki kan wani alƙalin Babban Kotun Majistare ta 4 da ke Wulari, Maiduguri, mai suna Yusuf Garba.
Binciken da kwamitin ƙorafe-ƙorafen jama’a ya gudanar ya gano cewa alƙalin ya karkatar da kuɗaɗen shiga na gwamnati har Naira 100,000.
Saboda haka aka sauke shi daga muƙaminsa tare da umartar ya kai rahoto ga Babban Magatakarda domin a sake masa muƙami.
Hukumar ta tabbatar wa jama’a cewa tana da niyyar ci gaba da tabbatar da gaskiya da adalci a kotuna.
Sannan ta ce za ta ladabtar da masu cin hanci da rashawa da kuma girmama masu gaskiya da riƙon amana.