Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana
Published: 27th, June 2025 GMT
Misali, a lokutan hare-haren, an kone gidaje da dama, inda wasu ahali ma, wanda yawansu ya kai, har zuwa 15, aka shafe su, daga doron kasa, a lokacin da suke kan bacci, a gidansu.
Wasu daga cikin wadanda suka tsallake Rijiya da baya daga hare-haren na ‘yan ta’addar, sun bayyna yadda ‘yan ta’addar, suka cinnawa wasu shaguna da ke a wata kasuwa, da ka mayar a matsayin wajen kwanan, ‘yan gudun hijira, wuta.
Duk da kokarin da wasu matasa da kuma kokrin jami’an tsaro na dakile maharani, hakan ya faskare su, hatta wani daya daga cikin jami’in tsaro da aka tura wanzar da tsaro, ya rasa ransa.
Duk a 2025, a watan Afiiru an kai hare-hare a Logo da Ukum, inda aka kashe sama da 50.
Abin takaicin shi ne, duba da cewa akasarin masu kai hare-haren, sai sun sanar sanar suke kai hare-haren.
A gafe daya kuma, shuwagabbin alumma a wadannan yankunan su kan ankarar da hukumomi kafen kai hare-haren, amma abin takaici, mahukuntan, ba su daukar matakan dakile kai hare-haren.
A kwanan baya, Shugaba Bola Tinubu, ya umarci manyan Hafshoshin sojin kasar, da su gaggauta, kawo karshen kai hare-haren, tare da dawo da zaman lafiya a jihar.
Kazalika, ya danganta kashe-kashen, a matsayin na rashin imani da janyo koma baya, inda kuma ya yi kira ga jagororin ‘yan siyasa da shuwagabanin alumomi da ke a jihar, musamman a yankunan da lamarin yafi yin kamari, da su dakatar da rura wata, kan rikice-rikicen, musamman kan yadda suke furta kalaman kiyayya.
Fafaroma, Leo na 14, a na sa bangaren, ya yi tir da kashe-kashen a jihar, inda ya danta lamarin da kisan Kiyashi.
Hakazalika, Gwamnan jihar Hyacinth Alia, a martaninsa, ya bukaci Gwamnatin Tarayya da ta kawo wa jihar dauki, wanda ya yi nuni da cewa, Biniwe ba wai dokar ta baci take bukata ba, daukin gaggawa take bukata, ta hanyar tura jami’an tsaro da kayan aiki, domin a yaki, masu kai hare-haren.
Sai dai, wannan furucin na gwamnan, tamkar holoko ne, kawai, domin alummar jihar, sun gaji, da yin wani zaman makoki, sun fi bukatar, a samar masu da jami’an tsaro, su kuma koma su ci gaba da noma gonakansu, suna kuma son su ci gaba da barcinsu, da idanuwansu, biyu, a rufe, ba tare da wata fargabar, za a kai masu hari a yayin da suke kan yin barcinsu ba.
A gafe daya kuma, ana ci gaba da cacar baki a tsakanin Gwamna Alia da wasu jiga-jigai na jihar, inda Gwamnan a kwanan baya, ya yi zargin cewa, akwai wasu ‘yan siyasar jihar, da ke zaune Abuja, suke ci gaba da kara rurar wutar rikici a jihar, ciki har da ma wasu jiga-jigan ‘yan Majalisar kasa da suke wakiltar mazabunsu, a majalisar.
Koda yake dai, ‘yan Majalisar, sun karyata wannan ikirarin na Gwamnan, inda suka zargi Alia, da kin wanzar da dokar barin yin kiwo a bainar jama’a a jihar.
Bai wai kawai cafko masu aikata ta’asar ya kamata ayi, ya zama wajibi, a hukunta su, kamar yadda dokar kasar, ta tanada.
