Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya
Published: 26th, June 2025 GMT
A yau Laraba, shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na kasar Mozambique Daniel Francisco Chapo, suka mikawa juna sakon taya murnar cika shekaru 50 da kafuwar huldar diflomasiyya tsakanin kasashensu.
A cikin sakonsa, shugaba Xi ya bayyana fatansa na kara hadin gwiwa da Chapo, a fannin yayata dadadden zumuncinsu bisa wannan zarafi mai kyau, da kuma zurfafa hadin gwiwarsu bisa tabbatar da ingantacciyar shawarar “ziri daya da hanya daya”, da kuma dandalin hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka da sauransu.
A nasa bangare, Chapo ya ce, kasarsa na fatan zurfafa huldar bangarorin biyu, bisa tushen mutunta juna, da samun ci gaba da cin moriya tare, da kuma habaka hadin kai, da kiyaye tsarin gudanar da harkokin kasa da kasa tsakanin mabambantan bangarori. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
‘Hayakin janareta’ ya kashe mutum 4 ’yan gida daya a Borno
Mazauna kauyen Chatta da ke karamar hukumar Hawul a jihar Borno sun fada alhini sakamakon rasuwar wasu mutum hudu ’yan gida daya.
Ba a dai tabbatar da ainihin musabbabin rasuwarsu ba, amma mazauna yankin da lamarin ya faru sun ce suna zargin hayakin injin samar da lantarki na janareta ne ya yi ajalin su.
An kama bama-baman da aka boye a cikin kayan gwangwan a Kaduna Ana zargin ‘yan sanda da karya hannun SoworeMajiyoyin da ke kauyen na sun shaida wa rundunar ’yan sandan jihar cewa wadanda suka mutun sun hada da Yakubu Samanja, matarsa Esther Yakubu, da ’ya’yansu biyu, Amos Yakubu da Maryamu Yakubu.
Wani dan uwan mamatan mai suna Ibrahim Samanja, ya ce ya gano faruwar hakan ne a lokacin da ya ziyarci gidan da sanyin safiyar Talata inda ya tarar da gidan gaba daya ba a halin da aka saba gani ba.
“Na zo da misalin karfe 7:00 na safe na yi ta buga kofar gidan amma babu wanda ya amsa, sai na shiga damuwa kuma daga karshe dole na balle kofar, a lokacin ne na ga gawarwakinsu a kwance a cikin dakin,” in ji shi.
Ya kuma ce, “Bayan gano lamarin nan da nan na sanar da hukumomin ’yan sanda da ma’aikatan lafiya yadda ba tare da bata lokaci ba suka ziyarci wurin inda suka tabbatar da mutuwar dukkan ’yan uwan hudu.
“Daga baya an kwashe gawarwakin zuwa babban asibitin garin Marama, inda aka ajiye su a dakin ajiyar gawarwaki domin adanawa da kuma tantance musabbabin mutuwar su.
Mutanen kauyen sun bayyana lamarin a matsayin abin da ya dame su kuma sun ce mamatan kafin nan ba su nuna alamun wata rashin lafiya ko damuwa ba kafin mutuwarsu ta farar daya.
Sun ce binciken farko da aka yi a wurin ya nuna babu wani alamun tashin hankali, amma mazauna yankin na zargin yiwuwar kamuwa da guba ko shakar gurbatacciyar iska daga wani injin janareta da suke amfani da shi.
Rundunar ’Yan Sandan jihar ta bakin Kakakinta, ASP Nahum Daso ta ce tuni an fara bincike don gano ainihin musabbabin mutuwar mutanen.