Leadership News Hausa:
2025-06-27@22:15:07 GMT

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Published: 27th, June 2025 GMT

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Koyon ilimi ta kafar sadarwa ta zamani yana kara bayyana muhimmancin koyarwa musamman, ma ga wadanda suka dade suna koyon.Akwai samfuna dadama wadanda ake amfani dasu wajen koyarwa wadanda ana tsara su ko shiryasu ne domin su kasance daidai,da fahimtar dalibai.Irin yadda ake bi ko amfani da hanyoyi wajen tabbatar da cewar an samu inganta bunkasar dabaru,kai harma da ci gaba da tunawa da lamarin tattalin arziki domin ci gaban wanda zai taimakawa mutum.

Ida ana bukatar damarmakin da za’a fahimci abin ya zahirance,kamata yayi ayi amfani da manhajar da ta dace, ko tayi daidai da bukatun manya wadanda suke wani kamfani.

 

Ta yaya ilimin da ake samun damar mallakarsa zai daidaita yadda rashin shi ke damuwar duniya gaba daya?

Rashin damar samun ilimi a duniya wata babbar matsala ce da ake ci gaba da fuskanta, amma shi ilimi yana zama wani babban makami wajen yin maganin ita matsalar. Ana kuma iya cimma hakan ne ta hanyar samar da ingantaccen ilimi,da kuma iya daidaita shi gibin ta hnyar samar da azuzuwan da suke biya bukatun zamantakewa da tattalin arziki,da kuma samar da wasu hanyoyi da mutane wadanda suke daga cikin wuraren da basu samu damar ba.Nan ga  hanyar da ilimin da za’a iya samu zai taimaka wajen yin maganin rashin samun daidaituwa:

Ba kowa damar yadda zai kara ilimi: Hanyoyin da za ‘a iya samun ilimin da zai amfanar,wato kamar karatun ilimin digirin da za’a iya yi da kafar sadarwa,ta zamani,domin  hanyoyin da mutane zasu  iya amfani da a kasashe masu tasowa ko al’umma cikin gundumomin da aka barsu a baya.Tsare- tsaren karatun na bada damar samun ilmi mai zurfi ba tare da an fuskantar matsalar rashin isassun kudade ba,a makarantun da suke ba,na gwamnati ba.

Ba wuraren da aka dannesu wajen tafarkin ci gaba,damar,suma,su nuna rin tasu bajintar:Ilimin da ake iya samarwa shi ma,yanaiya bada damar tabbatar da wuraren,da al’umman aka maida su ‘yan Bora,wadanda suka hada da maza da mata,da suke Karkara,da kuma sauran mutane da suke da,nakasa,sun samu irin damar ilimi da sauran al’mma suka samu lamarin da yake inganta duk abubuwan da suke bada damar tafiya tare da wasu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

“Yunwa da talauci ba wai abubuwa ne da suka shafi al’umma ba ne kawai, su ne ke haifar da rashin tsaro, laifuka, tashin hankali, da kuma wargajewar al’umma, wadannan al’amura suna haifar da mugun yanayi, talauci yana haifar da rashin tsaro da rashin tsaro, sannan kuma ya kara zurfafa talauci.

“Wadannan yunkurin a bayyane suke ta hanyar kara tallafi ga shirye-shiryen samar da abinci, habaka karfin aiwatar da doka, da ababen more rayuwa don tallafawa samarwa da rarraba noma.

“A ofishin mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, ONSA, muna ci gaba da hada kai da ayyukan motsa jiki da marasa karfi a fadin rundunonin soja, jami’an leken asiri, hukumomin tsaro, da masu ruwa da tsaki na gwamnati da masu zaman kansu.

“Duk da ci gaban da aka samu, batutuwa kamar rashin aikin yi, yunwa, da rashin samun damar matasa sun ci gaba da dawwama kuma suna bukatar mafi zurfi, mafita na dogon lokaci. Saboda haka, wannan dandalin yana ba da kyakkyawan tsari don fahimtar juna da raba ra’ayoyin. Kalubalen da muke fuskanta a yau suna da karfi da kuma bangarori da yawa. Saboda haka, manufarmu a nan ita ce, dole ne a hade tare, domin ci gaba da habaka aikin. “

A nasa bangaren, Babban Hafsan Hafsoshin Tsaron Kasar, CDS, Janar Christopher Musa, ya bayyana cewa yunwa da fatara ba kalubale ne kawai na zamantakewa ba har ma sun zama barazana ga tsaron kasa.

CDS wanda babban jami’in horas da sojoji Rear Admiral Ibrahim Shetimma ya wakilta, ya yi kira da a samar da tsarin yaki da yunwa da fatara na kasa baki daya, tare da jaddada tasirinsu ga tsaron cikin gida na Nijeriya.

Ya ce: “Rashin tsaro a yau ba wai kawai makamai ne ke bayyana shi ba, har ma da tauye tattalin arziki, rashin abinci, da bacin rai.

“Yankin Arewa ta Tsakiya, musamman Jihar Binuwai, misali ne karara na yadda rikicin manoma da makiyaya suka lalata amfanin gona da raba a’umma da matsugunansu.”

Musa ya yi nuni da cewa, rugujewar al’ummar manoma da mamaye filayen noma ba bisa ka’ida ba, na haifar da hauhawar farashin kayayyakin abinci, da lalata matsugunan jama’a, da kuma yin kaura, wanda hakan ya kawo tabarbarewar tattalin arziki da hadin kan kasa.

Ya yi kira ga al’umma da su hana masu aikata laifuka da ‘yan ta’adda mafaka ta hanyar tallafa wa tattara bayanan sirri, bayar da rahoto kan lokaci da kuma lura da al’umma.

CDS ya yi kira da a gaggauta sanya hannun jari a fannin raya aikin noma daga tushe, sannan ta bukaci gwamnati da masu ruwa da tsaki da su mayar da aikin noma a matsayin sana’a mai daraja da lada ta hanyar inganta hanyoyin samun lamuni, kayayyakin more rayuwa da kuma alakar kasuwa.

Ya kara da cewa, “Tare da hijirar da matasan karkara ke yi zuwa birane, yawan amfanin goma yana raguwa. Dole ne mu sake mayar da noma abin sha’awa, ba a matsayin makoma ta karshe ba, amma a matsayin aikin kasa da kuma aiki mai daraja,” in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai
  • Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS
  • Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP
  • Ƙarancin Abinci: UNICEF ta tallafa wa yara 600,000 a Borno da Yobe
  • Ƙarancin abinci: UNICEF ta tallafawa yara 600,000 a Borno, Yobe
  • 2027: Zan karɓi kowane irin muƙami da Tinubu zai ba ni — Sanata Barau
  • PDP ta mayar wa da na hannun damar Wike kujerarsa ta sakatarenta
  • Barau ya nesanta kansa daga masu nema masa kujerar mataimakin Tinubu a 2027
  • Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?