Bugu da kari, dole ne Gwamnatin Tarayya, ta gagauta daukar matakai, tare da kuma taimakawa Gwamnatin jihar, domin ta samu karfin tarwatsa masu kai wa alumomin, hare-haren da kare alumomin.
Ya kuma zama wajbi, a sake yin nazari, kan batun iyakokin jihohi da batun burtanin masu kiwon dabbobi da kuma karfafa dangantaka, a tsakanin Fulani makiyaya da sauran alumomin da ke a jihar.
Hakazalika, ya zama wajibi, Gwamnatin Tarayya ta hada taron tattaunawa na kasa, kan batun na kai hare-haren.
Wannan Jaridar, ita ma, ta bi sahun sauran ‘yan Nijeriya, wajen mika ta’aziyyarta, bisa rasa rayukan da hare-haren ya rutsa da su tare da kuma kira da a dauki matakan gaggawa kan batun, ba wai kawai, yin bayanai ba.
Lokaci ya yi, da za a kawo karshen rikice-rikice da nuna kiyaya, a tsakanin juna.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: kai hare haren kai hare hare
এছাড়াও পড়ুন:
An tura ’yan China 6 kurkuku kan laifin ta’addanci a Nijeriya
Wata Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Jihar Legas ta yi wa wasun ‘yan China shida ɗaurin shekara ɗaya bayan ta same su da laifin ta’addanci da zamba ta intanet.
Sanarwar da hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arziƙin Nijeriya ta’annati (EFCC) ta fitar ta ce kotun da ke unguwar Ikoyi ta Jihar Legas ce ta ɗaure mutanen ne bayan ta same su da laifi.
Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Muharram Harin asibiti ya kashe mutum 40 a Sudan — WHO“Masu laifin sun hada da : JIA You (da aka fi sani da A. You) da Wang Zheng Feng ( da aka fi sani da Feng) da Liu San Hua da Chen Wen Yuan da Liu BeiIxingda Wen Zong Xu (da aka fi sani Li Long),” in ji sanarwar.
EFCC ta ce masu laifin suna cikin mutum 792 da ake zargi da hannu a damfara ta hanyar kirifto waɗanda aka kama ranar 19 ga watan Disamba shekarar 2024 a Legas a wani samame da hukumar ta ƙaddamar mai taken “Eagle Flush Operation.”
Bayan an kama su ne aka gurfanar da su a gaban kotu kan zargin aikata ta’addanci da kuma aikata zamba ta intanet.
Sanarwar ta ambato tuhumar da aka yi wa masu laifin na shiga manhajar komfuta da gangan domin lalata tattalin arziki da zamantakewar al’ummar Nijeriya, wanda hakan ya nuna cewa ya aikata laifi da ya saɓa wa dokar hana laifukan intanet ta 2015 da kuma dokar hana ta’addanci ta 2022.
Daga farko dai waɗanda ake zargin sun musanta zargin da aka karanta musu daga takardar tuhumar.
Sai dai kuma a zaman kotun na ranar 23 ga watan Yuni sun sauya matsayarsu zuwa amsa laifi, kuma nan take lauyoyin gwamnati suka nemi kotu ta same su da laifi tare da hukunta su.
“Saboda haka, kotun ta same su da laifi tare da yi wa kowanne daga waɗanda ake tuhumar ɗaurin shekara ɗai-ɗai daga ranar 10 ga watan Disamba na shekarar 2025, da kuma cin kowanne daga cikinsu tarar naira miliyan ɗaya-ɗaya,” in ji sanarwar.
Alƙalin ya kuma ba da umarni ga shugaban hukumar kula da shige da fice ta Nijeriya ya tabbatar cewa an mayar da ’yan China ƙasar da suka fito cikin kwanani bakwai da zarar sun kammala wa’adin gidan yari.
Kazalika, kotun ta ba da umarnin cewa a sallamar da wayoyi da kamfutoci da kuma na’uororin samar da intanet da aka ƙwace daga masu laifin wa Gwamnatin Tarayyar Nijeriya.