Aminiya:
2025-10-13@18:09:46 GMT

Ƙudan zuma ya tarwatsa ɗaliban da ke jarrabawar NECO

Published: 27th, June 2025 GMT

Wasu gungun ƙudan zuma sun kai hari tare da tarwatsa ɗaliban da ke rubuta jarrabawar Hukumar da ke shirya jarrabawar kammala sakandare ta ƙasa ta Najeriya (NECO) a makarantar sakandaren kimiyya ta Mairi da ke Maiduguri a Jihar Borno.

Wannan hari na ba-zata da gungun ƙudan zumar suka kai ya tilastawa ɗalibai da malaman makarantar tserewa daga harabar makarantar domin neman tsira.

Shugaban APC na ƙasa Ganduje ya yi murabus NDLEA ta kafa cibiyar kula da masu shaye-shaye a Yobe 

Shaidun gani da ido sun ce, sun ga ɗalibai na barin litattafai da takalma da jakunkuna, har ma da kekunansu yayin da suke gudu daga makarantar.

A cewar wani ɗalibin da ke jarabawar da ya nemi a sakaya sunansa ya ce, ƙudan zuman sun daɗe da tarewa a wannan makarantar, amma ba su kai hari a baya ba sai a yanzu.

“Muna rubuta jarrabawar harshen larabci (Arabic) sai ƙudan zuma suka fito gadan-gadan daga wurin da suke da ke harabar makarantar suka far mana da harbi wanda ban san abin da ya jawo harin ba,” in ji wani dalibin.

Wannan lamari dai na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan wani harin ƙudan zuma da suka kai a makarantar Shehu Sanda Kyarimi da ke kan titin Bama a birnin na Maiduguri.

Ma’aikatar ilimi, kimiyya, fasaha da kirkire-kirkire ta jihar Borno ce ke kula da harkokin ilimi a jihar, gami da tabbatar da tsaron makarantu.

Duk da haka, abubuwan da suka faru irin waɗannan suna nuna buƙatar matakan kare ɗalibai daga barazanar da ba zato ba tsammani makamancin abin da ya faru a yanzu.

Harin dai ya kawo cikas ga gudanar da jarabawar NECO cikin kwanciyar hankali, lamarin da ya janyo damuwa a tsakanin ɗalibai da malamai da iyayen wannan makaranta.

Rahoton na nuna cewar, an yi sa’a kawo yanzu ba a samu asarar rayuka ko mummunan jikkata ba.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Iran Ya Ja Kunnen Amurka Kan Taba Jiragen Dakon Man Kasa

Wani babban dan majalisar dokokin kasar Iran ya ja kunnen kasar Amurka kan taba jiragen ruwan dakon danyen man kasar Iran a tekun farisa ko a wani wuri.

Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto Alaeddon Burujardi dan majalisar dokokin kasar Iran sannan mamba a kwamitin al-amuran kasashen waje da kuma tsaron kasa yana fadar haka.

Ya kuma kara da cewa duk wanda ya taba jiragen ruwan daukan man fetur na Iran wadanda suke dauke da danyen man fetur zuwa kasashen waje, ya san cewa iran ba zata kyale ba. Burujaedi ya bayyana cewa Washington ta san karfin sojojin ruwa na kasar Iran a bayan. Ya ce idan Amurka ta kuskura ta taba jirgin ruwan dakon mai na kasar Iran ta san cewa zata rama maida martani masu tsanani. Burujardi ya bayyana haka ne bayanda gwamnatin Amurka ta dorawa wasu mutane 50 da kuma kamfanonin jiragen ruwa masu jigilar danyen man fetur na kasar Iran daga kasashen UAE, Hong Kong da kuma China,takunkuman tattalin arziki

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Bayan Yakin Kwanaki 12, Kifar Da Gwamnatin JMI Ya Fita Daga Zabin Makiya: Aref October 11, 2025 Iran Ta Bukaci HKI Ta Aiwatar Da Yarjeniya Da Gaza Kamar Yadda Take October 11, 2025 HKI Ta Kashe Mutane 19 A Gaza Duk Tare Da Tsagaita Wuta October 11, 2025 Iran Tana Goyon Bayan Duk Wani Shirin Zaman Lafiya Da Ya Hada Da Kawo Karshen Kisan Kiyashi A Gaza October 11, 2025 Faransa Da Jamus Da Kuma Birtaniya Sun Bayyana Aniyarsu Ta Ganin An Farfado Da Tattauna Da Iran October 11, 2025 Kungiyoyin Falasdinawa Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Tsagaita Bude Wuta A Gaza October 11, 2025 Venezuala Ta Bukaci Kwamitin Sulhun M.D.D Da Ya Tabbatar Da Cewa: Amurka Tana Barazana Ga Zaman Lafiya October 11, 2025 Pakistan Ta Kai Hari Kan Kasar Afganistan, Inda Ake Rade-Radin Kashe Shugaban Taliban Na Kasarta October 11, 2025 Putin: Natanyahu Yana Son Warware Matsaloli Da Iran Cikin Lumana Ba Tare Da Yaki Ba October 10, 2025 Majalisar Turai Ta Bukaci Kasashen Nahiyar Su Kakkabo Jiragen Yakin Rasha October 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ba Bu Dalilin Da ASUU Za Ta Fara Yajin Aiki, An Biya Duk Buƙatunsu – Ministan Ilimi 
  • An Wallafa Ra’ayoyin Shugaba Xi Kan Batutuwan Da Suka Shafi Mata Da Yara Cikin Karin Harsunan Waje
  • Wata Kotu a Faransa ta yi watsi da rufe wata makarantar musulmi a birnin Nice  
  • Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 
  • Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
  • ’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno
  • Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Iran Ya Ja Kunnen Amurka Kan Taba Jiragen Dakon Man Kasa
  • Mutane 2 sun rasu a rikicin manoma da makiyaya a Kebbi
  • Iran Tana Goyon Bayan Duk Wani Shirin Zaman Lafiya Da Ya Hada Da Kawo Karshen Kisan Kiyashi A Gaza
  • Pakistan Ta Kai Hari Kan Kasar Afganistan, Inda Ake Rade-Radin Kashe Shugaban Taliban Na Kasarta